Sashe 93
Zaki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Gaba daya jin nai kaina yayi nauyi kuma yana ciwo, saboda tunawa da baya da kuma jin labarin Nana, sai dai bana ganin hakan a matsayin laifin da mahaifinta zai iya cewa ba zai yafe ba, wata kila yana raye ko kuma ya mutu Allah nasani, sosai zuciyata ta cika da kaunar Aliyu domin shine mutumen da ya fara maida ni mutum ya sa na maye gurbin duk wani abu da na rasa kuma yarda ya so ni yadda na ke, ba dan kyau na ko wani abu nawa ba, tsabanin duk wanda zai kalle ni ya so dan kyauna, Momy kuma ta biyo a sahu na biyu a kaunar da ta nuna min na son danta ya aureni saboda ya inganta rayuwarta kuma Rahma ta daina min kallon banza, yana da wahala a zamanin nan ace wani wanda baka sani ba kamar Momy da Aliyu su soka tsakani da Allah. Sai a yanzu na ke gane wasu abubuwan da Nana take hango min.
Hakika zabuwa da iyaye akwai ciwo da damuwa, ni kaina da Nana ta kamu da ciwon nan ina ta tsoro da zullumin rabuwa da ita, ni kenan da ke tare da albarkata ina ga ita da guduwa tai ta bar iyayen? Sai yanzu na gano dalilin cewar da take tana son ta san hannun da zan fada kamin ta bar duniya, tana kuma tsoron gaba saboda tana tunanin ba iyakar kaddararta kenan ba, lallai ko kadan ta ga na kuma abu ya zo da sauki da ya zama kodarta kawai aka cire kuma har ta samu tattafin Aliyu ya nema mata magani ta warke. A yanzu kam na yarda da zancenta cewar kaddarar Aliyu ce ta zo a hannunta kamar yadda tata kaddarar ta zo a hannun Babana.
Labarin Nana be kara min komai ba sai tausayi da jinka da kuma ganin darajar zabin iyaye ko da kuwa mai cutarwa ne, matukar ka bata musu rai dole ne sai wani abun ya same ka ko da ko kadan ne, kaunarta na ji ta karu a raina da kuma son zama kusa da ita, domin a yanzu ni kadai ce wacce take da, kuma ita kadai ce wacce na ke gani na ji sanyi a raina wato uwata.
Daga har ita cikin damuwa da tunani muka kwana, washe gari bayan mun yi sallah na zauna nai yi ma Babana addu'a sosai daman na saba masa a sujida sai dai wannan ta musammance, domin na san a yanzu babu abunda ya ke bukata a tare da ni kamar Addu'a ta. Misalin takwas da rabi na shiga part din Momy na share komai kamar yadda na sabawa kaina Amina da Husna kuma suka shirya abun karyawa suka ba ni nawa ni da Nana.
Na koma na kai mata, ruwan shayin kawai ta sha ta kasa cin komai fuskarta gaba daya ta kumbura, kana gani ka san a daren jiya ta kwana tunani kuma ta sha kuka.
“Nana Babanki zai yafe miki matukar yana raye, shekaru da yawa ya isa ya saka zuciyarsa laushi ya fahimce ki”
“Ba zai yafe min ba, na aikata kuskure na gudu saboda biyan bukatar raina be kamata wuya ta saka na koma ba”
“Ba saboda wuya za ki koma ba, saboda kin yi nadama kin gane kuskurenki za ki koma”
“Wata kila ma baya raye, abun kunya ne ace na haihu har dayan ya koma ga Allah mahaifina be san yayana ba, yayana kuma ba su san yan'uwana ba, ba zan iya komawa garin nan ba har abada, na barwa iyayena da masarautar Agadez abun kunya”
Ajiyar zuciya na sauke ina sauraren motar da naji an faka harabar gidan, hayaniyar Amina da Husna ne yasa na tashi na leka window sai na hango Momy ta fito daga motar ita kadai ba tare da Aliyu ba, wata kila ya tafi gidansa gurin matarsa ko kuma ba yau zai dawo ba.
Fitowa nai na tareta tare da rika jar jakar hannunta na bi bayanta, ita kuma tana ta min murmushi har muka shiga cikin falon, a nan ta zauna Amina ta debo mata ruwa suna ta daukinta kamar wacce ta shekara bata gidan, ita tana marmarin gwanin sha'awa uwa mai dadi.
“Momy ya Aliyu fa?”
Husna ta tambaya.
“Ba yau ba yace zai kwana biyu kamin ya dawo”
Momy na bada amsar zuciyata ta raya min wata kila da matarsa ya tafi shiyasa ba zai dawo yanzu ba. Ballantana na san idan Mama Fulani ta ji cewar saboda ni komai ya faru ba zata barshi ya dawo ba, a take na ji raina ya bace. Da abincin mu na rana na dawo part din mu ina jin cewar yanzu ne ma lokacin da ya kamata na auri Aliyun ko dan Rahma da Mama Fulani sai na ga idan mutuwa za su yi, ace irin tsanar da suke nunawa talaka Aliyu ya aure ni sai ya kenan? Kuma ina tunanin ta wannan hanyar ce kawai zan yi ma Momy tukuicin abunda tai mana, ita kadai ce hanyar da zan saka mahaifiyata cikin farinciki a yanzu na taimake ta ita ma ta sake jindadin rayuwa.
Da yamma ina cikin shirin zuwa makarantar islamiya, Momy ta aiko tana kirana Siyama ce ta shigo ta fada min gana sanye da nata uniform din na islamiya sai dai na ta dabam kamar yadda nawa yaks dabam kasacewar ba makarantarmu daya ba. Kamin na shiga part din Momy na hango mutumen jiya wato ustazu nan yau ma yana cikin shigarsa ta mutunci da kamala. Ina shiga Momy ta ce min.
“Wani na waje yana sallama da ke, wai yana neman izinin mu kamin yai magana da ke, ki fadawa Nana sannan ki je”
“Momy ban iya fira ba, ko naje ban san mi zan ce masa ba”
Na bata amsa a takaice wanda har cikin zuciyarta haka ne, idan na je ban san abunda zan fada masa ba, fira da wani a yanzu ina jin kamar ba zata min dadi ba, idan kuma na ce zan yi da gara duk mutanen da za su bude ba ki na furta kalmar so a gareni tabbas ko zai furta ko ya nuna zai zama babu kamun kai a ciki.
“To kije ku gaisa inyaso sai ki fada mishi an tsayar miki da miji ko kuma kina da wanda kike so”
Da wannan shawarar da ta ba ni na tashi na fita zuwa gurin mutunen, mun gaisa da shi cikin mutunci ya gabatar min da sunansa aikinsa da kuma inda ya ganni wai lokacin da na taso islamiyar nan har ya tambaye ni gidanmu. Kai tsaye na bashi hakuri kuma na fada masa cewar akwai wanda za a tsiyar min a gida, ya nuna min rashin jindadinsa da kuma yi min fatan alheri sannan muka yi sallama. komawa nai bq na dauki littafaina na wuce islamiya zuciyata cike da tunanin ko zuwa yaushe Aliyu zai dawo? Mi ya tsayar da shi a abujar? Ni dai sam ban jindadin rashin dawowarsa ba, ba zan kuma kira abun da so ba, domin ba ni tabbacin ina son Aliyu ko akasin hakan, sai dai na san akwai sabo wanda ko fada kake da mutum dole ne wani lokacin sai ka yi marmarinsa balle kuma yanzu da na fara gane amfanin abubuwan da yai min.
MOMY POV.
Bayan tafiyar Ataa islamiya Momy ta tashi ta debi yan gurin da Mama Fulani ta sako mata a kwali wato snacks da cake ta nufi bq da su, da far'arta ta shiga bq din yana wayance wa kamar komai bw faru ba, ta karanci damuwa a fuskar Nana sai dai bata maida hankaki akan tatauna da Nana akan matsalar ba, a zatonta abunda Muhseen yai ne har yanzu yake damunta.
“Mun yi tafiya shekaranjiya ban fada miki ba, tafiyar ta safe ce shiya saka”
“Babbu komi Hajjiya ya hanya?”
“Al-hamdulillah, ga wannan”
Momy ta mika mata plates din hannunta, sannan ta dora da dalilin zuwanta bq din.
“Daman Daddyn su ne yace a fada miki kuma a nemi shawararki aji ta bakinki, wai yana son indai za ki amince sati na mai zuwa a daurawa Ataa aure da wanda take so ko waye ne, mun hanke wannan shawarar ne saboda hankalin kowa ya kwanta ita kanta hankalinta ya kwanta kin ga ko zuwa sallamar nan ba dadi ne ba, amman idan har aka mata auren dole kowa ya kama gabansa, kuma yi mata auren ba shi yake nufin hana ta karatunta ba no zata cigaba da karatunta a gidan mijin ko kuma a nan idan zai yarda”
“Sati daya?”
Nana ta nanata.
“Nima kaina naga kamar abun yayi wuri, sai dai saboda kwanciyar hankali kowa ake son ayi haka, ina son ki manta da duk abunda ya faru ki tambayi Ataa wanda take so idan a kusa ne sai neme shi idan kuma nesa ne sai a san ta yi tun wuri, idan kuma kina ganin watan yayi tsawo za ki iya fadar lokacin da kike son a saka, nan da wata daya biyu uku ko shekara ma ko fiye da haka”
“A a hukuncin da kuka yanke ya yi, waya sani ko zan kai gobe ma balle nan da wata daya ko shekara, fatar ko wace uwa ai yarta ta samu gurin zaman da ya dace da ita, Na gode sosai Hajiya”
“Karki jin kunya ko nauyin komai Wallahi duk wani abunda nai saboda Allah nai, dan haka karki taba kawo wani abu a ranki, ni da ke an zama yan'uwa kuma zan mata komai kamar yadda nai alkwari In-Sha-Allah, idan tarewar a nan kusa ne ko nesa duk daya ne a gurina”
“Allah ya saka da alheri”
Sosai Nana ta so tayi ma Momy maganar tashinta, sai kuma ta ji nauyi saboda girman Abunda Momy ta zo mata da shi, idan kuma tai mata maganar a yanzu wata kila ba zata fahimta ba, sai kawai ta zabi aje maganar a cikin har na wani lokaci.
ALIYU POV.
Hakika zabuwa da iyaye akwai ciwo da damuwa, ni kaina da Nana ta kamu da ciwon nan ina ta tsoro da zullumin rabuwa da ita, ni kenan da ke tare da albarkata ina ga ita da guduwa tai ta bar iyayen? Sai yanzu na gano dalilin cewar da take tana son ta san hannun da zan fada kamin ta bar duniya, tana kuma tsoron gaba saboda tana tunanin ba iyakar kaddararta kenan ba, lallai ko kadan ta ga na kuma abu ya zo da sauki da ya zama kodarta kawai aka cire kuma har ta samu tattafin Aliyu ya nema mata magani ta warke. A yanzu kam na yarda da zancenta cewar kaddarar Aliyu ce ta zo a hannunta kamar yadda tata kaddarar ta zo a hannun Babana.
Labarin Nana be kara min komai ba sai tausayi da jinka da kuma ganin darajar zabin iyaye ko da kuwa mai cutarwa ne, matukar ka bata musu rai dole ne sai wani abun ya same ka ko da ko kadan ne, kaunarta na ji ta karu a raina da kuma son zama kusa da ita, domin a yanzu ni kadai ce wacce take da, kuma ita kadai ce wacce na ke gani na ji sanyi a raina wato uwata.
Daga har ita cikin damuwa da tunani muka kwana, washe gari bayan mun yi sallah na zauna nai yi ma Babana addu'a sosai daman na saba masa a sujida sai dai wannan ta musammance, domin na san a yanzu babu abunda ya ke bukata a tare da ni kamar Addu'a ta. Misalin takwas da rabi na shiga part din Momy na share komai kamar yadda na sabawa kaina Amina da Husna kuma suka shirya abun karyawa suka ba ni nawa ni da Nana.
Na koma na kai mata, ruwan shayin kawai ta sha ta kasa cin komai fuskarta gaba daya ta kumbura, kana gani ka san a daren jiya ta kwana tunani kuma ta sha kuka.
“Nana Babanki zai yafe miki matukar yana raye, shekaru da yawa ya isa ya saka zuciyarsa laushi ya fahimce ki”
“Ba zai yafe min ba, na aikata kuskure na gudu saboda biyan bukatar raina be kamata wuya ta saka na koma ba”
“Ba saboda wuya za ki koma ba, saboda kin yi nadama kin gane kuskurenki za ki koma”
“Wata kila ma baya raye, abun kunya ne ace na haihu har dayan ya koma ga Allah mahaifina be san yayana ba, yayana kuma ba su san yan'uwana ba, ba zan iya komawa garin nan ba har abada, na barwa iyayena da masarautar Agadez abun kunya”
Ajiyar zuciya na sauke ina sauraren motar da naji an faka harabar gidan, hayaniyar Amina da Husna ne yasa na tashi na leka window sai na hango Momy ta fito daga motar ita kadai ba tare da Aliyu ba, wata kila ya tafi gidansa gurin matarsa ko kuma ba yau zai dawo ba.
Fitowa nai na tareta tare da rika jar jakar hannunta na bi bayanta, ita kuma tana ta min murmushi har muka shiga cikin falon, a nan ta zauna Amina ta debo mata ruwa suna ta daukinta kamar wacce ta shekara bata gidan, ita tana marmarin gwanin sha'awa uwa mai dadi.
“Momy ya Aliyu fa?”
Husna ta tambaya.
“Ba yau ba yace zai kwana biyu kamin ya dawo”
Momy na bada amsar zuciyata ta raya min wata kila da matarsa ya tafi shiyasa ba zai dawo yanzu ba. Ballantana na san idan Mama Fulani ta ji cewar saboda ni komai ya faru ba zata barshi ya dawo ba, a take na ji raina ya bace. Da abincin mu na rana na dawo part din mu ina jin cewar yanzu ne ma lokacin da ya kamata na auri Aliyun ko dan Rahma da Mama Fulani sai na ga idan mutuwa za su yi, ace irin tsanar da suke nunawa talaka Aliyu ya aure ni sai ya kenan? Kuma ina tunanin ta wannan hanyar ce kawai zan yi ma Momy tukuicin abunda tai mana, ita kadai ce hanyar da zan saka mahaifiyata cikin farinciki a yanzu na taimake ta ita ma ta sake jindadin rayuwa.
Da yamma ina cikin shirin zuwa makarantar islamiya, Momy ta aiko tana kirana Siyama ce ta shigo ta fada min gana sanye da nata uniform din na islamiya sai dai na ta dabam kamar yadda nawa yaks dabam kasacewar ba makarantarmu daya ba. Kamin na shiga part din Momy na hango mutumen jiya wato ustazu nan yau ma yana cikin shigarsa ta mutunci da kamala. Ina shiga Momy ta ce min.
“Wani na waje yana sallama da ke, wai yana neman izinin mu kamin yai magana da ke, ki fadawa Nana sannan ki je”
“Momy ban iya fira ba, ko naje ban san mi zan ce masa ba”
Na bata amsa a takaice wanda har cikin zuciyarta haka ne, idan na je ban san abunda zan fada masa ba, fira da wani a yanzu ina jin kamar ba zata min dadi ba, idan kuma na ce zan yi da gara duk mutanen da za su bude ba ki na furta kalmar so a gareni tabbas ko zai furta ko ya nuna zai zama babu kamun kai a ciki.
“To kije ku gaisa inyaso sai ki fada mishi an tsayar miki da miji ko kuma kina da wanda kike so”
Da wannan shawarar da ta ba ni na tashi na fita zuwa gurin mutunen, mun gaisa da shi cikin mutunci ya gabatar min da sunansa aikinsa da kuma inda ya ganni wai lokacin da na taso islamiyar nan har ya tambaye ni gidanmu. Kai tsaye na bashi hakuri kuma na fada masa cewar akwai wanda za a tsiyar min a gida, ya nuna min rashin jindadinsa da kuma yi min fatan alheri sannan muka yi sallama. komawa nai bq na dauki littafaina na wuce islamiya zuciyata cike da tunanin ko zuwa yaushe Aliyu zai dawo? Mi ya tsayar da shi a abujar? Ni dai sam ban jindadin rashin dawowarsa ba, ba zan kuma kira abun da so ba, domin ba ni tabbacin ina son Aliyu ko akasin hakan, sai dai na san akwai sabo wanda ko fada kake da mutum dole ne wani lokacin sai ka yi marmarinsa balle kuma yanzu da na fara gane amfanin abubuwan da yai min.
MOMY POV.
Bayan tafiyar Ataa islamiya Momy ta tashi ta debi yan gurin da Mama Fulani ta sako mata a kwali wato snacks da cake ta nufi bq da su, da far'arta ta shiga bq din yana wayance wa kamar komai bw faru ba, ta karanci damuwa a fuskar Nana sai dai bata maida hankaki akan tatauna da Nana akan matsalar ba, a zatonta abunda Muhseen yai ne har yanzu yake damunta.
“Mun yi tafiya shekaranjiya ban fada miki ba, tafiyar ta safe ce shiya saka”
“Babbu komi Hajjiya ya hanya?”
“Al-hamdulillah, ga wannan”
Momy ta mika mata plates din hannunta, sannan ta dora da dalilin zuwanta bq din.
“Daman Daddyn su ne yace a fada miki kuma a nemi shawararki aji ta bakinki, wai yana son indai za ki amince sati na mai zuwa a daurawa Ataa aure da wanda take so ko waye ne, mun hanke wannan shawarar ne saboda hankalin kowa ya kwanta ita kanta hankalinta ya kwanta kin ga ko zuwa sallamar nan ba dadi ne ba, amman idan har aka mata auren dole kowa ya kama gabansa, kuma yi mata auren ba shi yake nufin hana ta karatunta ba no zata cigaba da karatunta a gidan mijin ko kuma a nan idan zai yarda”
“Sati daya?”
Nana ta nanata.
“Nima kaina naga kamar abun yayi wuri, sai dai saboda kwanciyar hankali kowa ake son ayi haka, ina son ki manta da duk abunda ya faru ki tambayi Ataa wanda take so idan a kusa ne sai neme shi idan kuma nesa ne sai a san ta yi tun wuri, idan kuma kina ganin watan yayi tsawo za ki iya fadar lokacin da kike son a saka, nan da wata daya biyu uku ko shekara ma ko fiye da haka”
“A a hukuncin da kuka yanke ya yi, waya sani ko zan kai gobe ma balle nan da wata daya ko shekara, fatar ko wace uwa ai yarta ta samu gurin zaman da ya dace da ita, Na gode sosai Hajiya”
“Karki jin kunya ko nauyin komai Wallahi duk wani abunda nai saboda Allah nai, dan haka karki taba kawo wani abu a ranki, ni da ke an zama yan'uwa kuma zan mata komai kamar yadda nai alkwari In-Sha-Allah, idan tarewar a nan kusa ne ko nesa duk daya ne a gurina”
“Allah ya saka da alheri”
Sosai Nana ta so tayi ma Momy maganar tashinta, sai kuma ta ji nauyi saboda girman Abunda Momy ta zo mata da shi, idan kuma tai mata maganar a yanzu wata kila ba zata fahimta ba, sai kawai ta zabi aje maganar a cikin har na wani lokaci.
ALIYU POV.