Sashe 102
Zaki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tun daga lokacin ya fara shirye shirye kamar yadda Momy ta fada masa, kudi ya cire mai yawa ya bawa wata yayar Momy yar kasuwa ta siyoma Ataa expensive clothes da tsarkoki masu kyau da tsada shoe dinta ma abun kallo ne, kusan kala talatin aka mata nata na sakawa wai na yanzu da kuma na kwaliyar amarci kamin a dinka mata na lefe idan komai ya laba hankali ya kwanta zai mata cikakken lefe domin yana son ya mayarda ita mutum ita ta zama tana fita da shiga irin ta yayan manya.
Bayan gidan da suka zauna d Rahma yana da wani gidan dabam mai kyau da tsare, wanda ya so ya aje Ataa a ciki ita kuma Rahma ya barta a wacan ma'ana ya raba musu gida saboda gudun fitina sai Momy ta hana ta saka Daddyn ya ba shi dayan gidansa mai part uku da ke unguwar koko road.
Sabon fenti aka yi ma gidan duk kuwa da kasancewar ba a taba shigarsa ba, saka kara kawata shi aka gyara wasu abubuwan, sannan Momy tai order wasu furnitures daga Kaduna masu tsada da kyau aka kawo aka zuba a dayan bangaren na Ataa gaba daya furnitures din bangrenta fafare ne tun daga dago har kujeru da duk wani abu na kwaliyar daki, gurin curtains din ne kawai akai musu surki da ja da sai kuma carpet din shi ma ja, after two days da kawo furnitures aka saka Electronics da wasu abubuwan na kawata gida.
Kayan kitchen kuma wata mai siyarda da kayan kitchen aka bawa kwangila da shirya komai on Friday aka saka. Ba Aliyu kadai ba, Momy m da yan'uwanta da Daddy da Abbah sun yi ma Ataa hidima sosai gurin gyara komai na gida. Sai dai duk wannan farinciki da jindadadi Ataa zata tare da Aliyu yake idan ya tuna cewar Babu Mama Fulani za ayi sai ya ji babu dadi, gashi tun lokacin da abun ya faru ta daina daukar wayarsa balle kuma ita ta kirashi da kanta Momy ma idan ta kira bata dagawa, sai dai ya kira Maryam ko. Rukaiyah ya tambayi lafiyarta.
Kamar yadda Momy ta tsara ranar Saturday akai walima, ba a yi wani taro ba domin ba kowa da kowa Momy ta gayyato ba, saboda kurewar lokaci wasu ma jin abun na Momy ne yasa suka zo ba tare da an gayyoto su din ba, wani abun mamaki har da Maryam da Rukaiya da kuma yayan Ammy, wanda Momy take sa ka ran Abbah ne ya turo su da kansa, domin Mama Fulani dai fushi take ba zata taba cewa su zo ba, ko da yake wani lokacin Mama Fulani ta kan yi wani abun dan hada kan zuri'ar ta da kuma yayanta.
Sosai Momy tai farinciki da ganinsu kuma ta jidadin zuwan na su.
ATAA. POV.
Ban kara tabbatar da cewar da gaske ne ba, sai da maga ana ta hidimar bikin, tun ranar laraba aka saka nai wa ka da ruwan lalle mai ja sosai, ranar da ta kama jumma aka zo aka kara gyara min gashina har gida, ba kitso aka min ba sai dai an gyara min shi yadda na ke jindadin zamansa a kaina. Lallen ma dan ubansu aka min mai kyau gaske, tun da nake a rayuwata ban taba yin lallae ba sai yau ashe haka yake kyau a fatata farin kafata dana hannuna ya fito fes lallen mai ja ya fito fes, domin ja ne kawai aka min da shi babu digon baki ko daya.
Ranar assabar na tashi da wani azababben ciwon kai saboda na wuni na kuma kwana ina kuka da tunanin. Da yamma aka sake saka ni nai wani wankan wata mai kwaliyar ta zo ta shirya ni tai min fentin nan na kanti sai na fito kamar ba ni ba, dogon hancin nan nawa sai ya kara fitowa kowa cewar yake na yi kyau ni dai nawa idone kawai zuciyata kuma cike da kuka. A mota mai kyau aka saka ni aka tafi da ni gidan Momy a can na tararda taro har an fara walimar ma, a cikin mutanen da suka halarta da su Yayan Mama Fulani da Ammy Maryam da Rukaiya har bana son hada ido da su saboda harata da suke. Duk wani wa'axi na Malamar ban ji ko daya ba, I hawaye kawai nake har kwaliyar tawa ta hoda ta soma gogewa, na sha hotuna sosai. Kamin Momy ta saka a sake maida ni gudin Kanwar tata Hajiya Mairo sai dai wannan karon tare da duka yayanta muka tafi da kuma wasu bakin fuska da ban sani ba. Ta ba ni abinci amman na kasa ci ruwa ma kasa sha nai sai gani nake kamar mafarki na ke. Bayan na gama sallah isha'i wata mai kwaliyar ba wacan ba ta sake zuwa ta gyara ni na saka wasu tufafin lace ne ash color mai kyau da ja mayafi sai kuma ta kalmin suma kala daya da gyalena sarkar kuma irin wannan ce mai ruwan gol wata kila ma gol din ne ban gane ba. A gidan Momy aka sake dawowa da ni tare da yan matan dake tare da ni aka kai ni gurin Nana wai ta min huduba sai aka fita aka bar ni daga ni sai ita, riketa nai na fashe da kuka ji nake kamar idan na tafi na tafi kenan ba dawowa. Ita bata iya ce min komai sai kuka take har wata yar'uwar Daddy ta shigo zata fita da ni sai na rike Nana gam ina kuka kamar yadda ita ma take yi tana rike da hannuna.
“Aure ai ya gaji haka, dan Allah ku yi hakuri sai kace wandanda akai wa mutuwa? Haba dai”
Shine abunda mutane suke ta fada ganin irin yadda ni da Nana muke ta kuka sosai, babu wanda ya san abunda na ke ji sai ni yau zan rabu da Nana wai wani aure zan yi auren da sai a yanzu na ke jin nadamar amincewa da Aliyu da nai da na sani na ce ban shirya auren kowa ba sai na zauna ni na Nana mu yi ta rayuwarmu. Batan fitowa da ni bangaren Nana aka kai ni Gurin Momy dakin na cike da mutane a haka tai min nasiha sai na rike hannunta ina ta girgiza mata kai ina kuka ita ma kanta sai dai ta yi hawayen.
Daker aka fito da ni aka saka ni a motar ina da kallon bq din Nana na tsaye jikin windows tana kallona ita da wasu yan'uwana Momy wata kila hakuri suke ba ta, a gidan baya aka sani ni tare da wasu mayan mata sauran yan matan kuma suka shiga sauran motocin, aka dauki hanya da ki hanyar da ban san wace unguwa ce ba domin kaina a kasa yake ina kuka har mutanen da ke cikin moyar suka soma tsarguwa da ni. Mun dade muna tafiyar sannan muna iso wani gida da ban san ina ne ba jin ana guda yasa gabana faduwa kuma na kara rushewa da kuka.
Wata matar ce da ba zan iya shaidar fuskarta ba ke rike da hannuna tana nutsawa da ni a cikin gidan har muka isa falon da ke ta kamshin turare sannan muka wuce uwar daga ma'ana bedroom nan dai kamshi ke tashi da kuma mutane a ciki da ba xa su fi mutum biyar ba bayan falon da ma da akwai wasu a nan. A tsakiyar gadon aka zauna da ni sannan aka fesa min wani turaren aka kara gyara min mayafina yadda zai sauko min da kyau. Sai da dattijawan cikin suka min addu'a kuma suka min huduba akan zaman aure hakuri yi na yi ba ri na ba ri da kuma toshe kunnu akan dukan abunda zan ji ko na gani.
Sannan suka tafi aka barni da yan mata masu kokarin bude mayafina su ga fuskata ni ko har lokacin hawaye na ke, ina jin wani yanayi da ban taba jin kaina a ciki ba, hakika ban san aure ba, ban san miye aure ba balle abubuwan da suke cikinsa, amman iina jin darajata ta karu na bar kulawar Nana da tarbiyarta na koma gurin ta Aliyu kamar yadda Momy tai min huduba. Wata sabuwar rayuwarce zan fara fuskanta wata kila mai dadi ce ko akasin haka, wata kila mai sauki ce ko kishiyarta, wata kila kuma na samu duka biyun wato dadi da daci sauki da kuma wahala.
Bana iya gane lokacin da aka shigo da Aliyu hayaniyar maza kawai na ji a dakin wasu na zolarsa, ban daga kaina a cikin mayafin na kalle ko su waye da waye a abokansa ba, amman nasan sun hausa mutum biyar kuma ba za su sama da mutu goma ba, baki gado ya zauna yana ga kamshin turarensa mai dadin shaka. Nasir ne ya fara yi mana nasiha sannan wani abokinsa ya dora sai kuma suka rufe da addu'a tare dayi mana fatar samun zaman lafiya kwanciyar hankali da kuma zuri'a ta gari. Da dai daya suka fara fita sannan sauran suka fice har da matan sai ya tashi ya raka abokansa, ina jin lokacin da motacinsu suka tashi suka bar cikin gidan sai kuma na ji yana jan kofar falon alamar rufewa yake.
Da zai dawo dakin sai da yai sallama sannan ya shigo, ni kuma na kasa amsawa har lokacin kaina na kasa ina ta wasa da yatsun hannuna, a inda ya zauna dazu ya sake zaunawa.
“Amarya.... ”
Sai na ji wata kunyar ta sake rufe. Kara hawowa yai saman gadon ya miko hannunsa ya bude mayafin da ke kaina ya dora shi a bayana yana murmushi sai kuma ya saka hannun na sa ya dago kaina sai na lumshe ido.
“Godiya ga Ubangijin da ya mallaka min wannan halittar ta inda ban yi zato ba, tsarki ya tabbata a gareka ya Allah”
Ya fada sannan ya Hura min iska a saman idona da suke kulle.
“Bude idonki ki kalli Masoyinki, bude idonki ki kalli mijinki na har abada”
Bayan gidan da suka zauna d Rahma yana da wani gidan dabam mai kyau da tsare, wanda ya so ya aje Ataa a ciki ita kuma Rahma ya barta a wacan ma'ana ya raba musu gida saboda gudun fitina sai Momy ta hana ta saka Daddyn ya ba shi dayan gidansa mai part uku da ke unguwar koko road.
Sabon fenti aka yi ma gidan duk kuwa da kasancewar ba a taba shigarsa ba, saka kara kawata shi aka gyara wasu abubuwan, sannan Momy tai order wasu furnitures daga Kaduna masu tsada da kyau aka kawo aka zuba a dayan bangaren na Ataa gaba daya furnitures din bangrenta fafare ne tun daga dago har kujeru da duk wani abu na kwaliyar daki, gurin curtains din ne kawai akai musu surki da ja da sai kuma carpet din shi ma ja, after two days da kawo furnitures aka saka Electronics da wasu abubuwan na kawata gida.
Kayan kitchen kuma wata mai siyarda da kayan kitchen aka bawa kwangila da shirya komai on Friday aka saka. Ba Aliyu kadai ba, Momy m da yan'uwanta da Daddy da Abbah sun yi ma Ataa hidima sosai gurin gyara komai na gida. Sai dai duk wannan farinciki da jindadadi Ataa zata tare da Aliyu yake idan ya tuna cewar Babu Mama Fulani za ayi sai ya ji babu dadi, gashi tun lokacin da abun ya faru ta daina daukar wayarsa balle kuma ita ta kirashi da kanta Momy ma idan ta kira bata dagawa, sai dai ya kira Maryam ko. Rukaiyah ya tambayi lafiyarta.
Kamar yadda Momy ta tsara ranar Saturday akai walima, ba a yi wani taro ba domin ba kowa da kowa Momy ta gayyato ba, saboda kurewar lokaci wasu ma jin abun na Momy ne yasa suka zo ba tare da an gayyoto su din ba, wani abun mamaki har da Maryam da Rukaiya da kuma yayan Ammy, wanda Momy take sa ka ran Abbah ne ya turo su da kansa, domin Mama Fulani dai fushi take ba zata taba cewa su zo ba, ko da yake wani lokacin Mama Fulani ta kan yi wani abun dan hada kan zuri'ar ta da kuma yayanta.
Sosai Momy tai farinciki da ganinsu kuma ta jidadin zuwan na su.
ATAA. POV.
Ban kara tabbatar da cewar da gaske ne ba, sai da maga ana ta hidimar bikin, tun ranar laraba aka saka nai wa ka da ruwan lalle mai ja sosai, ranar da ta kama jumma aka zo aka kara gyara min gashina har gida, ba kitso aka min ba sai dai an gyara min shi yadda na ke jindadin zamansa a kaina. Lallen ma dan ubansu aka min mai kyau gaske, tun da nake a rayuwata ban taba yin lallae ba sai yau ashe haka yake kyau a fatata farin kafata dana hannuna ya fito fes lallen mai ja ya fito fes, domin ja ne kawai aka min da shi babu digon baki ko daya.
Ranar assabar na tashi da wani azababben ciwon kai saboda na wuni na kuma kwana ina kuka da tunanin. Da yamma aka sake saka ni nai wani wankan wata mai kwaliyar ta zo ta shirya ni tai min fentin nan na kanti sai na fito kamar ba ni ba, dogon hancin nan nawa sai ya kara fitowa kowa cewar yake na yi kyau ni dai nawa idone kawai zuciyata kuma cike da kuka. A mota mai kyau aka saka ni aka tafi da ni gidan Momy a can na tararda taro har an fara walimar ma, a cikin mutanen da suka halarta da su Yayan Mama Fulani da Ammy Maryam da Rukaiya har bana son hada ido da su saboda harata da suke. Duk wani wa'axi na Malamar ban ji ko daya ba, I hawaye kawai nake har kwaliyar tawa ta hoda ta soma gogewa, na sha hotuna sosai. Kamin Momy ta saka a sake maida ni gudin Kanwar tata Hajiya Mairo sai dai wannan karon tare da duka yayanta muka tafi da kuma wasu bakin fuska da ban sani ba. Ta ba ni abinci amman na kasa ci ruwa ma kasa sha nai sai gani nake kamar mafarki na ke. Bayan na gama sallah isha'i wata mai kwaliyar ba wacan ba ta sake zuwa ta gyara ni na saka wasu tufafin lace ne ash color mai kyau da ja mayafi sai kuma ta kalmin suma kala daya da gyalena sarkar kuma irin wannan ce mai ruwan gol wata kila ma gol din ne ban gane ba. A gidan Momy aka sake dawowa da ni tare da yan matan dake tare da ni aka kai ni gurin Nana wai ta min huduba sai aka fita aka bar ni daga ni sai ita, riketa nai na fashe da kuka ji nake kamar idan na tafi na tafi kenan ba dawowa. Ita bata iya ce min komai sai kuka take har wata yar'uwar Daddy ta shigo zata fita da ni sai na rike Nana gam ina kuka kamar yadda ita ma take yi tana rike da hannuna.
“Aure ai ya gaji haka, dan Allah ku yi hakuri sai kace wandanda akai wa mutuwa? Haba dai”
Shine abunda mutane suke ta fada ganin irin yadda ni da Nana muke ta kuka sosai, babu wanda ya san abunda na ke ji sai ni yau zan rabu da Nana wai wani aure zan yi auren da sai a yanzu na ke jin nadamar amincewa da Aliyu da nai da na sani na ce ban shirya auren kowa ba sai na zauna ni na Nana mu yi ta rayuwarmu. Batan fitowa da ni bangaren Nana aka kai ni Gurin Momy dakin na cike da mutane a haka tai min nasiha sai na rike hannunta ina ta girgiza mata kai ina kuka ita ma kanta sai dai ta yi hawayen.
Daker aka fito da ni aka saka ni a motar ina da kallon bq din Nana na tsaye jikin windows tana kallona ita da wasu yan'uwana Momy wata kila hakuri suke ba ta, a gidan baya aka sani ni tare da wasu mayan mata sauran yan matan kuma suka shiga sauran motocin, aka dauki hanya da ki hanyar da ban san wace unguwa ce ba domin kaina a kasa yake ina kuka har mutanen da ke cikin moyar suka soma tsarguwa da ni. Mun dade muna tafiyar sannan muna iso wani gida da ban san ina ne ba jin ana guda yasa gabana faduwa kuma na kara rushewa da kuka.
Wata matar ce da ba zan iya shaidar fuskarta ba ke rike da hannuna tana nutsawa da ni a cikin gidan har muka isa falon da ke ta kamshin turare sannan muka wuce uwar daga ma'ana bedroom nan dai kamshi ke tashi da kuma mutane a ciki da ba xa su fi mutum biyar ba bayan falon da ma da akwai wasu a nan. A tsakiyar gadon aka zauna da ni sannan aka fesa min wani turaren aka kara gyara min mayafina yadda zai sauko min da kyau. Sai da dattijawan cikin suka min addu'a kuma suka min huduba akan zaman aure hakuri yi na yi ba ri na ba ri da kuma toshe kunnu akan dukan abunda zan ji ko na gani.
Sannan suka tafi aka barni da yan mata masu kokarin bude mayafina su ga fuskata ni ko har lokacin hawaye na ke, ina jin wani yanayi da ban taba jin kaina a ciki ba, hakika ban san aure ba, ban san miye aure ba balle abubuwan da suke cikinsa, amman iina jin darajata ta karu na bar kulawar Nana da tarbiyarta na koma gurin ta Aliyu kamar yadda Momy tai min huduba. Wata sabuwar rayuwarce zan fara fuskanta wata kila mai dadi ce ko akasin haka, wata kila mai sauki ce ko kishiyarta, wata kila kuma na samu duka biyun wato dadi da daci sauki da kuma wahala.
Bana iya gane lokacin da aka shigo da Aliyu hayaniyar maza kawai na ji a dakin wasu na zolarsa, ban daga kaina a cikin mayafin na kalle ko su waye da waye a abokansa ba, amman nasan sun hausa mutum biyar kuma ba za su sama da mutu goma ba, baki gado ya zauna yana ga kamshin turarensa mai dadin shaka. Nasir ne ya fara yi mana nasiha sannan wani abokinsa ya dora sai kuma suka rufe da addu'a tare dayi mana fatar samun zaman lafiya kwanciyar hankali da kuma zuri'a ta gari. Da dai daya suka fara fita sannan sauran suka fice har da matan sai ya tashi ya raka abokansa, ina jin lokacin da motacinsu suka tashi suka bar cikin gidan sai kuma na ji yana jan kofar falon alamar rufewa yake.
Da zai dawo dakin sai da yai sallama sannan ya shigo, ni kuma na kasa amsawa har lokacin kaina na kasa ina ta wasa da yatsun hannuna, a inda ya zauna dazu ya sake zaunawa.
“Amarya.... ”
Sai na ji wata kunyar ta sake rufe. Kara hawowa yai saman gadon ya miko hannunsa ya bude mayafin da ke kaina ya dora shi a bayana yana murmushi sai kuma ya saka hannun na sa ya dago kaina sai na lumshe ido.
“Godiya ga Ubangijin da ya mallaka min wannan halittar ta inda ban yi zato ba, tsarki ya tabbata a gareka ya Allah”
Ya fada sannan ya Hura min iska a saman idona da suke kulle.
“Bude idonki ki kalli Masoyinki, bude idonki ki kalli mijinki na har abada”