Sashe 84
Zaki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“A a ba mu da madubi ai”
Ataa ta fada tana murmushi.
“Zo na nuna miki kanki a wayana”
Ya zauna a kujerar da ke kusa da shi yana ciro wayar daga aljihunsa na gaba, bata zauna din ba ta juyo ta kalli Aliyu wanda idonsa ke kan wayarsa tunawa da yace ta daina sakewa Muhseen.
“a a bari na je na duba a Mota”
Ya fada sannan ta fara takawa zata wuce Muhseen ya bi bayanta da kallo komai na jikinta motsi yake a cikin uniform din kasancewarta mai tubultubul kuma uniform din ya dan kama jikinta din jiki ga shi bata da komai a ciki, da gangan yai hanzarin kai hannunsa ya kama gashin kanta ya juyo da ita ta rika yatsun hannunta.
“Pretty ina zoben da na baki...?”
Bata amsa shi ba tai saurin fisge hannunta tana kallon Aliyu hankalinta a tashe kamar wacce za ayi ma wani abu.
“Muhseen....!”
Aliyu ya daka masa tsawa a cikin muryar da shi kan shi be san da zamanta ba.
“Karka sake kuskuren yabon kyau Ataa balle ka ce zaka kai dan iskan hannunta ka taba ta, wannan ya zama na karshe ina nufi na karshe....”
Magana Aliyu yake ma Muhseen cikin tsawa yana nuna Muhseen da yatsansa kwayar idonsa gaba daya ta canja ta rine kamar ba shi ne da farin ido ba, shi kan shi Muhseen sai da gabashi ya fadi domin ya razana sosai da yanayin da ya ga Aliyu. Kamar kyalftawar walkiya haka Ataa ta bace bat a cikin falon kamin ta isa Bq har da gudunta, ganin irin tsawar da yai ma Muhseen da yake kanensa kuma dan'uwansa to ita kan ta san nata dukanta zai yi. Da sauri Momy ta fito daga kitchen tana kallonsu, kannensa ma Amina, Siyama da Husna duk sai da suka fito daga dakunansu jin yadda falon gaba daya yake amsa muryar Aliyu. har be janye yatsansa daga nuna Muhseen da yake ba sai rawa yatsan yake kamar zai da ki Muhseen da hannunsa.Wani irin abu yake ji yana masa yawo cikin jini wanda be taba jin irinsa ba, duk wani kishin Ataa da yake a can baya na yanzu ya ninka shi ninkin ba ninkin, ya yaba kyauta ya janyo gashinta kanta ya rika yatsanta, tunawa da irin kallon da yai mata da kalamansa na jiya sai ya ji kamar an yanga tsagen jikinsa an zubar a kasa, har lokacin Muhseen be iya cewa komai ba banda kallon kallon da suke da juna shi da Aliyu.
“Wai miye haka ne? Shikenan idan kuma abuja hankalin Fulani ya tashi idan kuma kuna nan nawa ya tashi? Wannan wace irin rayuwarce?”
Aliyu ya juyo ya kalli Momy.
“Ki fada masa ya daina shiga gonata”
“In daina shiga gonarka ko ka daina shiga gonata? What kind of nonsense is this, idan ina yaba kyau Ataa ko magana da ita ko taba ta miye matsalar ka da wannan?”
“Babu har sai ka sake”
Aliyu ya fada yana daga masa gira sannan ya fice daga falon zuwa bq.
“It's because tana gidanku?”
Muhseen ya fada a fusace yana bin Aliyu da kallon haushi.
“Muhseen nan mu ba gidansu ba ne, gidanku ne”
“To idan ba shi ba Momy miye ruwansa da ni? Naga dai ba shi da alaka da ita kamar yadda ni ma ba ni da, kuma son Ataa na ke son ta na ke be isa ya hana hakan ba... ”
Amina ta kalli Momy Momy ma ta kalli Amina kamin ita Aminar ta juya ta koma cikin dakinta.
“Na rasa gane kan Aliyu”
Muhseen ya sake fada.
“Ka yi hakuri Muhseen zan masa magana, ka yi hakuri dan Allah”
Maganar da Momy ta masa ce ta saka ya zauna saman kujera yana ta huci da mamakin yadda Aliyu yake son masa fin karfi.
ALIYU POV.
Tafiya yake yana kamar ba kasa yake takawa ba shi kan shi be taba jin kanshi a cikin irim wannan yanayin ba kamar yau. Ji yake kamar ba zai jure wani ya kara yabon kyau Ataa ba, ko da mace ce balle namiji. Yana shiga bq din Ataa ta daka tsalle tana ihu ta yi bayan Nana da ke zaune ta boye gabanta sai faduwa yake ta yi zaton ko dukanta Aliyu ya zo ya yi, duk da bata tsoronsa a yanzu amman tana tsoron yanayin da ta ganshi a yanzu. Yayi kokarin sauke fushinsa ya dan saki fuska sannan ya taka balcony din yana isa bakin kofar dakin da Nana take ciki ya tsaya ya cire takalminsa sannan ya shiga, risinawa yai har kasa kamar jiya ya gaishe ta ya mata ya jiki ta amsa masa fuska a sake Ataa na bayan Nana zaune tana dan lekoshi ta kawar da kai.
“Dan Allah Mama kar a sake bari Ataa ta fita tsakar gidan nan babu mayafi a jikin, kin ga akwai aljannu masu shiga jikin mutum gidan be rufe jiki ba, ko ka rufe ma ya aka kwashe balle kuma ba a rufe din ba? Yana da ta rika rufe jikinta da gashin kanta”
“In-Sha-Allah zai rega sakawa, muna goziya jiya kaya sun zo masu kyau Allah ya biya”
“Amin”
Yana amsawa da amin ya mike tsaye yana watsawa Ataa wata uwar harara domin mugun haushinta yake ji kamar ita tace Muhseen din ya kama hannunta ya rike, ita kuma ta murguda masa baki ta buya bayan Nana.ATAA POV.
Yana fita na fito daga bayan Nana na zauna daidai ina turo karamin bakina.
“Wai shi baya son ya ga wani na min far'ah ko muna wasa ko magana, ya fi son ya gan ni cikin bacin rai, idan yaga wani ya sakar min fuska ji yake kamar an masa ruwan mutuwa a zuciya”
Da yaren buzanci na fada cikin mugun jin haushinsa. Dariya Nana ta yi tana kallona ta ce.
“Tunda ba ya so ai sai ki daina, namiji baya jindadi idan yana ra'ayin mace yaga wani namijin na kula ta”
“Wacan zai ra'ayina? Wallahi duk ya bi ya tsane ni ban san abu da nai masa ba, bayan ma ni na fi dacewa na natseshi”
“Ki tsane shi aka ce mi? Ai baki da wata hujja ta tsanarsa, domin ya gama mana komai a duniyar nan”
“Haushi na yake ji kila ma dan yaga na fi shi kyau ne, sai wani ji da kan banza, kuma sai na kula Muhseen din haka kawai sai na yi ta shiga kunci ina bakin rai kamar shi, haka jiya ya kori mai koya min karatun nan da ya zo, wai ya cika far'a ya fi son ya ga ina ta bakinciki, shi fa dariya ta bakinciki take saka shi mtchhhhhhh”
Na karasa ina jan tsake har ga Allah yau kan Aliyu ya ba ni haushi, ban san abunda na tsare masa ba yake bakincikin ganin dariyata, wani lokacin ma sai yai ta abu kamar ba shi ba, dazun da naje tambayarsa ai dariya yai min, jiya yai min siyayya har ina jindadi amman yau ya canja kamar ba shi ba.
Murmushi kawai Nana take tana kallona kamin ta koma murza yatsun hannunta.
“Yanayin yaron nan yana tuna min da mahaifinki, haka yake kishi a lokacin da yake so na, ni kuma ina kishinsa saboda kyausa, idan yayan manyan sarakai suka zo nema na ranar ba zai yi bachi ba, saboda yana jin kamar zai rasa ni”
Ta fada da yaren buzanci hawaye na sauko mata, sai na kara matsawa kusa da ita na kwantar da kaina jikinta, sai ta shafa kan nawa hawayenta na sauka a kumatuna.
“Mutuwa ba tai kyau ba”
Ta fada da hausa tana son fashewa da kuka. Nima hawayen na soma yi tunawa da Baba na na san da yana raye duk wannan rayuwar ba mu shige ta ba, balle har Aliyu ya nemi takura domin Babana yana so na sosai. Ganin ina hawaye yasa tai saurin share nata kukan tana dariya kamar ba ita ba.
“Yana can cikin rahamar Allah In-Sha-Allah”
“Eh Nana yana cikin Rahama Allah ya jikanshi”
“Amin”Sanye da uniform Siyama ta kawo mana abun karyawar mu bayan ta gaisa da Nana ta fito daga bangaren mu ni kuma na biyota ina tambayarta ko nima zan iya zuwa makarantar.
“A a yau ba a zuwa sai da yamma, ai ita Islamiya sai assabar da lahadi kawai ake zuwa da safe”
“Na sani, amman na ga wata islamiyar idan mutum baya zuwa makarantar boko sai ya tafi islamiyar safe”
“Wannan ba a zuwa”
“Sai kin dawo Allah ya tsare”
Na fada ina kallonta gwanin sha'awa, sannan na juyo na dawo bq din na soma cire uniform din ina tunanin maganar Nana ta dazun wai idan yayan manyan sarakuna suka zo sai yai ta kishi, lallai Nana ta yi farin jini tunda har da yayan sarakuna sukai nemanta.
MUHSEEN POV.
Yana zaune a falon har Aliyu ya fito daga bq ya shiga motarsa ya dauki hanyar gida. Tunani yake ta yi yadda Aliyu ya zo rana tsaka yake son hana shi kula Ataa, idan ma wai wani sonta yake to shi mai gaba daya zai yi idan take takensa kenan shi zai fito kai tsaye ya aureta ya ga yadda zai yi. Har Momy ta gama hada breakfast din ta zubawa Siyama ta kuma zuba na su Nana ta bawa Siyama ta kai musu Muhseen na zaune a gurin be huce ba, a dinning ta jera sauran ta fada masa ya tashi ya karya sannan ta wuce bangare Daddy dan kai masa na shi su karya tare. Bayan ta gama da Daddy ta sallame shi ya wuce gurin aikinsa ta dawo part dinta sai ta samu Muhseen zaune a dinning shi kai yana cin plantain a hankali kana ganinsa kasan hankalinsa baya jikinsa, shi kai ne a dinning din hakan na nufi Amina da Husna sun gama karya sun tafi shi kuma ko rabi be yi ba. Sai da Momy ta kai kulolin data dauko part din Daddy kitchen sannan ta dawo dinning din ta ja kujerar da ke fuskantar ta Muhseen ta zauna.
“Ba ka ci abincin ba?”
Ataa ta fada tana murmushi.
“Zo na nuna miki kanki a wayana”
Ya zauna a kujerar da ke kusa da shi yana ciro wayar daga aljihunsa na gaba, bata zauna din ba ta juyo ta kalli Aliyu wanda idonsa ke kan wayarsa tunawa da yace ta daina sakewa Muhseen.
“a a bari na je na duba a Mota”
Ya fada sannan ta fara takawa zata wuce Muhseen ya bi bayanta da kallo komai na jikinta motsi yake a cikin uniform din kasancewarta mai tubultubul kuma uniform din ya dan kama jikinta din jiki ga shi bata da komai a ciki, da gangan yai hanzarin kai hannunsa ya kama gashin kanta ya juyo da ita ta rika yatsun hannunta.
“Pretty ina zoben da na baki...?”
Bata amsa shi ba tai saurin fisge hannunta tana kallon Aliyu hankalinta a tashe kamar wacce za ayi ma wani abu.
“Muhseen....!”
Aliyu ya daka masa tsawa a cikin muryar da shi kan shi be san da zamanta ba.
“Karka sake kuskuren yabon kyau Ataa balle ka ce zaka kai dan iskan hannunta ka taba ta, wannan ya zama na karshe ina nufi na karshe....”
Magana Aliyu yake ma Muhseen cikin tsawa yana nuna Muhseen da yatsansa kwayar idonsa gaba daya ta canja ta rine kamar ba shi ne da farin ido ba, shi kan shi Muhseen sai da gabashi ya fadi domin ya razana sosai da yanayin da ya ga Aliyu. Kamar kyalftawar walkiya haka Ataa ta bace bat a cikin falon kamin ta isa Bq har da gudunta, ganin irin tsawar da yai ma Muhseen da yake kanensa kuma dan'uwansa to ita kan ta san nata dukanta zai yi. Da sauri Momy ta fito daga kitchen tana kallonsu, kannensa ma Amina, Siyama da Husna duk sai da suka fito daga dakunansu jin yadda falon gaba daya yake amsa muryar Aliyu. har be janye yatsansa daga nuna Muhseen da yake ba sai rawa yatsan yake kamar zai da ki Muhseen da hannunsa.Wani irin abu yake ji yana masa yawo cikin jini wanda be taba jin irinsa ba, duk wani kishin Ataa da yake a can baya na yanzu ya ninka shi ninkin ba ninkin, ya yaba kyauta ya janyo gashinta kanta ya rika yatsanta, tunawa da irin kallon da yai mata da kalamansa na jiya sai ya ji kamar an yanga tsagen jikinsa an zubar a kasa, har lokacin Muhseen be iya cewa komai ba banda kallon kallon da suke da juna shi da Aliyu.
“Wai miye haka ne? Shikenan idan kuma abuja hankalin Fulani ya tashi idan kuma kuna nan nawa ya tashi? Wannan wace irin rayuwarce?”
Aliyu ya juyo ya kalli Momy.
“Ki fada masa ya daina shiga gonata”
“In daina shiga gonarka ko ka daina shiga gonata? What kind of nonsense is this, idan ina yaba kyau Ataa ko magana da ita ko taba ta miye matsalar ka da wannan?”
“Babu har sai ka sake”
Aliyu ya fada yana daga masa gira sannan ya fice daga falon zuwa bq.
“It's because tana gidanku?”
Muhseen ya fada a fusace yana bin Aliyu da kallon haushi.
“Muhseen nan mu ba gidansu ba ne, gidanku ne”
“To idan ba shi ba Momy miye ruwansa da ni? Naga dai ba shi da alaka da ita kamar yadda ni ma ba ni da, kuma son Ataa na ke son ta na ke be isa ya hana hakan ba... ”
Amina ta kalli Momy Momy ma ta kalli Amina kamin ita Aminar ta juya ta koma cikin dakinta.
“Na rasa gane kan Aliyu”
Muhseen ya sake fada.
“Ka yi hakuri Muhseen zan masa magana, ka yi hakuri dan Allah”
Maganar da Momy ta masa ce ta saka ya zauna saman kujera yana ta huci da mamakin yadda Aliyu yake son masa fin karfi.
ALIYU POV.
Tafiya yake yana kamar ba kasa yake takawa ba shi kan shi be taba jin kanshi a cikin irim wannan yanayin ba kamar yau. Ji yake kamar ba zai jure wani ya kara yabon kyau Ataa ba, ko da mace ce balle namiji. Yana shiga bq din Ataa ta daka tsalle tana ihu ta yi bayan Nana da ke zaune ta boye gabanta sai faduwa yake ta yi zaton ko dukanta Aliyu ya zo ya yi, duk da bata tsoronsa a yanzu amman tana tsoron yanayin da ta ganshi a yanzu. Yayi kokarin sauke fushinsa ya dan saki fuska sannan ya taka balcony din yana isa bakin kofar dakin da Nana take ciki ya tsaya ya cire takalminsa sannan ya shiga, risinawa yai har kasa kamar jiya ya gaishe ta ya mata ya jiki ta amsa masa fuska a sake Ataa na bayan Nana zaune tana dan lekoshi ta kawar da kai.
“Dan Allah Mama kar a sake bari Ataa ta fita tsakar gidan nan babu mayafi a jikin, kin ga akwai aljannu masu shiga jikin mutum gidan be rufe jiki ba, ko ka rufe ma ya aka kwashe balle kuma ba a rufe din ba? Yana da ta rika rufe jikinta da gashin kanta”
“In-Sha-Allah zai rega sakawa, muna goziya jiya kaya sun zo masu kyau Allah ya biya”
“Amin”
Yana amsawa da amin ya mike tsaye yana watsawa Ataa wata uwar harara domin mugun haushinta yake ji kamar ita tace Muhseen din ya kama hannunta ya rike, ita kuma ta murguda masa baki ta buya bayan Nana.ATAA POV.
Yana fita na fito daga bayan Nana na zauna daidai ina turo karamin bakina.
“Wai shi baya son ya ga wani na min far'ah ko muna wasa ko magana, ya fi son ya gan ni cikin bacin rai, idan yaga wani ya sakar min fuska ji yake kamar an masa ruwan mutuwa a zuciya”
Da yaren buzanci na fada cikin mugun jin haushinsa. Dariya Nana ta yi tana kallona ta ce.
“Tunda ba ya so ai sai ki daina, namiji baya jindadi idan yana ra'ayin mace yaga wani namijin na kula ta”
“Wacan zai ra'ayina? Wallahi duk ya bi ya tsane ni ban san abu da nai masa ba, bayan ma ni na fi dacewa na natseshi”
“Ki tsane shi aka ce mi? Ai baki da wata hujja ta tsanarsa, domin ya gama mana komai a duniyar nan”
“Haushi na yake ji kila ma dan yaga na fi shi kyau ne, sai wani ji da kan banza, kuma sai na kula Muhseen din haka kawai sai na yi ta shiga kunci ina bakin rai kamar shi, haka jiya ya kori mai koya min karatun nan da ya zo, wai ya cika far'a ya fi son ya ga ina ta bakinciki, shi fa dariya ta bakinciki take saka shi mtchhhhhhh”
Na karasa ina jan tsake har ga Allah yau kan Aliyu ya ba ni haushi, ban san abunda na tsare masa ba yake bakincikin ganin dariyata, wani lokacin ma sai yai ta abu kamar ba shi ba, dazun da naje tambayarsa ai dariya yai min, jiya yai min siyayya har ina jindadi amman yau ya canja kamar ba shi ba.
Murmushi kawai Nana take tana kallona kamin ta koma murza yatsun hannunta.
“Yanayin yaron nan yana tuna min da mahaifinki, haka yake kishi a lokacin da yake so na, ni kuma ina kishinsa saboda kyausa, idan yayan manyan sarakai suka zo nema na ranar ba zai yi bachi ba, saboda yana jin kamar zai rasa ni”
Ta fada da yaren buzanci hawaye na sauko mata, sai na kara matsawa kusa da ita na kwantar da kaina jikinta, sai ta shafa kan nawa hawayenta na sauka a kumatuna.
“Mutuwa ba tai kyau ba”
Ta fada da hausa tana son fashewa da kuka. Nima hawayen na soma yi tunawa da Baba na na san da yana raye duk wannan rayuwar ba mu shige ta ba, balle har Aliyu ya nemi takura domin Babana yana so na sosai. Ganin ina hawaye yasa tai saurin share nata kukan tana dariya kamar ba ita ba.
“Yana can cikin rahamar Allah In-Sha-Allah”
“Eh Nana yana cikin Rahama Allah ya jikanshi”
“Amin”Sanye da uniform Siyama ta kawo mana abun karyawar mu bayan ta gaisa da Nana ta fito daga bangaren mu ni kuma na biyota ina tambayarta ko nima zan iya zuwa makarantar.
“A a yau ba a zuwa sai da yamma, ai ita Islamiya sai assabar da lahadi kawai ake zuwa da safe”
“Na sani, amman na ga wata islamiyar idan mutum baya zuwa makarantar boko sai ya tafi islamiyar safe”
“Wannan ba a zuwa”
“Sai kin dawo Allah ya tsare”
Na fada ina kallonta gwanin sha'awa, sannan na juyo na dawo bq din na soma cire uniform din ina tunanin maganar Nana ta dazun wai idan yayan manyan sarakuna suka zo sai yai ta kishi, lallai Nana ta yi farin jini tunda har da yayan sarakuna sukai nemanta.
MUHSEEN POV.
Yana zaune a falon har Aliyu ya fito daga bq ya shiga motarsa ya dauki hanyar gida. Tunani yake ta yi yadda Aliyu ya zo rana tsaka yake son hana shi kula Ataa, idan ma wai wani sonta yake to shi mai gaba daya zai yi idan take takensa kenan shi zai fito kai tsaye ya aureta ya ga yadda zai yi. Har Momy ta gama hada breakfast din ta zubawa Siyama ta kuma zuba na su Nana ta bawa Siyama ta kai musu Muhseen na zaune a gurin be huce ba, a dinning ta jera sauran ta fada masa ya tashi ya karya sannan ta wuce bangare Daddy dan kai masa na shi su karya tare. Bayan ta gama da Daddy ta sallame shi ya wuce gurin aikinsa ta dawo part dinta sai ta samu Muhseen zaune a dinning shi kai yana cin plantain a hankali kana ganinsa kasan hankalinsa baya jikinsa, shi kai ne a dinning din hakan na nufi Amina da Husna sun gama karya sun tafi shi kuma ko rabi be yi ba. Sai da Momy ta kai kulolin data dauko part din Daddy kitchen sannan ta dawo dinning din ta ja kujerar da ke fuskantar ta Muhseen ta zauna.
“Ba ka ci abincin ba?”