Sashe 101
Zaki Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Ya amsa min fuskarsa babu murmushi ko wasa kamar ba shi ba. Ni kuma na fice ina ta masa kallon abunda yai min dazun.
Ko da na isa part din wato bq na samu Nana na share saman balcony din saurin aje abincin hannuna nai na karbi sharar nakarasa, sai ta koma cikin daki ta zauna. Bayan na gama na je ma sameta na dauko abun karyawa na aje mata na shiga na wanke bakina kamar yadda Momy ta fada sannan na zo muka karya.
“Ina jin kamar be dace ace har an miki aure Hajiya na zancen tarewarki a sati mai zuwa kuma ace yan'uwana da yan'uwan mahaifinki, ina jin kamar hakan be dace ba, kuma ina jin babu dadi idan na tuna da haka sai dai babu yadda zan yi”
Bayan mun gama cin abincin take min wannan maganar, gabana ne ya fadi.
“Tarewa ta sati mai zuwa Nana?”
“Haka ta roka ita da matar da suka zo jiya, kuma ta ce idan na amince zata fadawa Mahaifin Aliyu sun fada min sun dauke nauyin komai, za su yi duk abunda ya dace, kuma za a hada miki kayan sakawarki wasu tun a nan wasu kuma sai kinje can Saboda kurewar lokaci, tace ba za ayi wani hidima ba amman tana son ta shirya yar walima saboda addu'a”
Kuka na fara yi a take.
“Karatuna fa? Yanzu kenan? Barin zuwa makarantar zan yi? Kuma bokan ma ba za a a saka ni ba?”
“aa zancen karatunki tace yana nan za ki cigaba da karatunki ko bayan aure”
“Aa nana ni ban yarda ba Wallahi bana so, ma fasa auren gaba daya Wallahi ba zan yarda ba, ni ba zan iya zaman da shi ba, wayyo Nana dan Allah karki bari na tare yanzu....”
Shine abunda na ke fada ina rikon hannunta domin har ga Allah na tsorota da wani zaman aure a yanzu, yo ya ma zan yi zaman? Me ake cewa ya tsare tsaren suke ni na zan iya ba, ga wannan kazantar da yake min na san idan ina can sai ya sake min ita, karatuna ma lalacewa zai yi. Babu abunda Nana take sai kallo da fuskar tausayi domin kukan ba na wasa na ke ba.
“Na riga na karba mata ba zan iya canjawa a yanzu ba, Allah yasa hakan shi ya fi alheri”
Kara fadawa nai jikinta na fashe da kuka ina ta goga mata jikina kamar wata yarinya karama, bata ce min komai ba bayan hawayen da take har nai kuka na gama na tashi dan kaina na shiga bandakin na wanke fuskarta na saka uniform dina na tafi makarantar islamiya kasancewar ranar Lahadi ce ana zuwa da safe. Sai dai ban sake da kowa ba duk wanda ya kalleni ya san ina cikin damuwa domin har ga Allah bana son tarewar gaba daya ma sai na ji auren ya fita a raina.
Da shabiyun rana aka tashe mu na dawo gida kamar wata marar lafiya, abincin rana kawai na ci Momy ta aiko wai nai wanka za mu fita, sai na shiga nai wanka na shirya a cikin daya daga rigunan da Aliyu ya siyo min a ranar da yaje da ni shopping.
Amina aka kawo ta zo ta kirani muka shiga nota tare muka dauki hanyar gidan Zara mai lalle kalar fatata ta duba ta bani wasu abubuwan ta ce wannan na rika shafawa a jikina idan zan kwanta wannan kuma idan zan shiga da kamar minti goma haka, ni dai ji kawai na ke ba dan ina da niyar yi ba, daga ranar ban sake zuwa makarantar islamiya ba ban kuma sake saka Aliyu a idona ba, idan dare yayi sai Momy ta aiko min da fruits na sha, bayan kwana uku a gidan ta mayar da ni gurin wata kanwarta dake Abuja road, a can akai ta cusa min wasu abubuwa da na ke hadewa daker idan na gama na shiga bandaki nai kukana son raina na fito, duk na kasa sakewa a gidan lokaci zuwa lokaci Amina da Siyama da Husna suke zuwa su dubani, da dare fruit ake ba ni kamar yadda Momy take min a can sa safe kuma ba a bari na karya daabu mai nauyi da na ci kadan sai ace na barta haka a bani kaza mai magani da daci na ci, gashi tsoron matar na ke domin na lura ita ba kamar Momy ba ce sam bata wasa da yara balle ta sake da su, ba kuma wulakanci ba irin halin nan na dattijai.
Kullum sai an kaini gurin Zara ta gyada min jiki, ta shafa min turare na jiki da na kai da kuma na tsiguno, sannan ta ba ni ruwan magani ta ce nai wanka idan ta gama min dilka ni kaina a yanzu ina jin dadin jikina domin fatar jikin har wani sheki take tayi laushi sosai fiye da da, gashin kaina kuwa kamar ba nawa ba, domin kullum cikin shafa masa mai take tana gyara shi, ita kanta yabon kyauna take gaba daya na koma kamar ba ni ba, domin kuwa na fi da kyau da haske duk wani datti na fuskata da jikina sai da aka kawarda shi. Wata kabila ce ta zo ta auna ni ko'ina na jiki sai da ta auna ta sannan ta tafi, haka na rika kwana a gidan kullum idan na yi marmarin ganin Nana sai da a kira min ita a waya shi ma kuma idan Siyama ta zo ko Amina ko kuma Momy ta kira, a gidan matar idan zata hada abunda be kai kmya kawo ba ko wani abu mai nauyi ba sai ta kirani ta nuna min ta tambaye ni na gane, ko ban gane ba cewa na ke na ge saboda kawai a wuce gurin, sai dai kullum sai na sha kukan dare ni kadai ba tare da kowa ya sani ba.
ALIYU POV.
Sai da ta wuce sannan ya mike ya nufi dinning yana fadin.
“Tare kuka shirya abun karyawar ne?”
“Eh wai ina dan koya mata ne kamin taje can ta koya gaba daya”
Yayi shiru be ce komai ba har ya zauna ya bude abinci ya zubawa kansa ya soma ci yana ta tunanin abunda yai ma Ataa a dazu sai murmushi yake a zuciyarsa.
“Aliyu yarinyarnan tana son karatu sosai fa”
Da dago ya kalli Momy.
“Na sani shiyasa na shigar da ita islamiya ai, kuma bokon ma zan saka nan gaba In-Sha-Allah”
“Ina jin tsoro kar aurenku ya saka karatunta tarwatsewa”
“Saboda me? As long as zatai zaman aure ai zan barta tai karatunta, ba ni da matsala da wannan amman Momy..... ”
Sai kuma yai shiru ya kasa karasawa. Momy ta shiga zubawa Daddyn abincinsa tana tambayarsa.
“Amman me?”
“Tsawon wane lokaci zata dauka a gida tana karatun?”
“Karatu yana da lokaci ne?”
“Na yi magana da Daddynka jiya saboda Hajiya Ramatu ta kawo wata shawara har ta saka ni dole sai da naje bq nai magana da Nana ita kuma ta amince ta ce mana ba matsala, da na fadawa Daddynka sai yace shi babu ruwanshi shawara ta mu ce, kuma na kira babbar Yayarku after sallah asuba na fada mata komai ita ta bani shawara makamanciyar wacce Hajiya Ramatu ta ba ni”
Da dago tana ta kallonta, gabansa na dan faduwa irin na tsoron nan idan ba wani abun za a bullo da shi ba, wata kila ace ya kai Ataa wata makarantar boko a Abuja ko kasar waje ko kuma ya barta gida har nan da wani lokaci mai tsawo wanda yake jin cewar ba zai iya haka ba.
“Wani abun ne?”
Sai da Momy ta gama warewa Daddyn nasa abun karyarwa sannan ta ce.
“Wai Mun yanke shawarar Ataa ta tare dakinta next week Saturday”
Wani irin dadi da mamaki da annashuwa da farinciki Aliyu ya ji lokaci daya, amman yai kokarin dannewa saboda kar Momy ta ga haukarsa ko rashin kunyarsa, yayi murmushin dake nuna jindadinsa amman ya boye duk wani jindadin na ainahi a cikin ruhinsa.
“Amman Momy ita ta yarda?”
“Aisha ai bata da matsala duk inda aka bi da ita bi za tai, Nana kuma t amince har ma godiya tai mana jin cewar an dauke mata komai”
“Masha-Allah Allah ya tabbatar da alheri”
“Amin sai ka fara shirye shirye tun a yanzu”
Momy ta fada sannan ta dauki kayan abincin ta fice, wani irin murmushi Aliyu yai ya girgiza hannunsa ya shafa kansa abincin ma sai ya kasa ci.
Ko da na isa part din wato bq na samu Nana na share saman balcony din saurin aje abincin hannuna nai na karbi sharar nakarasa, sai ta koma cikin daki ta zauna. Bayan na gama na je ma sameta na dauko abun karyawa na aje mata na shiga na wanke bakina kamar yadda Momy ta fada sannan na zo muka karya.
“Ina jin kamar be dace ace har an miki aure Hajiya na zancen tarewarki a sati mai zuwa kuma ace yan'uwana da yan'uwan mahaifinki, ina jin kamar hakan be dace ba, kuma ina jin babu dadi idan na tuna da haka sai dai babu yadda zan yi”
Bayan mun gama cin abincin take min wannan maganar, gabana ne ya fadi.
“Tarewa ta sati mai zuwa Nana?”
“Haka ta roka ita da matar da suka zo jiya, kuma ta ce idan na amince zata fadawa Mahaifin Aliyu sun fada min sun dauke nauyin komai, za su yi duk abunda ya dace, kuma za a hada miki kayan sakawarki wasu tun a nan wasu kuma sai kinje can Saboda kurewar lokaci, tace ba za ayi wani hidima ba amman tana son ta shirya yar walima saboda addu'a”
Kuka na fara yi a take.
“Karatuna fa? Yanzu kenan? Barin zuwa makarantar zan yi? Kuma bokan ma ba za a a saka ni ba?”
“aa zancen karatunki tace yana nan za ki cigaba da karatunki ko bayan aure”
“Aa nana ni ban yarda ba Wallahi bana so, ma fasa auren gaba daya Wallahi ba zan yarda ba, ni ba zan iya zaman da shi ba, wayyo Nana dan Allah karki bari na tare yanzu....”
Shine abunda na ke fada ina rikon hannunta domin har ga Allah na tsorota da wani zaman aure a yanzu, yo ya ma zan yi zaman? Me ake cewa ya tsare tsaren suke ni na zan iya ba, ga wannan kazantar da yake min na san idan ina can sai ya sake min ita, karatuna ma lalacewa zai yi. Babu abunda Nana take sai kallo da fuskar tausayi domin kukan ba na wasa na ke ba.
“Na riga na karba mata ba zan iya canjawa a yanzu ba, Allah yasa hakan shi ya fi alheri”
Kara fadawa nai jikinta na fashe da kuka ina ta goga mata jikina kamar wata yarinya karama, bata ce min komai ba bayan hawayen da take har nai kuka na gama na tashi dan kaina na shiga bandakin na wanke fuskarta na saka uniform dina na tafi makarantar islamiya kasancewar ranar Lahadi ce ana zuwa da safe. Sai dai ban sake da kowa ba duk wanda ya kalleni ya san ina cikin damuwa domin har ga Allah bana son tarewar gaba daya ma sai na ji auren ya fita a raina.
Da shabiyun rana aka tashe mu na dawo gida kamar wata marar lafiya, abincin rana kawai na ci Momy ta aiko wai nai wanka za mu fita, sai na shiga nai wanka na shirya a cikin daya daga rigunan da Aliyu ya siyo min a ranar da yaje da ni shopping.
Amina aka kawo ta zo ta kirani muka shiga nota tare muka dauki hanyar gidan Zara mai lalle kalar fatata ta duba ta bani wasu abubuwan ta ce wannan na rika shafawa a jikina idan zan kwanta wannan kuma idan zan shiga da kamar minti goma haka, ni dai ji kawai na ke ba dan ina da niyar yi ba, daga ranar ban sake zuwa makarantar islamiya ba ban kuma sake saka Aliyu a idona ba, idan dare yayi sai Momy ta aiko min da fruits na sha, bayan kwana uku a gidan ta mayar da ni gurin wata kanwarta dake Abuja road, a can akai ta cusa min wasu abubuwa da na ke hadewa daker idan na gama na shiga bandaki nai kukana son raina na fito, duk na kasa sakewa a gidan lokaci zuwa lokaci Amina da Siyama da Husna suke zuwa su dubani, da dare fruit ake ba ni kamar yadda Momy take min a can sa safe kuma ba a bari na karya daabu mai nauyi da na ci kadan sai ace na barta haka a bani kaza mai magani da daci na ci, gashi tsoron matar na ke domin na lura ita ba kamar Momy ba ce sam bata wasa da yara balle ta sake da su, ba kuma wulakanci ba irin halin nan na dattijai.
Kullum sai an kaini gurin Zara ta gyada min jiki, ta shafa min turare na jiki da na kai da kuma na tsiguno, sannan ta ba ni ruwan magani ta ce nai wanka idan ta gama min dilka ni kaina a yanzu ina jin dadin jikina domin fatar jikin har wani sheki take tayi laushi sosai fiye da da, gashin kaina kuwa kamar ba nawa ba, domin kullum cikin shafa masa mai take tana gyara shi, ita kanta yabon kyauna take gaba daya na koma kamar ba ni ba, domin kuwa na fi da kyau da haske duk wani datti na fuskata da jikina sai da aka kawarda shi. Wata kabila ce ta zo ta auna ni ko'ina na jiki sai da ta auna ta sannan ta tafi, haka na rika kwana a gidan kullum idan na yi marmarin ganin Nana sai da a kira min ita a waya shi ma kuma idan Siyama ta zo ko Amina ko kuma Momy ta kira, a gidan matar idan zata hada abunda be kai kmya kawo ba ko wani abu mai nauyi ba sai ta kirani ta nuna min ta tambaye ni na gane, ko ban gane ba cewa na ke na ge saboda kawai a wuce gurin, sai dai kullum sai na sha kukan dare ni kadai ba tare da kowa ya sani ba.
ALIYU POV.
Sai da ta wuce sannan ya mike ya nufi dinning yana fadin.
“Tare kuka shirya abun karyawar ne?”
“Eh wai ina dan koya mata ne kamin taje can ta koya gaba daya”
Yayi shiru be ce komai ba har ya zauna ya bude abinci ya zubawa kansa ya soma ci yana ta tunanin abunda yai ma Ataa a dazu sai murmushi yake a zuciyarsa.
“Aliyu yarinyarnan tana son karatu sosai fa”
Da dago ya kalli Momy.
“Na sani shiyasa na shigar da ita islamiya ai, kuma bokon ma zan saka nan gaba In-Sha-Allah”
“Ina jin tsoro kar aurenku ya saka karatunta tarwatsewa”
“Saboda me? As long as zatai zaman aure ai zan barta tai karatunta, ba ni da matsala da wannan amman Momy..... ”
Sai kuma yai shiru ya kasa karasawa. Momy ta shiga zubawa Daddyn abincinsa tana tambayarsa.
“Amman me?”
“Tsawon wane lokaci zata dauka a gida tana karatun?”
“Karatu yana da lokaci ne?”
“Na yi magana da Daddynka jiya saboda Hajiya Ramatu ta kawo wata shawara har ta saka ni dole sai da naje bq nai magana da Nana ita kuma ta amince ta ce mana ba matsala, da na fadawa Daddynka sai yace shi babu ruwanshi shawara ta mu ce, kuma na kira babbar Yayarku after sallah asuba na fada mata komai ita ta bani shawara makamanciyar wacce Hajiya Ramatu ta ba ni”
Da dago tana ta kallonta, gabansa na dan faduwa irin na tsoron nan idan ba wani abun za a bullo da shi ba, wata kila ace ya kai Ataa wata makarantar boko a Abuja ko kasar waje ko kuma ya barta gida har nan da wani lokaci mai tsawo wanda yake jin cewar ba zai iya haka ba.
“Wani abun ne?”
Sai da Momy ta gama warewa Daddyn nasa abun karyarwa sannan ta ce.
“Wai Mun yanke shawarar Ataa ta tare dakinta next week Saturday”
Wani irin dadi da mamaki da annashuwa da farinciki Aliyu ya ji lokaci daya, amman yai kokarin dannewa saboda kar Momy ta ga haukarsa ko rashin kunyarsa, yayi murmushin dake nuna jindadinsa amman ya boye duk wani jindadin na ainahi a cikin ruhinsa.
“Amman Momy ita ta yarda?”
“Aisha ai bata da matsala duk inda aka bi da ita bi za tai, Nana kuma t amince har ma godiya tai mana jin cewar an dauke mata komai”
“Masha-Allah Allah ya tabbatar da alheri”
“Amin sai ka fara shirye shirye tun a yanzu”
Momy ta fada sannan ta dauki kayan abincin ta fice, wani irin murmushi Aliyu yai ya girgiza hannunsa ya shafa kansa abincin ma sai ya kasa ci.