Sashe 76
Zaki Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Ya furta yana karasowa zuwa inda na ke ya duba kan nawa, tashi nai zaune ina kallon yadda fuskarsa ta canja ganin bandeji a goshi idona har ya kumbura saboda kukan da nai na gaji.“Ba zai yiyu ba, yarinya kamar wannan ace zata sake shiga wani halin kuma, ta wanne zata ji da jin mahaifiyarta ko da kishin matarka? Kishin ya kai har ta saka aje a fasa mata kai? Wannan wane irin rashin mutunci ne? Idan ma sun ta kake yin hakan zai saka ka fasa ne? Shi kenan dam tana talaka ba da daraja da kima a gurinku? Idan yar wani Minister ta ce Rahma ta isa ta dake ta ma balle har ta nuna mata yatsa? Da ace ita ce ta yi ma Rahma haka ina da tabbacin yau Ataa a gidan yari zata kwana saboda ta taba yar gata, to ya bata fi ya ba Rahma dan ta tana yar masu arziki bata fi Ataa ba dukansu mutane ne, suna zamansu lafiya cikin rufin asiri za su tashi hankalinta da na mahaifiyarta, ita Rahma idan mai tunani ce ai kamata yai ta kama Ataa ta rike ta martaba ta kodar mahaifiyarta ce a cikim cikinta fa, tasan bata da lafiya idan Allah ya ga dama sai ta fadi ta mutu a take amman sai neman wulakanta wata take? Idan ma son ta kake ta isa ta hana ne? Wallahi ka jawa matarka kunne idan ba haka fadan a tsakanin mu zai dawo domin ba zan zuba ido su cewa Ataa mutunci ba, idan ma ai kake goya mata baya to ko kuma ka kwashi matarka ku koma can Abuja.....!”
Tana kawai nan ta tashi a ficewa ta nufi dakinta ba tare da ta tsaya sauraren abunda Aliyu zai fada ba. Tun da take fadan na ke kallonta ina hawaye cike da kauna marar misaltuwa, wata uwa bata taba tsaya ta shigar min fada ba bayan Nana amman a yau na samu wata mace da ta rike ni 'ya har ta take fada da danta akan abunda surukarta tai min, ciwon kan da zazzabin da suke son rufe ni a take na neme su na rasa, wani irin kaunar Momy ya cika min zuciyata, hakika ta uwa Momy uwa ta gari ce mai iya kula da yayan kowa kamar yayanta. Risinawa Aliyu yai gabana yana kallon fuskata a hankali ya shiga min magana.
“Sannu”
Na gyada masa kai tare da saka hannu na share hawayena.
“Wacce ta dake ki cewa tai Rahma ta turo ta?”
Na girgiza kai.
“Bude ba ki yi min magana mana”
Kasa nai da kaina haka nan kawai na samu kaina da kasa bude baki na ce masa komai har na tsawon lokaci. Tashi nai tsaye na soma takawa da zimmar shiga bathroom din Amina saboda fitsarin da suka cika min mara, sai na ji ya kira Husna da ke kitchen ta fito da sauri.
“Rika ta ki kai ta daki”
Sai da ta kalleshi sannan ta zo ta rika ni ta nufi dakinta da ni a maimakon dakin Amina.“Kwantawa za ki yi?”
“A a fitsari zan yi”
Bandakin ta nufa da ni sai da muka shiga ciki sai ta fito, bayan na gama abunda zan yi na fito sai na zauna kasa na jingina da gadonta, murmushi na ke abunda Momy ta yi min ya faranta min rai sosai, Husna na shigowa dakin ta saka na tashi daga kasa na koma saman gadonta na kwanta, nan da nan bachi yai gaba da ni.
ALIYU POV.
Da kallo ya bi Ataa wance Husna ke rike da ita har suka shige dakin. Yana ta mamakin abunda Rahma tai bayan yau da ita ya wuni saboda ita ne be je ko'ina ba. Mikewa yai tsaye ya fice daga falon zuwa motarsa, yana shiga ya dauki hanyar gidansa. Harabar gidan ya faka motarsa yana kallon wata bakuwar mota da ke fake a gafen ta Rahma, ya fito yana rike da keys din motarsa a hannunsa ya tura kofar falon ya shiga. Rahma ya samu zaune ita da Muneera a kujera daya, da alama fira suke yi ko kuma wani abun Muneera take fadawa Rahma sai dai ganinsa ya saka sun yi shiru.
“Sannu da zuwa”
Rahma ta fada sai yai mata banza ya nufi upstairs.
“Ranka ya bace saboda an gargadi wata banza”
Ta fada tana mikewa tsaye, shi kuma ya juyo ya kalleta.
“Akan me za ki nemi takurwa yar mutane? Ce miki nai ina sonta? And what makes you think abunda kika saka ka mata zai sa na canja na fasa taimakonta ne? Wallahi abunda kika yi be kara min komai ba sai tausayinta, yarinyar da ke jinyar mahaifiyarta saboda ke a maimakon ki tausaya mata ki taimake ta sai neman saka ta kike a cikin wata fitinar, matace ke ina martaba ki ina mutuntaki ba zan bari wani ya zaga miki rigar mutunci ba, kamar yadda ba ba zan bari ki yagawa wani ba wanin ma kuma wacce ta taimake ki rayuwarki”
Ya fada cikin daga muryar fuskarsa a hade kamar bakin hadari.
“Abunda kake yi abun kunya ne Aliyu namiji mai daraja mai kima da mutumci kamar ka ace yana bibiyar wata banza yar talakawa yar bara a titi wacce bata san mutuncin kanta ba, namiji nawa na kwanta da ita lokacin da take bara baka sani ba, amman abun kunya har ka dauki robe da cake ka bata zobe ma mai tsada wanda na yi imani bata taba ganin irinsa a rayuwarta, ka yi kuskure Aliyu kuma kana shirin aikata kuskure idan har ka ce zaka hada ni kishi da wata kazama wacce ba a san ubanta ba balle asalinta, wannan ne kuskure mafi girma da zaka aikata hada ni kishi da yar talaka, abunda za ka yi ka burgeni ka nemo yar wani minister ko yar wani mai ji da kansa ka hada ni shi da ita amman ba yar iska yar gantali a titi ba, wacce ta kwana a titi yan sanda suka gama amfani da ita Doc Asim ya gama amfani da ita kai kuma yanzu kake son kawota cikin gidanka”
Tana fadar hakan ta juya sai Aliyu ya juyo da ita da dukan karfinsa yana kallonta naman fuskarsa har rawa yake saboda bacin rai.
“Idan zan so Ataa ba zan so ta dan wani abu nata ba, kamar yadda ke ma ban so ki dan wani abu na ki ko na gidanku ba, ban taba son mace dan wani abu nata ba kin fi kowa sanin wannan”
“Ba haka ba ne, ka so ni a yadda na ke saboda ka san cewa baka haihuwa saboda kai juya ne, so that sai mu taru mu mutu a haka, yanzu kuma kana ganin ka gaji da ni mahaifiyarka ta saka ni a gaba shine zaka fara son wata ko? Watan ma yar titi wacce kai da kanka kake nuna mata kyama amman mahaifiyarta take kokarin gyarata saboda kana sonta, daman na sani yan'uwanka gaba daya ba so na suke ba”
“Ba ki da kunya Rahma, kina magana kamar ba ki san da wanda ki ke magana ba, mi yake damun ki ne?”
“Abunda yake damunka Aliyu, abunda ya saka ka canja ka koma kamar mahaukaci akan wata dabba can, shiyasa na gano matsala da kai idan har zaka iya runtse ido a halin da muke ciki ka ce zaka min kishi to sai an bata guri ta zo ta zauna da kai fa haihu na gani”
“Za ki yi nadama matukar kika ce Zabin Rai za ki bi, ina daga miki kafa ne saboda sanin abunda yake tare da ke, ina tausayin ranar da za ki yi nadama Rahma, wulakanta dan 'adam ba shi da kyau musamman wanda ya taimaki rayuwarka”
Wani kallon mamaki tai masa
“Haka ka fadan to sai kaje ka aureta ka zauna da ita, daman ai haka halin ku maza yake”
Ya nufi hanyar dakinta a fusace tana wugar da zoben.Aliyu ya juyo gurin Muneera ya kwada mata mari mai kyau sai da ta jishi har cikin kanta.
“Karki sake zuwa ki ce za ki taba yarinyar mutane, duk wani abu a tsakanina da Rahma ne babu ruwanku a ciki”
Ta dafe kuncin hawaye na sauko mata tace.
“Saboda wata banza yar talakawa za ka mare ni Aliyu?”
Kara mata marin yai a dayar fuskarta sai ta hada hannu biyu da dafe fuskarta tana fashewa da kuka.
“Talaka ai ta muku rana, ko ba kodar talaka ce a jikin yayarki ba? Ku ba ku san darajar talaka ba amman kun iya wulakanta shi? Bana son wuce gona da iri, ki tsaya a matsayinki na kanwar matata babu ruwanki da rayuwarmu, kuma ki fice min daga gida yanzu nan”
Kamar kyaftawar ido haka ta fice daga falon har lokacin da ta kai gurin motarta bata dauke hannunta daga kan fuskarta ba dan har lokacin bata daina jin zafin marin da yai mata ba.
Rahma na shiga dakinta ta dauko makullin motarta da mayafinta ta fito cikin fushi ta fice daga gidan.
Tana kawai nan ta tashi a ficewa ta nufi dakinta ba tare da ta tsaya sauraren abunda Aliyu zai fada ba. Tun da take fadan na ke kallonta ina hawaye cike da kauna marar misaltuwa, wata uwa bata taba tsaya ta shigar min fada ba bayan Nana amman a yau na samu wata mace da ta rike ni 'ya har ta take fada da danta akan abunda surukarta tai min, ciwon kan da zazzabin da suke son rufe ni a take na neme su na rasa, wani irin kaunar Momy ya cika min zuciyata, hakika ta uwa Momy uwa ta gari ce mai iya kula da yayan kowa kamar yayanta. Risinawa Aliyu yai gabana yana kallon fuskata a hankali ya shiga min magana.
“Sannu”
Na gyada masa kai tare da saka hannu na share hawayena.
“Wacce ta dake ki cewa tai Rahma ta turo ta?”
Na girgiza kai.
“Bude ba ki yi min magana mana”
Kasa nai da kaina haka nan kawai na samu kaina da kasa bude baki na ce masa komai har na tsawon lokaci. Tashi nai tsaye na soma takawa da zimmar shiga bathroom din Amina saboda fitsarin da suka cika min mara, sai na ji ya kira Husna da ke kitchen ta fito da sauri.
“Rika ta ki kai ta daki”
Sai da ta kalleshi sannan ta zo ta rika ni ta nufi dakinta da ni a maimakon dakin Amina.“Kwantawa za ki yi?”
“A a fitsari zan yi”
Bandakin ta nufa da ni sai da muka shiga ciki sai ta fito, bayan na gama abunda zan yi na fito sai na zauna kasa na jingina da gadonta, murmushi na ke abunda Momy ta yi min ya faranta min rai sosai, Husna na shigowa dakin ta saka na tashi daga kasa na koma saman gadonta na kwanta, nan da nan bachi yai gaba da ni.
ALIYU POV.
Da kallo ya bi Ataa wance Husna ke rike da ita har suka shige dakin. Yana ta mamakin abunda Rahma tai bayan yau da ita ya wuni saboda ita ne be je ko'ina ba. Mikewa yai tsaye ya fice daga falon zuwa motarsa, yana shiga ya dauki hanyar gidansa. Harabar gidan ya faka motarsa yana kallon wata bakuwar mota da ke fake a gafen ta Rahma, ya fito yana rike da keys din motarsa a hannunsa ya tura kofar falon ya shiga. Rahma ya samu zaune ita da Muneera a kujera daya, da alama fira suke yi ko kuma wani abun Muneera take fadawa Rahma sai dai ganinsa ya saka sun yi shiru.
“Sannu da zuwa”
Rahma ta fada sai yai mata banza ya nufi upstairs.
“Ranka ya bace saboda an gargadi wata banza”
Ta fada tana mikewa tsaye, shi kuma ya juyo ya kalleta.
“Akan me za ki nemi takurwa yar mutane? Ce miki nai ina sonta? And what makes you think abunda kika saka ka mata zai sa na canja na fasa taimakonta ne? Wallahi abunda kika yi be kara min komai ba sai tausayinta, yarinyar da ke jinyar mahaifiyarta saboda ke a maimakon ki tausaya mata ki taimake ta sai neman saka ta kike a cikin wata fitinar, matace ke ina martaba ki ina mutuntaki ba zan bari wani ya zaga miki rigar mutunci ba, kamar yadda ba ba zan bari ki yagawa wani ba wanin ma kuma wacce ta taimake ki rayuwarki”
Ya fada cikin daga muryar fuskarsa a hade kamar bakin hadari.
“Abunda kake yi abun kunya ne Aliyu namiji mai daraja mai kima da mutumci kamar ka ace yana bibiyar wata banza yar talakawa yar bara a titi wacce bata san mutuncin kanta ba, namiji nawa na kwanta da ita lokacin da take bara baka sani ba, amman abun kunya har ka dauki robe da cake ka bata zobe ma mai tsada wanda na yi imani bata taba ganin irinsa a rayuwarta, ka yi kuskure Aliyu kuma kana shirin aikata kuskure idan har ka ce zaka hada ni kishi da wata kazama wacce ba a san ubanta ba balle asalinta, wannan ne kuskure mafi girma da zaka aikata hada ni kishi da yar talaka, abunda za ka yi ka burgeni ka nemo yar wani minister ko yar wani mai ji da kansa ka hada ni shi da ita amman ba yar iska yar gantali a titi ba, wacce ta kwana a titi yan sanda suka gama amfani da ita Doc Asim ya gama amfani da ita kai kuma yanzu kake son kawota cikin gidanka”
Tana fadar hakan ta juya sai Aliyu ya juyo da ita da dukan karfinsa yana kallonta naman fuskarsa har rawa yake saboda bacin rai.
“Idan zan so Ataa ba zan so ta dan wani abu nata ba, kamar yadda ke ma ban so ki dan wani abu na ki ko na gidanku ba, ban taba son mace dan wani abu nata ba kin fi kowa sanin wannan”
“Ba haka ba ne, ka so ni a yadda na ke saboda ka san cewa baka haihuwa saboda kai juya ne, so that sai mu taru mu mutu a haka, yanzu kuma kana ganin ka gaji da ni mahaifiyarka ta saka ni a gaba shine zaka fara son wata ko? Watan ma yar titi wacce kai da kanka kake nuna mata kyama amman mahaifiyarta take kokarin gyarata saboda kana sonta, daman na sani yan'uwanka gaba daya ba so na suke ba”
“Ba ki da kunya Rahma, kina magana kamar ba ki san da wanda ki ke magana ba, mi yake damun ki ne?”
“Abunda yake damunka Aliyu, abunda ya saka ka canja ka koma kamar mahaukaci akan wata dabba can, shiyasa na gano matsala da kai idan har zaka iya runtse ido a halin da muke ciki ka ce zaka min kishi to sai an bata guri ta zo ta zauna da kai fa haihu na gani”
“Za ki yi nadama matukar kika ce Zabin Rai za ki bi, ina daga miki kafa ne saboda sanin abunda yake tare da ke, ina tausayin ranar da za ki yi nadama Rahma, wulakanta dan 'adam ba shi da kyau musamman wanda ya taimaki rayuwarka”
Wani kallon mamaki tai masa
“Haka ka fadan to sai kaje ka aureta ka zauna da ita, daman ai haka halin ku maza yake”
Ya nufi hanyar dakinta a fusace tana wugar da zoben.Aliyu ya juyo gurin Muneera ya kwada mata mari mai kyau sai da ta jishi har cikin kanta.
“Karki sake zuwa ki ce za ki taba yarinyar mutane, duk wani abu a tsakanina da Rahma ne babu ruwanku a ciki”
Ta dafe kuncin hawaye na sauko mata tace.
“Saboda wata banza yar talakawa za ka mare ni Aliyu?”
Kara mata marin yai a dayar fuskarta sai ta hada hannu biyu da dafe fuskarta tana fashewa da kuka.
“Talaka ai ta muku rana, ko ba kodar talaka ce a jikin yayarki ba? Ku ba ku san darajar talaka ba amman kun iya wulakanta shi? Bana son wuce gona da iri, ki tsaya a matsayinki na kanwar matata babu ruwanki da rayuwarmu, kuma ki fice min daga gida yanzu nan”
Kamar kyaftawar ido haka ta fice daga falon har lokacin da ta kai gurin motarta bata dauke hannunta daga kan fuskarta ba dan har lokacin bata daina jin zafin marin da yai mata ba.
Rahma na shiga dakinta ta dauko makullin motarta da mayafinta ta fito cikin fushi ta fice daga gidan.