← Book details Zaki Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 10 OF 143

Sashe 10

Zaki Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Yana fadar hakan ya juya ya fice, ni kuma na bishi da kallon kauna kauna irin ta wanda ya taimake ka a halin da kake da bukatar taimakon. A dare Nana ta dan ta6a fira da ni tana tambayar abubuwan da ke mana ina ta fada mata ita kanta tai farinciki sosai kuma tai masa addu'a sannan ta sha kankana kadan kamar yadda ya umarta, ni ko a daren sai da nai tas na ci na koshi sannan na kwanta kan shimfidar da ya kawo mana ni da Lukman, kusan sai na ce ban taba kwanciya akan wani abu mai dadi makamancin katifa ba irin yau.
Tun daga lokacin kullum Nana cikin kara samun lafiya take, ni da Lukman kuma ba mu kara zuwa bara ba, kudin daya bani tun a karon farko ma ban sake taba su ba domin komai na ke bukata yi mana yake babu abunda muke yi da kanmu tun kama daga abinci magani da duk wani abun bukata. Sai dai abu daya yake ta bani tsoro, yadda Nana ta gagara komawa daidai, motsi kadan sai ta rike kirjinsa ko gefen cikinta ta ce ciwo yake mata kuma tana yawan fadawa likitan amman sai ya ce ba wata matsala ba ce zata ji sauki nan gaba kadan. Mutanen da muka zaman arziki da su suna ta zuwa suna duba Nana, kusan sai na yi sati ban leka gida ba idan ma wanka zan yi sai na yi a bandakin da ke dakin, daman can kuma wanka ba damu na yai ba, iya kar kokarin da na ke a yanzu na tsayar da sallah a kan lokacij ne ganin bana aikin komai a nan asibitin sai zama, Nana ma ina kokarin ganin na saka ta yi duk kuwa da irin kin son taba ruwa da take ko da na zafi ne yanzu sai ta ji jikinta ya kara rashin karfi, ganin hakan yasa na samo mata kasa na koya mata taimama kamar yadda aka koyar da mu makarantar islamiya lokacin da na ke zuwa.
Kullum cikin yi ma likitan nan da ban san sunansa addu'a muke ni da Nana, yana kulawa da mu sosai, ba dan rashin lafiyar Nana da ke cikin raina ba da Allah kadai yasan kibar da zan yi akan abubuwan dadin da muke ci, sai dai Nana kan ta kasa komawa yadda take a da, walwalarta kuzarinta da kuka sakewa ta kasa yi kusan kullum sai rama take daman can ba wani jikin ne da ita sosai ba.
Wasa wasa muka kwashe wata daya a asibitin, har zaman ya fara gundirata ita kanta Nana da ke ciwon sai ta fara gajiya, kullum addu'ar Allah ya bata lafiya mu bar asibitin, kowa mamaki yadda dafin macijin ya zame mata haka ake yi, ko da yake likitan ya fada mana cewar dafin ya warke ciwon cikin cikinta ne kawai ya rage ya warke. kusan sai na saba da nurses din da ke dan shigowa duba wani lokacin amman masu sake fuska a cikin, sauran kan sai dai su yi min kallon banza, da kuma mutanen da ke zam waje harabar asibitin suna jinyar wasu, domin idan na gaji da zama cikin dakin da take sai na dauko tabarmar nai shimfida a waje ni da Lukman mu zauna, har ita wani lokacin Nurse Shukura tana fitowa da ita ta sha iska, duk a cikin Nurse din Shukuwa ta fi sake min sai dai a yadda na lura kamar shi likitan baya son shirinmu da ita, wata kila akwai rashin jituwa a tsakaninsu ne ko kuma wani abun oho, domin na lura da ita ma kamar bata jindadin yadda muke yabonsa muke saka masa albarka da addu'ar alheri.
Haka nan kawai wani lokacin idan bata aikin komai sai ta shigo dakinmu mu yi ta fara kamar mun saba, ta haka har na san unguwar da take zama wato tudun wada da kuma inda ni ma nake zama har take ce min tana da wata kawa a kusa da mu, akwai ranar da take fada min cewar tana tausayina ni da Lukman jin cewar ba mu da kowa a nan Nigeria ko ma muna da su ni ban sansu ba, domin Mahaifina be tana fada min ba Nana ma bata nuna fada min ba, har take ce min ya kamata na nemi yan'uwa ko'in suke saboda wata rana. A lokacin na samu Nana na tisata a gaba ina tambayar wasu daga cikin yan'uwanta har take fada min harma da na Babana ma.
Misalin karfe biyu da yan mintuna na fito daga dakin na nufo gurin da muke zama a harabar asibitin inda shuke-shuke na zauna. Ban yi minti hudu da zama gurin ba sai ga kawata Farida ta zo, na jidadin zuwanta domin yau harabar babu mutanen da muka saba fira wasu an sallame su wasu kuma suna ciki gurin kula da masara lafiya, wadannn bakin fuskar kuma sun tsare ni da idonsu, dukuwa da nasa wannan kallon baya rasa nasaba da irin kyauna da kuma manyan idanuwan da Allah yai min haka zalika gashin kaina, shiyasa ba kasafai na ke son yin alwala a waje ba sai gaka hankali kowa ya dawo kaina duk da kasancewar gashin nawa a cinkushe yake guri daya har wani warin tsami yake, domin ba kitso nake masa ba idan am anyi kitson sai warware saboda sulbin gashi, kuma ba damuwa nai da na wanke ba balle har na shace shi ko na gyara.
Dambun da suka na masara ne ta riko mana, duk da kasancewar bana jin yunwa amman hakan be hana ni ci ba domin ina son dambu kusan duk wani abu da za a sarrafa shi da masara ko shimkafa ko dawa ina sonsa. Na ci dambu da yawa saboda yajin da aka cika a ciki domin ni ma'abociyar cin ya ji ce sosai, bayan mun gama fira ta shiga ciki ta duba Nana tai mata ta jiki sannan ta fito na rakota har bakin titin ringin sambo ina ta jin kamar na bita dan har ga Allah zaman asibitin ya fara ci min rai. A hanyata ta dawowa ne na hadu da Nurse Shukura tana sanye da uniform dinta amman ta dora bakar abaya sama ta rataya jakarta da alama ta tashi daga aikin ne zata tafi gida.

“Anty Shukura kin tashi ne”

“Eh sai kuma gobe, na kika fito?”

“Wallahi kawata na raka ina jin kamar na bita, zaman asibitin nan na ishemu”

Na fada ina yar dariya kadan, sai tai murmushi ta ce.

“Zama kan ai yanzu kuka fara tunda har kika ga Doc Asim ne yake kula da ku, in ma kina son mahaifiyarku ta samu lafiya to ki dauke ta daga asibitin nan ki kaita wata ko ku koma a gida, idan ba haka ba Wallahi za ki iya rasa mahaifiyarki asibitin nan ballantana yana ganin ba ku da kowa kin ga asirinsa rufe ba wanda zai san dalilin mutuwar mahaifiyarku”

Hankali na tashi da ji kalamanta har ya kasa boyuwa a fuska ta.

“Me kike Nufi Anty Shukura?”

“Bana nufin komai kawai baki ganin ciwon mahaifiyarki na ki ci ya ki cinyewa kullum kuna nan, ai ya kamata ki yi tunanin canja mata asibiti, kuma karki ce ni na baki shawara idan kin tashi kawai ki ce ke kin gaji gida za ku koma, Wallahi da masu kudi ne ku ko masu yan'uwan da yanzu an yi tunanin wata hanyar daban amman ba zama haka nan ba har kuna kokarin shiga wata na biyu asibitin nan, akan saran maciji kawai haba Ataa ke ma ai ya kamata ki yi tunani”

Tana gama fadar hakan ta yi wucewarta ta bar ni nan tsaye ina ta nazarin maganganunta, gaskiya ta fada wani gurin tabbas da masu kudi fa yanzu an canja nata asibiti amman kuma mu ba kamar su ba ne, kuma idan muka ce za mu canja asibiti kudin magani dawainiya wa zai yi da mu? Na san dai ba za mu hadu da dan albarka likita kamar wannan ba. In ta wannan sake saken na nufi cikin ward din tare da tunanin wata kila likitan be kware sosai ba shiyasa ka Nana ta gagara warkewa garau.

#Team Ataa
#Team Rahma
#Team Aliyu

Masu yi ma Rahama addu'ar mutuwa ita ma lafiyarta kawai take nema ita da mijinta 😀 amman kun fara dora mata tsana tun ba a je ko'ina ba 😑
https://my.w.tt/PWohUhlPv9.

*Z A K I*

By Khadeeja Candy

7️⃣
Chapter 10 · 0% Book details