← Book details Zaki Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 9 OF 143

Sashe 9

Zaki Part 1 Complete Hausa Novel · about 4 min read

“Komai zan miki Dear, na yi magana da Doc Asim dazu da rana har ya hada ni da likitan da za muje UK tare da shi, In-Sha-Allah within week din nan za mu gama duk wani shirye-shiyen sai muje can a saka miki, i will pay Doc Asim a huge of money saboda wannan abun da yai min, zan yi masa godiyar saving a billionaire naira wife”

Ya fada yana kissing din wuyanta, tare da saka halshensa yana wasa da gurin.

“I promise you idan kika samu lafiya ba zan raga miki ba”

Ya fada sound so sexy kamin ya shiga aika mata da sakwanni masu zafi.......

ATAA POV.

Lokacin da nurse din ta shigo ta dubata sai ta kalle a hartsine ta ce.

“Farkawa ne za tai, kuma wannan jinin ai dole ya fito tunda jiya akai tiyatar be gama bushewa ba”

Nurse din ta fada kamin ta kalleni.

“Ga ki kyakkyawa kin maida kanki kazama”

Ko kadan ban kula wata maganarta ba, wani dadi na ji ya lullube ni jin cewar farkawa ne Nana za ta yi, sai raina ya fara fari, wani irin shauki ya kamani na ji kamar na taba ta tai magana, ina ta kallon Nana kamin na maida dubana gurin Nurse din yadda ta saka tufafinta da yadda take aikinta sai ya burgeni daman na dade ina ganin sha'awar aikin likita ko unguwar zoma amman ba ni da wannan halin hali saboda ba ni da wannan gatan na karatu, wa na ke da shi da zai tsaya min nai karatu har na kai ga zama nurses ko likita? Ni da karatun secondary ma ya gagareni sai bara da aikin titi.
  Bayan ta fice na zauna a kujerar dake facing dinta Lukman kuma yai kwance kasa yana jin bachi, ido na kura mata tun ina kallonta da kyau har bachi ya soma sata na, shigowar likitan ce tasa na Nana tana bude idonta tana rufewa kamar bata san inda take ba. Ni nai saurin mikewa tsaye likitan kuma yai saurin karasowa kusa da ita ya shiga dubata sai na ga yana ta murmushi.

“Masha-Allah tiyata ta yi kyau, na sunanta?”

“Nana”

Na bashi amsa ina wani irin murmushi da ke bayyana irin farincikin da ke raina. Sai ya shiga kiran sunanta cikin ikon Allah da iyawarsa ta amsa muryarta can kasa kasa.

“Na'am”

“Sannu”

Ya ce da ita a lokacin da ta kalleshi. Sannan ni ma na fada.

“Sannu Nana”

Sai ta kalleni ta gyada min kai sai kuma ya dan dago kan kadan ta kalli cikinta da ke lullube da zane.

“Ina Lukman”

“Gashi yana bachi”

Na bata amsa da sauri.

“Waya kawo ni asibiti?”

“Ni na kawo ki maciji ne ya tsare ki, shine wannan likitan ya taimaka ya miki tiyata ya cire miki dafin kuma yai miki allura ya siya miki magani”

“Allah ya saka da alheri”

Ta fada daker tana kallonsa. Sai ya cire mata wasu abubuwan da ke jikinta ya kalli Lukman.

“Bari a samo muku abunda za ku rika kwana ko, ba ki san ana dauka cuta kasa ba da za ki bar shi ya kwanta”

Na yi shiru bance komai ba, shi kuma ya juya ya fice daga dakin. Be jima ba ya dawo tare da wasu masu sharar asibitin su hudu ko wannensu dauke da abubuwan bukata, tabarma ce da babban bargo da filo da kuma buta da carpet din sallah, dayan kuma abinci ne ya kawo mana. Wallahi sai na rasa da wanne baki zan yi ma likitan nan godiya da irin dawainiyar da yake da mu ko da shi ya haifi Nana iyaka kenan yadda yake kashe mana kudi sai ka ce ya sanmu.

“Za a kawo muku kayan tea gobe, ai kin iya gada shayi ko? Sai ki rika hada mata tana sha da fruits”

Ya fada bayan mutanen masu shara sun fita.

“Dan Allah ya sunanka?”

Na tambaya cike da fargabar yadda zai amsa min.

“Ina son na rika saka ka a addu'a ta ne idan nai, irin alherin da kake mana yayi yawa kana ta dawainiya da mu kamar ka san inda muka fito”

Kallo yai n wasu yan mintuna kamin ya dauke kansa tare da wani guntun numfashi ya ce.

“Ba komai ba sai kin min addu'a ba, Allah zai ba ni lada ai”
Chapter 9 · 0% Book details