Sashe 54
Zaki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Wallahi ni bana ma son minti biyar ta kara a gidan nan wacan yarinyar da kike gani tun da ta zo kullum sai wani mummunan abu ya faru”
“Za ki wuce ko ba zaki wuce ba”
Mama Fulani ta daka min tsawar da ta sakani mikewa tsaye a razane na fice da sauri. Garejin na dawo na zauna ina ta kuka mai karfi wai ko wani zai ji ya zo ya tambaya dalilin kukana yajd ya bata hakuri amman babu wanda ya zo har na ji muryarta tana kiran Zaharadden direba.
“Ki fito yanzu nan ko na shigo cikin na ci miki mutumci”
Da sauri na tashi na dauki jakar tawa na nufi garden na dauko ragowar tufafin dana shanya tun rana na saka a ciki na dawo garejin na saka sauran da musasshiyar farfesun kazar dana shanya na saka cikin jakar da siyayar da Kamal yai min, sannan na saka Hijab dina na fito ina hawaye na tsaya jikin garejin ina kallon kudin da take ba wa direban.
“Ka tabbatar ta shiga mota sannan na mika mata sauran kudi, idan an isa kaduna ta hau motar sokoto ai tasan gidan ubanta idan aka sauke ta a can”
“To Hajiya”
Ya fada yana karbar kudin tare da zagaya wa wajen motar ya bude ya shiga.
“Zo ki wuce mun rabu da kaya”
“Kudin aikina fa?”
“Aikin da ko wata ba ki yi ba? Je ki turo ubanki ya zo ya dibar miki”
“Ubana baya duniya Hajiya, ya tafi idan zan ki je zan je kowa zai je, amman Allah zai dibar min hakkina”
Shine kawai abunda na iya fada cikin kuka na nufi motar na bude na shiga, ina jinta tana ta zagina. Hawaye ne suke ta min zuba har muka isa tashar, a lokacin da direban yai farkin na bude zan fita sai na ji ya ce.
“Ki yi hakuri da rayuwa, haka take zuwa juyi juyi Allah ya sauwake mana talauci ni da ke mu daina zama karkashin kowa”
Da na kalleshi sai na ga hawaye a idonsa.
“Amin”
Na amsa sannan na sauka daga motar shi ma ya fito, sai da yaje gurin yan Union ya hannata musu ni ya basu kudin motar zuwa kaduna da kuma kudin motar Kaduna to sokoto sannan ya ciro dubu biyu ya mika min.
“Gashi ki rike wannan Allah ya kai ki lafiya sai wata rana”
“Na gode”
Na karba da hannu biyu ina ta hawaye kamar wacce akai wa ido dan hawayen kawai.
“Lafiya Mutuwa akai miki?”
Daya daga cikin mutanen ya tambaya. Sai na girgiza masa kai ina jan magina.
“Aa ba mutuwa akai min ba”
“To Allah ya sauwake”
“Amin”
Shi ya nuna min motar da zan shiga sannan ya bawa direban kudina da kuma kudin motar da zai saka ni ta Kaduna sannan na shiga na zauna muna jiran karin wasu mutum biyu. Ban dade da zaman ba aka kira sallah la'asar sai da aka kira sallar na tuna da cewar ban yi sallah azahar ba, sauri na fita daga motar na nufi gefen masallacin nai alwala da butar su sannan na nufi wani dan daki dana hango mata na shiga na shiga ciki nai sallah, na fadawa Allah bukakata kuma na kai masa kukana na kuma roki mafita akan dukan lamura na. Ba bar tashar ba sai biyar da kwata sannan direbamu ya kama hanya.ALIYU POV.
Da mugun bachin rai ya fita daga asibitin yana cikin motarsa Momy ta kira shi ta fada masa cewar an sallami Rahma kuma ya zo ya tafi da ita, jin wannan labarin yasa ki sakewa daga bachin ran da yake ciki sai ya dauki hanyar asibitin. Ko da y shiga ciki ya samu Momy da Mommy Rahma suna fita Rahma na zauna tare da kanenta guri daya fuskarta babu walwala, ganin Aliyu ya saka kanen nata suka tashi daga saman gadon suka dauki wasu kayan da za a tafi da su suka fice. Da murmushi Aliyu yake kallonta amman ita ka kasa sakewa kamar ba ita aka sallama ba.
“Amman na ce idan mun wuta yau zuwa gobe za mu tafi da ita can sokoto ta samu kula kuma idan tana kusa da mu ita kanta zata fi walwala”
Mommy Rahma ta fada har Aliyu ya bude ba ki zai yi magana sai Momy ta shiga kuma ta shanye duk wani abu da yake da niyar fada.
“Eh nima na yi wannan tunanin hakan zai fi, shi kanshi Dan wajen Fulani ai ba zai ki ba, Allah dai ya bata lafiya muma ai goben za mu koma”
Shiru yai be ce komai ba, saboda Momy ta saye bakinsa. Mommyn Rahma da Momy tare suka jera a gaba suna tafiya shi kuma ya jero shi da Rahma suka nufo gurin da ake aje motoci. Wata motar Mommyn Rahma da kanenta suka shiga Mommy kuma ta shiga gidan baya Aliyu da Rahma suka shiga gaba. Sai da ya fara shiga har cikin gidan Mama Fulani ya sauke Momy har sisters dinsa suka fito suka ga Rahma ban da Mama Fulani da take jin sai dai Rahma ta fita daga motar taje ta gaisheta. Bayan Momy ta fita ya wuce da Rahma gidansa, bata ce masa komai ba shi ma be ce mata ba har suka isa tana kao hannu ta bude motar sai ya rike dayan hannun wanda hakan yasa ta kalleshi.
“Rahma kamar ba ki murna da sallamar nan da aka miki?”
“Miye abun murna a gurin gawar da aka kai asibiti? Ai kasan daga asibitin sai kabari, ba warkewa nai gaba daya ba, to me zai saka ni murna?”
“Wani ya baki tabbacin cewa ba za ki warke ba? Ko kuwa kina da shaidar cewar mutuwa za ki yi saboda kina da wannan ciwon”
“Za ka iya bani tabbacin cewar zan warke na tashi kamar kai? Ko kuwa zaka ba ni tabbacin cewar wannan ciwon ba zai yi ajalina ba?”
Ta aika masa da tambaya cikin tambaya ba tare da ta bashi amsar tambayar da yai mata ba. Fita tai daga motar ya zagaya gefenta ya bude mata motar ya fito da ita ta rumgumeta sai ta karasa fashewa da kukan da take ta kankame shi sosai tana shakar turaren jikinsa.
“Bana son na rayu da wani namijin baya kai Aliyu, ina son ka sosai, ko da bana aurenka ba zan iya jurar ka kula da wata macen kamar yadda kake kula da ni ba, ba zan bari son wata mace ya shiga zuciyarka ba dan Allah ka min alkawari ko bayan raina ba zaka auri wata ba”
“Mi zai saka na auri wata bayan kina raye? Ko wace ta cancanci wani gurbi a zuciyata bayan ke Rahma? Be kamata kina irin wadannan tunanin ba”
Akwai abubuwa da yawa da ba su kamata na aikata su ba Aliyu amman dole na aikata, a zuci tai wannan maganar tana nasalta yadda zata rayu ba tare da Aliyu ba na dan lokaci kamin da dawo masa kuma ta dawo da farincikinta da cikar burinta na haihuwa. Rikata Aliyu yai suka shiga cikin falon zuciyarsa cike da tausayinta duk kuwa da irin maganganun da tai masa dazun suna cikin ransa.
ZAKI
By Khadeeja Candy
28...
ATAA POV.
Misalin goma na dare muka isa Kaduna, a cikin tashar direban ya sama min guri na kwana bayan na yi sallah, washe gari ma sai da na siya pure water sannan nai sallah asuba, bayan ruwan naira goma ban sake saka komai a bakina domin jin nai bana bukatar komai kuma bana jin yunwa, da asuba muka kamo hanyar sokoto daga Kaduna, ina ta jin kamar zan yi amai a motar saboda kaurin mai da tafiya mai nisa wacce ban saba da ita ba. Ana gama sallah azahar muka shigo sokoto, ba dowowar dadi nai ba amman tuna cewar da mahaifiyata zan gana sai na ji sanyi, a wani bangaren kuma ina ta zullumi da tunanin abunda zan fada mata domin na san ba zata ji dadi idan na fada mata an korono ba, gashi kuma ban samu kudi ba. A babbar tasha muka sauka na dauko jakata da dubu daya da dari biyar da sauran canjin da na siya ruwa da su cikin kudin da direban Mama Fulani ya ba ni. Sai da na kawo bakin titi sannan na tari napep na shiga na fada masa inda zai kawo ni. Daga tashar zuwa Clapperto road dari da hansi ya kawo ni na bashi kudinsa na fita zuciyarta cike da zullumi da tunanin karyar da zanyi, har ina tunanin fara zuwa gidan Maman Salma sai kuma na wuce gidansu Farida kai tsaye. Wani dan karamin dakin kwano ne akai a gafen gidan wanda akai masa fuska daga can gabans ta yadda wanda yake cikin dakin baya ganin wanda zai zo wanda kuma zai zo baya iya ganin na ciki. Ina ta mamakin miye a gurin domin ban san da dakim kwanon ba kamin na tafi,. Da sallama na shiga cikin gidan sai Farida ta fito waje da sauri tana washe hakora.
“Oyoyo Ataa”
Rumgume ni tai duk da ina cikin bacin rai hakan be hana ni murna ba na rumgumeta muna murna da ganin juna.
“Ina jin muryar na ce ke ce”
“Ni ce fatar na same ku lafiya”
“Lafiya kalau”
Na sake ta na nufi dan kitchen din da nasan na bar Nana a cikin kamin na karasa ta ce.
“Ai am maida Nana dakin waje”
Cikin yanayin rashin jindadi ta fada fuskarta na nuna haka. Ban tambayi dalili ba sai dai naji faduwar gaba jin hakan, sai na juyo na fito daga gidan gaba daya na nufi inda kofar dakin kwanon take Farida na biye da ni a baya yanayinta kamar mai jin tsoro. Mutuwar tsaye a bakin kofar dakin kwanon na saki jakar da ke hannuna ina kallon Nana da ke kwance kamar kare domin babu tsoka a jikinta sai ƙassa, kanta ba dankwali gashin kanta ya tsire an rufa mata wani zane dakin gana daya wari yake warin kashi da fitsari, kallo take ba dan ta ganeni ba sai dan mutum take gani ban san lokacin da hawaye suka fara min zuba ba zuciyata ta rufe tai min wani irin mugun nauyi..
“Za ki wuce ko ba zaki wuce ba”
Mama Fulani ta daka min tsawar da ta sakani mikewa tsaye a razane na fice da sauri. Garejin na dawo na zauna ina ta kuka mai karfi wai ko wani zai ji ya zo ya tambaya dalilin kukana yajd ya bata hakuri amman babu wanda ya zo har na ji muryarta tana kiran Zaharadden direba.
“Ki fito yanzu nan ko na shigo cikin na ci miki mutumci”
Da sauri na tashi na dauki jakar tawa na nufi garden na dauko ragowar tufafin dana shanya tun rana na saka a ciki na dawo garejin na saka sauran da musasshiyar farfesun kazar dana shanya na saka cikin jakar da siyayar da Kamal yai min, sannan na saka Hijab dina na fito ina hawaye na tsaya jikin garejin ina kallon kudin da take ba wa direban.
“Ka tabbatar ta shiga mota sannan na mika mata sauran kudi, idan an isa kaduna ta hau motar sokoto ai tasan gidan ubanta idan aka sauke ta a can”
“To Hajiya”
Ya fada yana karbar kudin tare da zagaya wa wajen motar ya bude ya shiga.
“Zo ki wuce mun rabu da kaya”
“Kudin aikina fa?”
“Aikin da ko wata ba ki yi ba? Je ki turo ubanki ya zo ya dibar miki”
“Ubana baya duniya Hajiya, ya tafi idan zan ki je zan je kowa zai je, amman Allah zai dibar min hakkina”
Shine kawai abunda na iya fada cikin kuka na nufi motar na bude na shiga, ina jinta tana ta zagina. Hawaye ne suke ta min zuba har muka isa tashar, a lokacin da direban yai farkin na bude zan fita sai na ji ya ce.
“Ki yi hakuri da rayuwa, haka take zuwa juyi juyi Allah ya sauwake mana talauci ni da ke mu daina zama karkashin kowa”
Da na kalleshi sai na ga hawaye a idonsa.
“Amin”
Na amsa sannan na sauka daga motar shi ma ya fito, sai da yaje gurin yan Union ya hannata musu ni ya basu kudin motar zuwa kaduna da kuma kudin motar Kaduna to sokoto sannan ya ciro dubu biyu ya mika min.
“Gashi ki rike wannan Allah ya kai ki lafiya sai wata rana”
“Na gode”
Na karba da hannu biyu ina ta hawaye kamar wacce akai wa ido dan hawayen kawai.
“Lafiya Mutuwa akai miki?”
Daya daga cikin mutanen ya tambaya. Sai na girgiza masa kai ina jan magina.
“Aa ba mutuwa akai min ba”
“To Allah ya sauwake”
“Amin”
Shi ya nuna min motar da zan shiga sannan ya bawa direban kudina da kuma kudin motar da zai saka ni ta Kaduna sannan na shiga na zauna muna jiran karin wasu mutum biyu. Ban dade da zaman ba aka kira sallah la'asar sai da aka kira sallar na tuna da cewar ban yi sallah azahar ba, sauri na fita daga motar na nufi gefen masallacin nai alwala da butar su sannan na nufi wani dan daki dana hango mata na shiga na shiga ciki nai sallah, na fadawa Allah bukakata kuma na kai masa kukana na kuma roki mafita akan dukan lamura na. Ba bar tashar ba sai biyar da kwata sannan direbamu ya kama hanya.ALIYU POV.
Da mugun bachin rai ya fita daga asibitin yana cikin motarsa Momy ta kira shi ta fada masa cewar an sallami Rahma kuma ya zo ya tafi da ita, jin wannan labarin yasa ki sakewa daga bachin ran da yake ciki sai ya dauki hanyar asibitin. Ko da y shiga ciki ya samu Momy da Mommy Rahma suna fita Rahma na zauna tare da kanenta guri daya fuskarta babu walwala, ganin Aliyu ya saka kanen nata suka tashi daga saman gadon suka dauki wasu kayan da za a tafi da su suka fice. Da murmushi Aliyu yake kallonta amman ita ka kasa sakewa kamar ba ita aka sallama ba.
“Amman na ce idan mun wuta yau zuwa gobe za mu tafi da ita can sokoto ta samu kula kuma idan tana kusa da mu ita kanta zata fi walwala”
Mommy Rahma ta fada har Aliyu ya bude ba ki zai yi magana sai Momy ta shiga kuma ta shanye duk wani abu da yake da niyar fada.
“Eh nima na yi wannan tunanin hakan zai fi, shi kanshi Dan wajen Fulani ai ba zai ki ba, Allah dai ya bata lafiya muma ai goben za mu koma”
Shiru yai be ce komai ba, saboda Momy ta saye bakinsa. Mommyn Rahma da Momy tare suka jera a gaba suna tafiya shi kuma ya jero shi da Rahma suka nufo gurin da ake aje motoci. Wata motar Mommyn Rahma da kanenta suka shiga Mommy kuma ta shiga gidan baya Aliyu da Rahma suka shiga gaba. Sai da ya fara shiga har cikin gidan Mama Fulani ya sauke Momy har sisters dinsa suka fito suka ga Rahma ban da Mama Fulani da take jin sai dai Rahma ta fita daga motar taje ta gaisheta. Bayan Momy ta fita ya wuce da Rahma gidansa, bata ce masa komai ba shi ma be ce mata ba har suka isa tana kao hannu ta bude motar sai ya rike dayan hannun wanda hakan yasa ta kalleshi.
“Rahma kamar ba ki murna da sallamar nan da aka miki?”
“Miye abun murna a gurin gawar da aka kai asibiti? Ai kasan daga asibitin sai kabari, ba warkewa nai gaba daya ba, to me zai saka ni murna?”
“Wani ya baki tabbacin cewa ba za ki warke ba? Ko kuwa kina da shaidar cewar mutuwa za ki yi saboda kina da wannan ciwon”
“Za ka iya bani tabbacin cewar zan warke na tashi kamar kai? Ko kuwa zaka ba ni tabbacin cewar wannan ciwon ba zai yi ajalina ba?”
Ta aika masa da tambaya cikin tambaya ba tare da ta bashi amsar tambayar da yai mata ba. Fita tai daga motar ya zagaya gefenta ya bude mata motar ya fito da ita ta rumgumeta sai ta karasa fashewa da kukan da take ta kankame shi sosai tana shakar turaren jikinsa.
“Bana son na rayu da wani namijin baya kai Aliyu, ina son ka sosai, ko da bana aurenka ba zan iya jurar ka kula da wata macen kamar yadda kake kula da ni ba, ba zan bari son wata mace ya shiga zuciyarka ba dan Allah ka min alkawari ko bayan raina ba zaka auri wata ba”
“Mi zai saka na auri wata bayan kina raye? Ko wace ta cancanci wani gurbi a zuciyata bayan ke Rahma? Be kamata kina irin wadannan tunanin ba”
Akwai abubuwa da yawa da ba su kamata na aikata su ba Aliyu amman dole na aikata, a zuci tai wannan maganar tana nasalta yadda zata rayu ba tare da Aliyu ba na dan lokaci kamin da dawo masa kuma ta dawo da farincikinta da cikar burinta na haihuwa. Rikata Aliyu yai suka shiga cikin falon zuciyarsa cike da tausayinta duk kuwa da irin maganganun da tai masa dazun suna cikin ransa.
ZAKI
By Khadeeja Candy
28...
ATAA POV.
Misalin goma na dare muka isa Kaduna, a cikin tashar direban ya sama min guri na kwana bayan na yi sallah, washe gari ma sai da na siya pure water sannan nai sallah asuba, bayan ruwan naira goma ban sake saka komai a bakina domin jin nai bana bukatar komai kuma bana jin yunwa, da asuba muka kamo hanyar sokoto daga Kaduna, ina ta jin kamar zan yi amai a motar saboda kaurin mai da tafiya mai nisa wacce ban saba da ita ba. Ana gama sallah azahar muka shigo sokoto, ba dowowar dadi nai ba amman tuna cewar da mahaifiyata zan gana sai na ji sanyi, a wani bangaren kuma ina ta zullumi da tunanin abunda zan fada mata domin na san ba zata ji dadi idan na fada mata an korono ba, gashi kuma ban samu kudi ba. A babbar tasha muka sauka na dauko jakata da dubu daya da dari biyar da sauran canjin da na siya ruwa da su cikin kudin da direban Mama Fulani ya ba ni. Sai da na kawo bakin titi sannan na tari napep na shiga na fada masa inda zai kawo ni. Daga tashar zuwa Clapperto road dari da hansi ya kawo ni na bashi kudinsa na fita zuciyarta cike da zullumi da tunanin karyar da zanyi, har ina tunanin fara zuwa gidan Maman Salma sai kuma na wuce gidansu Farida kai tsaye. Wani dan karamin dakin kwano ne akai a gafen gidan wanda akai masa fuska daga can gabans ta yadda wanda yake cikin dakin baya ganin wanda zai zo wanda kuma zai zo baya iya ganin na ciki. Ina ta mamakin miye a gurin domin ban san da dakim kwanon ba kamin na tafi,. Da sallama na shiga cikin gidan sai Farida ta fito waje da sauri tana washe hakora.
“Oyoyo Ataa”
Rumgume ni tai duk da ina cikin bacin rai hakan be hana ni murna ba na rumgumeta muna murna da ganin juna.
“Ina jin muryar na ce ke ce”
“Ni ce fatar na same ku lafiya”
“Lafiya kalau”
Na sake ta na nufi dan kitchen din da nasan na bar Nana a cikin kamin na karasa ta ce.
“Ai am maida Nana dakin waje”
Cikin yanayin rashin jindadi ta fada fuskarta na nuna haka. Ban tambayi dalili ba sai dai naji faduwar gaba jin hakan, sai na juyo na fito daga gidan gaba daya na nufi inda kofar dakin kwanon take Farida na biye da ni a baya yanayinta kamar mai jin tsoro. Mutuwar tsaye a bakin kofar dakin kwanon na saki jakar da ke hannuna ina kallon Nana da ke kwance kamar kare domin babu tsoka a jikinta sai ƙassa, kanta ba dankwali gashin kanta ya tsire an rufa mata wani zane dakin gana daya wari yake warin kashi da fitsari, kallo take ba dan ta ganeni ba sai dan mutum take gani ban san lokacin da hawaye suka fara min zuba ba zuciyata ta rufe tai min wani irin mugun nauyi..