Sashe 142
Zaki Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
“Koda ai da kaddararsa wani jinkiri alheri ne, kuma da ka yi auren a koma ana kuka ai kara kawai kayi hakuri har na kwarai ya zo, domin duk yadda ta matsu tai auren ba tai Rukaiya ba da ta auri wanda ko boko be yi ba, da ma ace yayi karatun sai a sama amsa aiki amman babu bokon abubuwan sai a hankali wani lokacin haka jarrabawa take zuwa ma mutum kuma komai yana bukatar a tsananta bincike, da yanzu an yi bincike mai zurfi ai da duk haka be faru ba, amman sai aka tsaya ana masa kallon dan babban mutum ganin ya zo nema masa aure kuma yana bin sunansa a matsayin ubansa”
“Gaskiya kan abun babu dadi amman kaddara ce, ta riga fata haka Allah ya so”
“Na mu kawai Addu'a ne, kuma na fadawa Mama na ce tai ta mata addu'a Allah ya bata miji na gari, ita kuma Rukaiya Allah ya mata mafita”
“Amin”
Na amsa ina kallonsa ya mike tsaye yana murza ido.
“Lafiya?”
“Zazzabi na ke ji”
“To ka sha magani sai ka kwanta”
“To Hajiya ta”
Na masa murmushi sai ya mayar min sannan ya dauke plate din da muka ci abincin ya nufi kitchen.
Kwana biyu da wannan na sake jin irin wacan ciwon sai dai wannan ya ci uban wacan ta ko'ina domin ba kaina ba ba cikina ba ba bayana ba ba marata ba ko'ina ji nake yana murda min, haka na wuni tun safe har dare kkuma Allah ya bani ikon yin girkina cikin karfin hali har na gama, sai da yamma abun ya tsananta min idan zan zauna sai na ji kamar abu zai fito min da baya, hankali be kara tashi ba sai da naje fitsari na ga jini sannan na kira Hamma a waya na fada masa. Daga office ya dawo gida hankali tashe a lokacin har na fara kuka babu hawaye saboda tsananin azaba.
“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u, wayyo bayana wayyo cikina Momy Mama, har da Mama Fulani da Ammy”
Su na ke ta fadi har aka shiga da ni dakin haihuwa, bana iya komai dai dai amman ina jin lokacin da akai ta rigima da Hamma kamin a samo macen da zata karbi haihuwa ta. Ihu nake iya karfina su ko sai ce min suke na nai nishi.
“Nishin ya kare wayuo Allah Allah ka cece ni, wayyo Allah Wallahi Aliyu ne”
Na fada cikin rudewa da jin zafin murdawar da cikin ke min.
“Addu'a ake Allah ake kira”
Likitar ta fada min hakan yasa na fara karanto addu'ain da na sani a cikin har na neman tsari daga azabar kabari da talauci amman jin anke kamar ana karo min abun, da na ga abun be min ba na koma salatin Annabi. A haka na kwashe awa hudu ban haihuwa tun ina nishin da sauran karfina har karfin ya kare.
“Dan Allah ku kira min Momy dan Allah ta zo”
“Ba Momy ba ko Daddy ba zai zo ba balle Momy sai da kika zo haihuwa kika tuna da Momy, sai kin ji yadda kowa ya ji”
Matar ta fada tana dariya.
“Wayuo Allah ka min Rahama Allah na tuba”
Na fada ina da kuka sosai, sai ga Hamma ya shigo a cikin dakin duk ya hada gumi kamar shi ke nakudar, hannu ya kama ya rike idonsa cike da kwalla yana ta min addu'a. Cikin ikon Allah da iyawarsa na soma jin abu na fito min, wani uban uhu na kwala sai da ji nai an yanka ni da wani abun an janyo abun sai kuka yake, sai suka dora min shi saman ciki suka ware min kafafuwansa.
“Kall ki gani me kika haifa?”
“Namiji”
Na fada a wahalce sannan sukai dariya suka dauke shi.
ALIYU POV.
Farinciki ya kasa barinsa ya yarda cewar dansa yake gani, jininsa be san lokacin da ya saki Ataa ya nufi inda Nurse din da ke goge jaririn take sannan dayar ta fita ta karbo kayan jariri, kamin a saka masa kaya sai da Aliyu ya karbi dan yai masa kiss sannan ya mika shi aka saka masa kaya. Shi ya fito rike da abunsa ya nufo inda su Mama Fulani take tsaye a take gurin suka fara ihu da murna. Wannan ya karba wannan ya karba, aka hau yi masa hotuna cikin har da uban yaron ya aikawa Momy kuma ya dora status dinsa. A rana duk wani family member na su sai da yai farinciki da samun haihuwa da Aliyu yai. Sai a lokacin ya gane yana tsananin son Ataa da kaunarta, jin nai kamar na lashe ta yake ji ita da abunda ta haifa ba ma shi kadai ba har da Mama Fulani sai a lokacin da san darajar Ataa.
Sosai yan'uwan Nana suka so a ba su Ataa su tafi da ita can, amman Mama Fulani da Momy suka tsaya kai da fata akan ayi musu alfama a bar musu ita a nan saboda Aliyu idan aka maida ita a can ba zai samu damar zuwa ko da yaushe ba ga shi kuma ba zai yayu ya koma can da zama gaba daya, ko yake yadda yake rawar kafarta zai iya tarewa a can sai dai ya nuna musu rashin an ido akan matarsa ko kadansa.
An zubawa Ataa kayan barka kamar ba gobe ta kowane bangare samun kyauta take da kulawa sai ta zama yar gata. A ranar suna jariri ya ci suna Muhammad Amir, an yi bidiri an kashe kudi iya kudi, an yi abubuwa da dama na rabawa mutane wani abun da zai baka mamaki har da Mommyn Rahma, dole ta zo ko dan nadamar da tai ga kuma alakar Ataa da dukiyarsu.
Kwana uku da bikin sunan aka sake yankewa Asim makamancin hukuncin da aka yanke masa a wacan kotun ta sokoto, yanzu kan babu zancen daukaka kara sai fuskantar abunda ya aikata. Hasara biyu da uku ta same shi ga na rufe asibitinsa ga na bacin suna ga kuma na rufe shi gidan yari.
**** **** ****
ATAA POV.
Sai da nai arba'in sannan na tafi Nijar ganin yan'uwana, wata daya nai a can duk kuwa da kasancewar Hamma be so haka ba amman ban bi ya kansa ba domin na lura idan na biye shi ba zan yi zuminci ba, domin shi ya fi son kullum ina kusa da shi ko dan dansa, naga dangi na kusa da na nesa daidai gwargwado, kuma na ga kauna da soyayya ni da Amir ta ko wane bangare, har sai na ji kamar kar na dawo.
Ba Abuja na dawo kai tsaye ba, a gidan Momy na fara sauka sati na daya a can ita ta kaini gurin wasu yan'uwanta da ban sani ba da ma waenda na sani na gaishe su sannan na dawo Abuja gurin Mijina. Ina dawowa Hamma ya daukar min wata dattijiwa mai kula da gina, ni kuwa aikina girka abinci kula Amir sai kuma makarantar da na ke zuwa domin bana wasa da karatuna saboda burin da na ke da shi na yin zurfi a ilmi ko da kuwa Hamma ba zai barni nai aiki ba ina da burin yin zurfi a ilmina
Amir na da wata uku akai bikin Husna da Amina, mun chashe sosai mun biki mai amsa sunan bikin har manta nai da ina da da sai idan zai sha nono ake kawo shi da ya sha nonon, yan'uwan ubanshi za su dauke shi bachi kawai ke hada ni da shi. Wani abun tausayin har kuma tsawon lokacin Maryam bata samu wani ba Rukaiya kuma na dauke da juna biyu ita da sauran Amare, matar Muhseen ce kawai bata samu komai ba, daman na san za a rina an sace zanen mahaukaciya na san sai ya gama lokacinsa kamin ya haihu.
Na maida hankalina sosai akan karatuna, da kula da mijina da kuma dana, karatu be hana shi ko daya ba, haka ma kula da mijina da na be hanani karatun ba, na dage na mika dukam imani da karfina da dama saboda samun cikar burina. Ga goyon baya da na ke samu da kauna ta ko wane bangare, kan kace kwabo na goge a makarantar cikin shekaru uku ni ma ana dama da ni a cikin daliban da za su shiga aji na karshe wato Sss3 a Royal Academy.
Daf da yin Candy na samu wani cikin hakan kuma yayi min daidai domin na san iya lamani Hubby ya yi min na daga min kafa daga haihuwa duk kuwa da irin son yayan da yake har na gama makarantar. A week later akai bikin Maryam da wani mai mata biyu a sokoto dan'uwana Momy da ta hada ta da shi kuma suka daidaita. Ba laifi mutumen na da rufin asiri daidai gwargwado sai dai zaman kishi da zata fuskanta da matan sakkwato wanda za su gyara mata zama ta gane kuskurenta.
“Gaskiya kan abun babu dadi amman kaddara ce, ta riga fata haka Allah ya so”
“Na mu kawai Addu'a ne, kuma na fadawa Mama na ce tai ta mata addu'a Allah ya bata miji na gari, ita kuma Rukaiya Allah ya mata mafita”
“Amin”
Na amsa ina kallonsa ya mike tsaye yana murza ido.
“Lafiya?”
“Zazzabi na ke ji”
“To ka sha magani sai ka kwanta”
“To Hajiya ta”
Na masa murmushi sai ya mayar min sannan ya dauke plate din da muka ci abincin ya nufi kitchen.
Kwana biyu da wannan na sake jin irin wacan ciwon sai dai wannan ya ci uban wacan ta ko'ina domin ba kaina ba ba cikina ba ba bayana ba ba marata ba ko'ina ji nake yana murda min, haka na wuni tun safe har dare kkuma Allah ya bani ikon yin girkina cikin karfin hali har na gama, sai da yamma abun ya tsananta min idan zan zauna sai na ji kamar abu zai fito min da baya, hankali be kara tashi ba sai da naje fitsari na ga jini sannan na kira Hamma a waya na fada masa. Daga office ya dawo gida hankali tashe a lokacin har na fara kuka babu hawaye saboda tsananin azaba.
“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u, wayyo bayana wayyo cikina Momy Mama, har da Mama Fulani da Ammy”
Su na ke ta fadi har aka shiga da ni dakin haihuwa, bana iya komai dai dai amman ina jin lokacin da akai ta rigima da Hamma kamin a samo macen da zata karbi haihuwa ta. Ihu nake iya karfina su ko sai ce min suke na nai nishi.
“Nishin ya kare wayuo Allah Allah ka cece ni, wayyo Allah Wallahi Aliyu ne”
Na fada cikin rudewa da jin zafin murdawar da cikin ke min.
“Addu'a ake Allah ake kira”
Likitar ta fada min hakan yasa na fara karanto addu'ain da na sani a cikin har na neman tsari daga azabar kabari da talauci amman jin anke kamar ana karo min abun, da na ga abun be min ba na koma salatin Annabi. A haka na kwashe awa hudu ban haihuwa tun ina nishin da sauran karfina har karfin ya kare.
“Dan Allah ku kira min Momy dan Allah ta zo”
“Ba Momy ba ko Daddy ba zai zo ba balle Momy sai da kika zo haihuwa kika tuna da Momy, sai kin ji yadda kowa ya ji”
Matar ta fada tana dariya.
“Wayuo Allah ka min Rahama Allah na tuba”
Na fada ina da kuka sosai, sai ga Hamma ya shigo a cikin dakin duk ya hada gumi kamar shi ke nakudar, hannu ya kama ya rike idonsa cike da kwalla yana ta min addu'a. Cikin ikon Allah da iyawarsa na soma jin abu na fito min, wani uban uhu na kwala sai da ji nai an yanka ni da wani abun an janyo abun sai kuka yake, sai suka dora min shi saman ciki suka ware min kafafuwansa.
“Kall ki gani me kika haifa?”
“Namiji”
Na fada a wahalce sannan sukai dariya suka dauke shi.
ALIYU POV.
Farinciki ya kasa barinsa ya yarda cewar dansa yake gani, jininsa be san lokacin da ya saki Ataa ya nufi inda Nurse din da ke goge jaririn take sannan dayar ta fita ta karbo kayan jariri, kamin a saka masa kaya sai da Aliyu ya karbi dan yai masa kiss sannan ya mika shi aka saka masa kaya. Shi ya fito rike da abunsa ya nufo inda su Mama Fulani take tsaye a take gurin suka fara ihu da murna. Wannan ya karba wannan ya karba, aka hau yi masa hotuna cikin har da uban yaron ya aikawa Momy kuma ya dora status dinsa. A rana duk wani family member na su sai da yai farinciki da samun haihuwa da Aliyu yai. Sai a lokacin ya gane yana tsananin son Ataa da kaunarta, jin nai kamar na lashe ta yake ji ita da abunda ta haifa ba ma shi kadai ba har da Mama Fulani sai a lokacin da san darajar Ataa.
Sosai yan'uwan Nana suka so a ba su Ataa su tafi da ita can, amman Mama Fulani da Momy suka tsaya kai da fata akan ayi musu alfama a bar musu ita a nan saboda Aliyu idan aka maida ita a can ba zai samu damar zuwa ko da yaushe ba ga shi kuma ba zai yayu ya koma can da zama gaba daya, ko yake yadda yake rawar kafarta zai iya tarewa a can sai dai ya nuna musu rashin an ido akan matarsa ko kadansa.
An zubawa Ataa kayan barka kamar ba gobe ta kowane bangare samun kyauta take da kulawa sai ta zama yar gata. A ranar suna jariri ya ci suna Muhammad Amir, an yi bidiri an kashe kudi iya kudi, an yi abubuwa da dama na rabawa mutane wani abun da zai baka mamaki har da Mommyn Rahma, dole ta zo ko dan nadamar da tai ga kuma alakar Ataa da dukiyarsu.
Kwana uku da bikin sunan aka sake yankewa Asim makamancin hukuncin da aka yanke masa a wacan kotun ta sokoto, yanzu kan babu zancen daukaka kara sai fuskantar abunda ya aikata. Hasara biyu da uku ta same shi ga na rufe asibitinsa ga na bacin suna ga kuma na rufe shi gidan yari.
**** **** ****
ATAA POV.
Sai da nai arba'in sannan na tafi Nijar ganin yan'uwana, wata daya nai a can duk kuwa da kasancewar Hamma be so haka ba amman ban bi ya kansa ba domin na lura idan na biye shi ba zan yi zuminci ba, domin shi ya fi son kullum ina kusa da shi ko dan dansa, naga dangi na kusa da na nesa daidai gwargwado, kuma na ga kauna da soyayya ni da Amir ta ko wane bangare, har sai na ji kamar kar na dawo.
Ba Abuja na dawo kai tsaye ba, a gidan Momy na fara sauka sati na daya a can ita ta kaini gurin wasu yan'uwanta da ban sani ba da ma waenda na sani na gaishe su sannan na dawo Abuja gurin Mijina. Ina dawowa Hamma ya daukar min wata dattijiwa mai kula da gina, ni kuwa aikina girka abinci kula Amir sai kuma makarantar da na ke zuwa domin bana wasa da karatuna saboda burin da na ke da shi na yin zurfi a ilmi ko da kuwa Hamma ba zai barni nai aiki ba ina da burin yin zurfi a ilmina
Amir na da wata uku akai bikin Husna da Amina, mun chashe sosai mun biki mai amsa sunan bikin har manta nai da ina da da sai idan zai sha nono ake kawo shi da ya sha nonon, yan'uwan ubanshi za su dauke shi bachi kawai ke hada ni da shi. Wani abun tausayin har kuma tsawon lokacin Maryam bata samu wani ba Rukaiya kuma na dauke da juna biyu ita da sauran Amare, matar Muhseen ce kawai bata samu komai ba, daman na san za a rina an sace zanen mahaukaciya na san sai ya gama lokacinsa kamin ya haihu.
Na maida hankalina sosai akan karatuna, da kula da mijina da kuma dana, karatu be hana shi ko daya ba, haka ma kula da mijina da na be hanani karatun ba, na dage na mika dukam imani da karfina da dama saboda samun cikar burina. Ga goyon baya da na ke samu da kauna ta ko wane bangare, kan kace kwabo na goge a makarantar cikin shekaru uku ni ma ana dama da ni a cikin daliban da za su shiga aji na karshe wato Sss3 a Royal Academy.
Daf da yin Candy na samu wani cikin hakan kuma yayi min daidai domin na san iya lamani Hubby ya yi min na daga min kafa daga haihuwa duk kuwa da irin son yayan da yake har na gama makarantar. A week later akai bikin Maryam da wani mai mata biyu a sokoto dan'uwana Momy da ta hada ta da shi kuma suka daidaita. Ba laifi mutumen na da rufin asiri daidai gwargwado sai dai zaman kishi da zata fuskanta da matan sakkwato wanda za su gyara mata zama ta gane kuskurenta.