Sashe 34
Zaki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Na yi zaton kema kin dauki ni kamar yar ki ne za ki share min hawayena shiyasa na kawo kukana a gurinki”
Ta fada hawaye na sauko mata sannan ta mike tsaye ta dauki veil dinta ta fito Momy na binta da kallo. Haka ta fito hawaye na sauko mata amman bata damu da ta share ba, duk a maganganun da Momy tai mata ta fi jin zafin na haihuwa, taya Momy za tai mata wannan maganar kamar ba ta san Allah ne yake komai ba? Ta sani ita kanta bata da matsala Aliyu ma bashi da matsala so zata iya haihuwa a duk lokacin da Allah ya so. Amman bayan Mama Fulani a yau ma Momy ta yi mata gorin haihuwa. A maimakon ta koma gida sai ta wuce family house dinsu gurin Mommy ta da Daddy su da take ganin kamar sun fi kowa kaunarta a duniya, domin tana da tabbacin da su ta kaiwa kukanta tun farko da basu mata bakar magana kamar yadda Momy tai mata ba. Daf da kofar shiga falon ta faka motarta sannan ta fita tana hawaye har lokacin ta shiga falon. Mutane ta samu da dama a falon suna ta hidimar canja decorations din Falon ko ba a fada mata ba tasan Mai gidan Daddybsu ne zai zo wato Alhaji Bashiru Muhammdu Sarkin Agades, domin ta san a duk lokacin da zai zo sai Daddy ya saka an yi gyaran gidan, kuma an gyara masa masaukinsa, daman tun gobarar da ta faru be zo ba kuma be aiko kowa ya yi ma Daddy jaje ba, kasancewar Daddy yayi hasarar dukiya mai yawa a Shopping mall din nan daya kone, domin shopping mall din ya yafi ko wane kawo kudi kuma shi ne wanda kudin Daddy zalla a ciki ba da na mai gidansa ba.
Mommy na zaune a falon tana kallon yadda ake saka labulayen Rahma ta shigo yadda ta ga fuskarsa da ganinta a wannan lokacin ta san ba lafiya ba, hakan yasa hankalinta yai mugun tashi har ta kasa hakura ta kawo kusa da ita ta tashi ta tarbeta.
“Ke lafiya?”
“Momy Aliyu wata yake so?”
“Wata yake so, wata wa? Waya fada miki”
A nan ta narke a kasa ta fashe da kuka wanda hakan yasa hankalin Mommy kara tashi ta rikata itama tana fashewa da kuka.
“Rahma ki fada min minene?”
Daker tai shiru har ta iya zanawa Mommy abunda ya faru, sai Mommy rika hannunta suka nufi part din Daddynta, Mommy tai masa bayanin komai a take shi ma ransa ya bace musamman da ya ga yadda yar lelensa take kuka. A take ya daga waya ya kira Aliyu ya ce ya zo ya same shi a gida, ba a dauki thirty minutes ba sai ga Aliyu zaune a falon daddy daman he used to respect his in-laws da kuma iyayensa da matarsa duk abunda ya shafi nan baya wasa da shi.
Daddy ne ya fara kora masa da bayani kamin Mommy ta dora da nata cikin fada.
“Be ma kyautu ace ka fara son wata ba Aliyu, kasan halin da Rahma take ciki idan kace zaka mata kishiya da wanne kake son ta ji?”
Tun da suke maganar yake ta kallonsu har sukai suka gama sannan ya kalli Rahma ya ce.
“Lokacin da zan aureki na fada miki cewar da ke kadai zan zauna? Na miki wannan alkawarin ke kadai za ki zauna?”
Rahma ba tace komai ba sai kuka take, sannan ya kalli Daddy da Mommy ya ce.
“Ciyar da yarku shayarda ita nema mata lafiya abu ne daya rataya a kaina, kuma shi ya kamata ku tuhume ni da shi idan ban mata ba, ba wai zancen karin aure ko kin sa ba, wannan abu ne da ke tsakanin ni da ita, matsala da za mu iya gyarata a tsakaninmu, ku hukunta ni idan na tsallake daya daga cikin abunda musulunci ya ce nai mata na take na ki nai amman ba wannan ba”
“To rashin kunya za ka mana kanan ko?”
Mommy ta fada tana watsa masa wani kallo kamar ba sukurinta ba.
“Babu zancen rashin kunya a ciki Mommy, Rahma ta yi ba daidai ba kamata yai ku fada mana ku nuna mata abunda tai ba daidai ba ne, ba wai ku kirani ku tsare kamar haka ba”
Daddyn kan mamaki da kataici ya hana shi cewar komai sai wani kallo yake watsawa Aliyu ta cikin gilashin idonsa, ya manta da cewar Aliyu mai arziki ne dan mai arziki dan gin amsu arziki, da dai ace talaka ne yake auren yarsu da za su iya juya shi yadda suke so amman ba mai arzikin da baya jiran abun hannunsu kamar Aliyu ba. Jin babu wanda ya sake cewa komai yasa shi kallon Daddy ya ce.
“Akwai wata matsalar ne bayan wannan?”
“Lallai Aliyu wuyanka yai kauri wato ita wannan ba matsala ba ce ko?”
Daddy ya fada, Aliyu dai be ce komai ba sai kallon Rahma yake da idon da ke nuna ya fusata sosai.
“Daddy ka bar shi kawai zan yi magana da shi”
Rahma ta fada tana dagowa daga jikin Mommy ta dake kokarin riketa.
“Babu inda za ki bishi yaje yai ta cusa miki bakinciki a zuciyata ya akashe mana ke da ranki”
“Aa Mommy zan yi magana da shi, daman ban yi magana da shi ba ne na fada muku, idan abun ya gagara zan...”
Sai kuma tai shiru bata karasa ba, tana tsoron kar ran iyayenta ya bace su hanata komawa gidan sahibinta ko wata matsalar wacce ta fi wannan ta shiga.
“Sai da safen ku”
Aliyu ya fada yana mikewa tsaye ya fice daga falon, da sauri Rahma ta bi bayansa wanda hakan yasa ran Mommy baci son tai ta riketa a gidan har sai Aliyu ya gane kurensa. A tare suka iso gurin motarsa Rahma na ta kallon fuskarsa ko zai kalleta amman be kalleta har ya bude motarsa ya shiga ya danna horn aka bude masa gate ya fice ya barta a gurin tsaye. Da sauri itama ta shiga motarta ta bishi ko da ta isa gidan ta samu har ya shiga dakinsa yana kokarin cire tufafin jikinsa. Jikinta a sanyaye ta shiga dakin tana ta kallonsa amman ko inda take be kalla ba, har ya cire tufafin ya daura tawul ya shiga yai wanka ya fito tana a gurin zaune, so take ta masa magana kuma bata san mi zata ce masa ba, har ta gaji da zaman ta tashi ta koma dakinta ta shiga bathroom tai alwala ta gabatar da sallah isha'i, bayan ta gama ta hau saman gadon ta zauna, ta san ba zai shigo dakinta ba tun da yana fushi da ita, kuma idan taje can ba kula zai yi ba. A saman gadon tai ta juyi bachi ya ki daukarta, sauka tai daga saman gadon ta nufi dakinsa tana hawaye ta tura kofar ta shiga sai ta hango shi saman gado kwance. Bayansa ta kwanta ya kai hannu ta taba kansa.
“Dan Allah ka yi hakuri ba zan sake ba”
Shiru be ce mata komai ba, ta sake fada be ce komai ba ko matsawa be yi ba sai da kwanta bayansa tana kuka, sannan ya tashi zaune ita ta tashi zaune tana kallonsa.
“Matsalar da ke tsakaninmu wacce za mu iya solving sai ace sai kin dauka kin kai gidanku? Idan ma zan kara aurene kina tunanin yin haka zai saka na fasa? Duk abubuwan da nake miki Rahma saboda ina son ki ne, kuma ina taka tsantsan da lafiyarki ne, ba wai dan ki juyani kamar dan ki ba”
“I'm sorry”
Ta fada da muryar kuka tana kama hannunsa, a sannan ya jimke hannunsa cikin nata alamar ya hakura kenan ya kai bakinsa ya sumbanci goshinta.
“Wannan ya zama first and last, dan ba zan dauka ba”
“Ba zan sake ba”
Ta fada tana ta kallonsa, sai ya jata jikinsa ya rumgume suka kwanta tare. After like one hour ta dan dago kanta tana kallonsa ta ce.
“Aliyu kana son haihuwa ko? Kana son yara right”
“Yes”
“Amman baka taba nuna min ba”
“Saboda karki damu ne, kuma ga lalurar da kike fama da ita shiyasa ban damu da ki samu cikin ba”
Hannu ta kai ta shafa fuskarsa.
“Zan samu ciki zan saka ka farinciki In-Sha-Allah, zan haihuwa duk inda haihuwa ta kai sai na samo ta, zan kashe ko nawa ne na haihu Aliyu just for you”
Murmushi yai ya sake sumbantarta.
“Allah ya bamu mai albarka”
“Amin”
Ta fada tana kara kankameshi.
“Amman ina son mu koma Abuja, hankali zai fi kwanciya idan muna can”
“Yaushe kike son mu koma?”
“Jibi”
“To ki fara shiri daga yanzu”
“Thank you, i love you”
“I love you too”
Lumshe ido tana sauraren sakwannin da yake aika mata masu zafi.
ATAA POV.
A lokacin da na shiga Bathroom din sai da nai fitsari a bandaki sannan na wanke shi, na fito na gyara bedroom din na fesa turare kamar yadda aka fada min, haka na bi duka dakunan na gyara ko wannen sannan na sauko da kayan mopping din na nufi inda na daukosu na aje.
“Ke je ki cire Hijab din nan karna sake ganinki da shi sai idan fita za ayi, a cikin gidan ki yi ta saka mana Hijab kina watsa mana kora”
Ta fada hawaye na sauko mata sannan ta mike tsaye ta dauki veil dinta ta fito Momy na binta da kallo. Haka ta fito hawaye na sauko mata amman bata damu da ta share ba, duk a maganganun da Momy tai mata ta fi jin zafin na haihuwa, taya Momy za tai mata wannan maganar kamar ba ta san Allah ne yake komai ba? Ta sani ita kanta bata da matsala Aliyu ma bashi da matsala so zata iya haihuwa a duk lokacin da Allah ya so. Amman bayan Mama Fulani a yau ma Momy ta yi mata gorin haihuwa. A maimakon ta koma gida sai ta wuce family house dinsu gurin Mommy ta da Daddy su da take ganin kamar sun fi kowa kaunarta a duniya, domin tana da tabbacin da su ta kaiwa kukanta tun farko da basu mata bakar magana kamar yadda Momy tai mata ba. Daf da kofar shiga falon ta faka motarta sannan ta fita tana hawaye har lokacin ta shiga falon. Mutane ta samu da dama a falon suna ta hidimar canja decorations din Falon ko ba a fada mata ba tasan Mai gidan Daddybsu ne zai zo wato Alhaji Bashiru Muhammdu Sarkin Agades, domin ta san a duk lokacin da zai zo sai Daddy ya saka an yi gyaran gidan, kuma an gyara masa masaukinsa, daman tun gobarar da ta faru be zo ba kuma be aiko kowa ya yi ma Daddy jaje ba, kasancewar Daddy yayi hasarar dukiya mai yawa a Shopping mall din nan daya kone, domin shopping mall din ya yafi ko wane kawo kudi kuma shi ne wanda kudin Daddy zalla a ciki ba da na mai gidansa ba.
Mommy na zaune a falon tana kallon yadda ake saka labulayen Rahma ta shigo yadda ta ga fuskarsa da ganinta a wannan lokacin ta san ba lafiya ba, hakan yasa hankalinta yai mugun tashi har ta kasa hakura ta kawo kusa da ita ta tashi ta tarbeta.
“Ke lafiya?”
“Momy Aliyu wata yake so?”
“Wata yake so, wata wa? Waya fada miki”
A nan ta narke a kasa ta fashe da kuka wanda hakan yasa hankalin Mommy kara tashi ta rikata itama tana fashewa da kuka.
“Rahma ki fada min minene?”
Daker tai shiru har ta iya zanawa Mommy abunda ya faru, sai Mommy rika hannunta suka nufi part din Daddynta, Mommy tai masa bayanin komai a take shi ma ransa ya bace musamman da ya ga yadda yar lelensa take kuka. A take ya daga waya ya kira Aliyu ya ce ya zo ya same shi a gida, ba a dauki thirty minutes ba sai ga Aliyu zaune a falon daddy daman he used to respect his in-laws da kuma iyayensa da matarsa duk abunda ya shafi nan baya wasa da shi.
Daddy ne ya fara kora masa da bayani kamin Mommy ta dora da nata cikin fada.
“Be ma kyautu ace ka fara son wata ba Aliyu, kasan halin da Rahma take ciki idan kace zaka mata kishiya da wanne kake son ta ji?”
Tun da suke maganar yake ta kallonsu har sukai suka gama sannan ya kalli Rahma ya ce.
“Lokacin da zan aureki na fada miki cewar da ke kadai zan zauna? Na miki wannan alkawarin ke kadai za ki zauna?”
Rahma ba tace komai ba sai kuka take, sannan ya kalli Daddy da Mommy ya ce.
“Ciyar da yarku shayarda ita nema mata lafiya abu ne daya rataya a kaina, kuma shi ya kamata ku tuhume ni da shi idan ban mata ba, ba wai zancen karin aure ko kin sa ba, wannan abu ne da ke tsakanin ni da ita, matsala da za mu iya gyarata a tsakaninmu, ku hukunta ni idan na tsallake daya daga cikin abunda musulunci ya ce nai mata na take na ki nai amman ba wannan ba”
“To rashin kunya za ka mana kanan ko?”
Mommy ta fada tana watsa masa wani kallo kamar ba sukurinta ba.
“Babu zancen rashin kunya a ciki Mommy, Rahma ta yi ba daidai ba kamata yai ku fada mana ku nuna mata abunda tai ba daidai ba ne, ba wai ku kirani ku tsare kamar haka ba”
Daddyn kan mamaki da kataici ya hana shi cewar komai sai wani kallo yake watsawa Aliyu ta cikin gilashin idonsa, ya manta da cewar Aliyu mai arziki ne dan mai arziki dan gin amsu arziki, da dai ace talaka ne yake auren yarsu da za su iya juya shi yadda suke so amman ba mai arzikin da baya jiran abun hannunsu kamar Aliyu ba. Jin babu wanda ya sake cewa komai yasa shi kallon Daddy ya ce.
“Akwai wata matsalar ne bayan wannan?”
“Lallai Aliyu wuyanka yai kauri wato ita wannan ba matsala ba ce ko?”
Daddy ya fada, Aliyu dai be ce komai ba sai kallon Rahma yake da idon da ke nuna ya fusata sosai.
“Daddy ka bar shi kawai zan yi magana da shi”
Rahma ta fada tana dagowa daga jikin Mommy ta dake kokarin riketa.
“Babu inda za ki bishi yaje yai ta cusa miki bakinciki a zuciyata ya akashe mana ke da ranki”
“Aa Mommy zan yi magana da shi, daman ban yi magana da shi ba ne na fada muku, idan abun ya gagara zan...”
Sai kuma tai shiru bata karasa ba, tana tsoron kar ran iyayenta ya bace su hanata komawa gidan sahibinta ko wata matsalar wacce ta fi wannan ta shiga.
“Sai da safen ku”
Aliyu ya fada yana mikewa tsaye ya fice daga falon, da sauri Rahma ta bi bayansa wanda hakan yasa ran Mommy baci son tai ta riketa a gidan har sai Aliyu ya gane kurensa. A tare suka iso gurin motarsa Rahma na ta kallon fuskarsa ko zai kalleta amman be kalleta har ya bude motarsa ya shiga ya danna horn aka bude masa gate ya fice ya barta a gurin tsaye. Da sauri itama ta shiga motarta ta bishi ko da ta isa gidan ta samu har ya shiga dakinsa yana kokarin cire tufafin jikinsa. Jikinta a sanyaye ta shiga dakin tana ta kallonsa amman ko inda take be kalla ba, har ya cire tufafin ya daura tawul ya shiga yai wanka ya fito tana a gurin zaune, so take ta masa magana kuma bata san mi zata ce masa ba, har ta gaji da zaman ta tashi ta koma dakinta ta shiga bathroom tai alwala ta gabatar da sallah isha'i, bayan ta gama ta hau saman gadon ta zauna, ta san ba zai shigo dakinta ba tun da yana fushi da ita, kuma idan taje can ba kula zai yi ba. A saman gadon tai ta juyi bachi ya ki daukarta, sauka tai daga saman gadon ta nufi dakinsa tana hawaye ta tura kofar ta shiga sai ta hango shi saman gado kwance. Bayansa ta kwanta ya kai hannu ta taba kansa.
“Dan Allah ka yi hakuri ba zan sake ba”
Shiru be ce mata komai ba, ta sake fada be ce komai ba ko matsawa be yi ba sai da kwanta bayansa tana kuka, sannan ya tashi zaune ita ta tashi zaune tana kallonsa.
“Matsalar da ke tsakaninmu wacce za mu iya solving sai ace sai kin dauka kin kai gidanku? Idan ma zan kara aurene kina tunanin yin haka zai saka na fasa? Duk abubuwan da nake miki Rahma saboda ina son ki ne, kuma ina taka tsantsan da lafiyarki ne, ba wai dan ki juyani kamar dan ki ba”
“I'm sorry”
Ta fada da muryar kuka tana kama hannunsa, a sannan ya jimke hannunsa cikin nata alamar ya hakura kenan ya kai bakinsa ya sumbanci goshinta.
“Wannan ya zama first and last, dan ba zan dauka ba”
“Ba zan sake ba”
Ta fada tana ta kallonsa, sai ya jata jikinsa ya rumgume suka kwanta tare. After like one hour ta dan dago kanta tana kallonsa ta ce.
“Aliyu kana son haihuwa ko? Kana son yara right”
“Yes”
“Amman baka taba nuna min ba”
“Saboda karki damu ne, kuma ga lalurar da kike fama da ita shiyasa ban damu da ki samu cikin ba”
Hannu ta kai ta shafa fuskarsa.
“Zan samu ciki zan saka ka farinciki In-Sha-Allah, zan haihuwa duk inda haihuwa ta kai sai na samo ta, zan kashe ko nawa ne na haihu Aliyu just for you”
Murmushi yai ya sake sumbantarta.
“Allah ya bamu mai albarka”
“Amin”
Ta fada tana kara kankameshi.
“Amman ina son mu koma Abuja, hankali zai fi kwanciya idan muna can”
“Yaushe kike son mu koma?”
“Jibi”
“To ki fara shiri daga yanzu”
“Thank you, i love you”
“I love you too”
Lumshe ido tana sauraren sakwannin da yake aika mata masu zafi.
ATAA POV.
A lokacin da na shiga Bathroom din sai da nai fitsari a bandaki sannan na wanke shi, na fito na gyara bedroom din na fesa turare kamar yadda aka fada min, haka na bi duka dakunan na gyara ko wannen sannan na sauko da kayan mopping din na nufi inda na daukosu na aje.
“Ke je ki cire Hijab din nan karna sake ganinki da shi sai idan fita za ayi, a cikin gidan ki yi ta saka mana Hijab kina watsa mana kora”