Sashe 55
Zaki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Daker na iya daga kafata na shiga cikin dakin hawaye na sauko min wasu na bin wasu. Kusa da ita na je na zauna ina kiran sunanta.
“Nana Nana Nana”
Shiru bata amsa min ba, sai kallona take kamar bata gane ba. Hijab dina na cire na na aje Farida na tsaye tana kallona har na janyota domin bana iya daukarta gaba daya bakin kofar dakin na kawo ta na aje, na fito da komai na dakin na nemi tsohuwar tsintsiyar mu da naga a cikin kaya na share dakin, na dauki roba na shiga ciki na debo ruwa kasancewar cikin gidansu Farida a akwai rijiya, na dawo dakin na zuba ruwan na wanke na masa tas, duk abunda na ke Farida na tsaye tana kallona ta kasa komai, Hijab din nawa na saka na je gawon nama na siyo omo da kudin hannu na siyo fura da nono da madara na dawo, ko da na dawo Farida ta shige cikin gida, ni kuma na sake sakawa dakin omo na wanke shi ya cire duk wani karni da warin da yake sannan na dauko turaren da Kamal ya siya min na saka duk da kasancewar na jiki ba hakan be hana dakin kamshi ba, zane da zane na hada na zagaye sannan na sake debo wasu ruwan na kai na jata a haka na kaita gurin na zuba mata ruwa nai mata wanka ko ina na jikinta sai da na wanke sannan na sake dawowa da ita a cikin tufafi na dauki wata riga da Aliyu ya bani na saka lokacin da nai rashin lafiya ta manya na saka mata na daura mata dankwalin sai na aje ta a waje saboda dakin be gama budewa ba. Wasu ruwan na sake debowa na saka kayan ci abincin mu a gaba na wanke su ma sannan na dama mata furar na saka ludayi ina ta bata tana sha a hankali har ta sha ya iashe sai na debo mata ruwa na bata ta ta sha da yawa, sai ta sauke wani irin ajiyar zuciya yana saka ni jin tausayinta fiye da da, sannan na dauke ta na maida ta dakin na fito na saka tufafinta a gaba na wanke su na shanya sannan na daw dakin kusa da ita na zauna ina ta kallonta kamar yadda ita ma take kallona irin kallo da ke nuna bata gane ni ba, ko kuma bata san inda kanta yake ba kawai dai tana gani ne.
“Nana”
Bata amsa ni bata kuma daina kallona ba, hakan yasa na fashe da kuka na kama hannunta na rike, na dawo amman babu kudin maganin kuma n tararda ciwonta ya fi na da, sai dai ina tunanin dawowar tawa tai amfani domin gashi yanzu ina zaune gabanta ina kula da ita. Farida ce ta shigo dakin ta tsaya daga jikin kofa tana kallona.
“Bayan tafiyarki abun yai tsamari bata iya tashi komai a inda take take yinsa, na iya kokarina na kula da ita, daga baya Mama ta hanani, wacan kitchen din da ke cikin gida ya lalace shiyasa Baba ya buga mata kwano ya dawo da ita”
Hannu na saka na share hawayen idonta.
“Kin san ba zaki iya kula min davita yadda ya kamata ba, miyasa kika ce za ki yi? Miyasa kika bari na tafi? Aminta ba ta ce haka ba Farida yanzu da mahaifiyarki ce kina tunanin zan iya barinta a haka? Wallahi ba zan iya ba”
“Na yi iya kokarina Ataa Wallahi dawainiya da Ataa ba abu ne mai sauki ba”
“Eh na sani ai, ba abu ne mai sauki kula da Nana ba, ba abu ne mai sauki kula da uwar da ba taka ba, amman kin san ba dan dole ba babu yadda za ayi na tafi na barta, idan kika duba dalilin tafiyata kadai ya isa ya saka ki tausaya min ki tausaya mata ki kula da ita”
Ta yi shiru bata ce komai ba, ni kuma na mike tsaye na fito waje nai alwala nai sallah na cire Hijab din na aje na rafka uban tagumi ina kallonta, ta ina zan samu mafita? Duniyar nan ta juya min ko ina na raba ba dadi, duk inda na saka gaba da zimmar cimma burina sai wani abun ya shiga gabana ya tare, sai yanzu na gane kwata kwata bana da sa'ar rayuwa kuma bana da nasara a rayuwata sai dai hakan ba zai saka na kyale rayuwar Nana a haka ba, ko da ko raina zan ransa. Ta ina zan fara baran zan koma? Ko kuwa sata zan yi? Wani zai kaiwa koke na ko kuwa mutuncina zan siyar? Duka ban gan mafita a wannan ba. Da tunanin inda zan samu taimako na kwana na a raina.
ALIYU POV.
Bayan sun shiga cikin gidan ne Rahma na dakinta na wuce dakinsa yai wanka ya fita masallacin unguwar yai sallah la'asar sannan ya dawo cikin gidan ya shiga dakin Rahma, zaune ya same ta saman sallaya da alama ita ta gama sallah ne a yanzu. Kasa ya zauna kusa da ita yana kallon fuskarta dake dauke da damuwa, har ya bude baki yai mata magana sai wayarsa dake aljihu tai vibration alamar kira, ciro wayar yai ganin number Mama Fulani be tsaya bata lokaci ba ya daga.
“Aliyu kana ina?”
“Gida”
“Zo ina son magana da kai?”
“Lafiya dai?”
“Lafiya akan matsalar haihuwarka ne, Rahma ta fada mana gaskiya ai”
“Gaskiya kuma? Wani abun ne?”
Mama Fulani bata sake ce masa komai ba ta kashe wayar. Sai ya kalli Rahma
“Wani abun kika fada wa Mama?”
“Ban yi magana da Mama ba, amman na yi da Momy shi ma kuma ban san cewa ba su sani ba”
Wani kallo ha aika mata irin kallon nan na me kika fada musu.
“Na fada mata cewar matsalar haihuwar daga kai ne”
“For what?”
“Na dauka sun sani”
“Ko sun sani be kamata ki yi wannan maganar da su Rahma”
“Abun ne ya fara damuna yanzu, kuma a da suna ta ganin laifina amman yanzu za su fahimci ba daga ni ba ne wata kila za su daga min kafa”
“Amman idan matsalar daga ni ne be zama damuwarki ba? Kina kokarin chanjawa daga yadda na sanki Rahma”
“Ba canja nake ba Aliyu, damuwar ka damuwa ta ce, sai dai a yanzu matsalar nan ni ta fi shafuwa fiye da kai, a baki rame na ke zan iya mutuwa a ko da yaushe, ba tare da na bar abunda za a tuna da ni ba, amman kai kana nan raye har na tsawon lokaci”
Be sake ce mata komai ba ya mike tsaye yana saka wayar ajihunsa ya fice daga dakin. Cikin bacin rai ya isa gidan sam be jidadin abunda Rahma tai masa ba, domin be fadawa kowa ba kuma be za ci zata iya fadawa wasu ba, wasun ma kuma iyayensa. Ko da ya shiga falon Kanensa na ciki suna ta fira da dariya, be kula su ba ya haye sama zuwa dakin Mama Fulani sai ya samu Momy da Abbah a ciki suna fira shiga dakin da murmushinsa ya zauna saman kujerar da Abbah yake zaune yana gaisawa da shi.
“Abbah dawowan rana kai?”
“Eh Wallahi Hajiya Fulani ta fada min na ce bari na samu na zo mu gaisa da ita”
“Gaskiya kam ko mu da muke cikin gida muna wahalar ganawa da kai balle ba ko”
“To ya za ayi aikin ne a haka sai hakuri”
Mama Fulani ce ta shigo dakin ta tsaya jikin kofa tana kiran Aliyu.
“Aliyu magana nake son yin da kai fa”
Tashi Aliyu yai ya bi bayanta suka nufi dakin Baby a ciki suka zauna. Ta kalle irin duban bana wasa ba ta ce.
“Rahma ta ce matsalar daga gareka ne?”
“Matsalar me ba?”
Yayi kamar be fahimci abunda take magana akai ba.
“Ba mu da matsayin da zaka fada mana matsalar ka ne Aliyu? Ko kuma ka boye mana gaskiya ne saboda ka kare matar ka?”
“Ba ko daya, na san idan na fada muku za ku damu, ni kuma ba haka na ke so ba, kuma ko da matsalar daga ni ne idan Allah ya rubuta zan haihu zan haihu”
“Da gaske ne kenan?”
“Gaskiya ne Mama”
Mama Fulani ta rufe baki idonta cike da kwalla.
“Aliyu da gaske fa ka ce”
Na gyada mata kai.
“Gaskiya ne Mama, sun ce kwayoyin halittafa ba su da karfin da za su rayu a mahaifar Rahma”
“Kuma babu wani abun da za a iya yi? Babu wata mafita”
Ta tambaya cikinnmuryar kuka domin har ga Allah bata son abunda ya taba Aliyu, balle kuma haihuwa da take babbar abu.
“Mafita kawai addu'a kuma zan cigaba da neman magani ko Allah zai saka a dace”
Dafe kai tai cike da tausayinsa. Tashi Aliyu yai ya koma kusa da ita ya zauna.
“Mama ki daina damuwa ba komai”
“Akwai komai Aliyu, haihuwa tana da muhimmanci sosai za mu so muga jikokinka, kuma ba zan so wata macen ta ki ka saboda rashin haihuwa ba”
“Miya kawo wannan maganar kuma?”
“Kana tunanin Rahma zata zauna da kai a haka? Gashi ta fara korafi tun yanzu, shiyasa na so ka kara auren tun tuni amman ka ki”
“Babu zance aure a gabana Mama, ni bana iya zama da mace sama da daya bana iya rayuwa da mata biyu”
“Ba ni kadai ba Aliyu Momynka ma ta damu kuma duk wanda yake kaunar ka idan yaji wannan maganar dole zai damu da matsalarka”
“Ko wane bawa da akwai abunda ake kaddara masa Mama wata kila ni irin jarrabata kenan”
“Haka ne”
Ta fada tana share hawayenta sannan ta ce.
“Kuma ina son na fada maka karka taba yarda ko tunanin daukar kodarka ka ce zaka bawa Rahma dan na san halinka”
Murmushi yai mai sauti.
“Mi ya kawo wannan maganar kuma Mama? Idan na na bata ai Rahma matata ce”
“Eh matarka ce amman mu iyayenka ba ku yarda ka bata ba, kar ma ka taba wannan tunanin a rayuwarka, sai dai a nema mata magani ko kuma a samu wata dabam a siya mata amman ba taka ba sam ba mu aminta ba...”
“Nana Nana Nana”
Shiru bata amsa min ba, sai kallona take kamar bata gane ba. Hijab dina na cire na na aje Farida na tsaye tana kallona har na janyota domin bana iya daukarta gaba daya bakin kofar dakin na kawo ta na aje, na fito da komai na dakin na nemi tsohuwar tsintsiyar mu da naga a cikin kaya na share dakin, na dauki roba na shiga ciki na debo ruwa kasancewar cikin gidansu Farida a akwai rijiya, na dawo dakin na zuba ruwan na wanke na masa tas, duk abunda na ke Farida na tsaye tana kallona ta kasa komai, Hijab din nawa na saka na je gawon nama na siyo omo da kudin hannu na siyo fura da nono da madara na dawo, ko da na dawo Farida ta shige cikin gida, ni kuma na sake sakawa dakin omo na wanke shi ya cire duk wani karni da warin da yake sannan na dauko turaren da Kamal ya siya min na saka duk da kasancewar na jiki ba hakan be hana dakin kamshi ba, zane da zane na hada na zagaye sannan na sake debo wasu ruwan na kai na jata a haka na kaita gurin na zuba mata ruwa nai mata wanka ko ina na jikinta sai da na wanke sannan na sake dawowa da ita a cikin tufafi na dauki wata riga da Aliyu ya bani na saka lokacin da nai rashin lafiya ta manya na saka mata na daura mata dankwalin sai na aje ta a waje saboda dakin be gama budewa ba. Wasu ruwan na sake debowa na saka kayan ci abincin mu a gaba na wanke su ma sannan na dama mata furar na saka ludayi ina ta bata tana sha a hankali har ta sha ya iashe sai na debo mata ruwa na bata ta ta sha da yawa, sai ta sauke wani irin ajiyar zuciya yana saka ni jin tausayinta fiye da da, sannan na dauke ta na maida ta dakin na fito na saka tufafinta a gaba na wanke su na shanya sannan na daw dakin kusa da ita na zauna ina ta kallonta kamar yadda ita ma take kallona irin kallo da ke nuna bata gane ni ba, ko kuma bata san inda kanta yake ba kawai dai tana gani ne.
“Nana”
Bata amsa ni bata kuma daina kallona ba, hakan yasa na fashe da kuka na kama hannunta na rike, na dawo amman babu kudin maganin kuma n tararda ciwonta ya fi na da, sai dai ina tunanin dawowar tawa tai amfani domin gashi yanzu ina zaune gabanta ina kula da ita. Farida ce ta shigo dakin ta tsaya daga jikin kofa tana kallona.
“Bayan tafiyarki abun yai tsamari bata iya tashi komai a inda take take yinsa, na iya kokarina na kula da ita, daga baya Mama ta hanani, wacan kitchen din da ke cikin gida ya lalace shiyasa Baba ya buga mata kwano ya dawo da ita”
Hannu na saka na share hawayen idonta.
“Kin san ba zaki iya kula min davita yadda ya kamata ba, miyasa kika ce za ki yi? Miyasa kika bari na tafi? Aminta ba ta ce haka ba Farida yanzu da mahaifiyarki ce kina tunanin zan iya barinta a haka? Wallahi ba zan iya ba”
“Na yi iya kokarina Ataa Wallahi dawainiya da Ataa ba abu ne mai sauki ba”
“Eh na sani ai, ba abu ne mai sauki kula da Nana ba, ba abu ne mai sauki kula da uwar da ba taka ba, amman kin san ba dan dole ba babu yadda za ayi na tafi na barta, idan kika duba dalilin tafiyata kadai ya isa ya saka ki tausaya min ki tausaya mata ki kula da ita”
Ta yi shiru bata ce komai ba, ni kuma na mike tsaye na fito waje nai alwala nai sallah na cire Hijab din na aje na rafka uban tagumi ina kallonta, ta ina zan samu mafita? Duniyar nan ta juya min ko ina na raba ba dadi, duk inda na saka gaba da zimmar cimma burina sai wani abun ya shiga gabana ya tare, sai yanzu na gane kwata kwata bana da sa'ar rayuwa kuma bana da nasara a rayuwata sai dai hakan ba zai saka na kyale rayuwar Nana a haka ba, ko da ko raina zan ransa. Ta ina zan fara baran zan koma? Ko kuwa sata zan yi? Wani zai kaiwa koke na ko kuwa mutuncina zan siyar? Duka ban gan mafita a wannan ba. Da tunanin inda zan samu taimako na kwana na a raina.
ALIYU POV.
Bayan sun shiga cikin gidan ne Rahma na dakinta na wuce dakinsa yai wanka ya fita masallacin unguwar yai sallah la'asar sannan ya dawo cikin gidan ya shiga dakin Rahma, zaune ya same ta saman sallaya da alama ita ta gama sallah ne a yanzu. Kasa ya zauna kusa da ita yana kallon fuskarta dake dauke da damuwa, har ya bude baki yai mata magana sai wayarsa dake aljihu tai vibration alamar kira, ciro wayar yai ganin number Mama Fulani be tsaya bata lokaci ba ya daga.
“Aliyu kana ina?”
“Gida”
“Zo ina son magana da kai?”
“Lafiya dai?”
“Lafiya akan matsalar haihuwarka ne, Rahma ta fada mana gaskiya ai”
“Gaskiya kuma? Wani abun ne?”
Mama Fulani bata sake ce masa komai ba ta kashe wayar. Sai ya kalli Rahma
“Wani abun kika fada wa Mama?”
“Ban yi magana da Mama ba, amman na yi da Momy shi ma kuma ban san cewa ba su sani ba”
Wani kallo ha aika mata irin kallon nan na me kika fada musu.
“Na fada mata cewar matsalar haihuwar daga kai ne”
“For what?”
“Na dauka sun sani”
“Ko sun sani be kamata ki yi wannan maganar da su Rahma”
“Abun ne ya fara damuna yanzu, kuma a da suna ta ganin laifina amman yanzu za su fahimci ba daga ni ba ne wata kila za su daga min kafa”
“Amman idan matsalar daga ni ne be zama damuwarki ba? Kina kokarin chanjawa daga yadda na sanki Rahma”
“Ba canja nake ba Aliyu, damuwar ka damuwa ta ce, sai dai a yanzu matsalar nan ni ta fi shafuwa fiye da kai, a baki rame na ke zan iya mutuwa a ko da yaushe, ba tare da na bar abunda za a tuna da ni ba, amman kai kana nan raye har na tsawon lokaci”
Be sake ce mata komai ba ya mike tsaye yana saka wayar ajihunsa ya fice daga dakin. Cikin bacin rai ya isa gidan sam be jidadin abunda Rahma tai masa ba, domin be fadawa kowa ba kuma be za ci zata iya fadawa wasu ba, wasun ma kuma iyayensa. Ko da ya shiga falon Kanensa na ciki suna ta fira da dariya, be kula su ba ya haye sama zuwa dakin Mama Fulani sai ya samu Momy da Abbah a ciki suna fira shiga dakin da murmushinsa ya zauna saman kujerar da Abbah yake zaune yana gaisawa da shi.
“Abbah dawowan rana kai?”
“Eh Wallahi Hajiya Fulani ta fada min na ce bari na samu na zo mu gaisa da ita”
“Gaskiya kam ko mu da muke cikin gida muna wahalar ganawa da kai balle ba ko”
“To ya za ayi aikin ne a haka sai hakuri”
Mama Fulani ce ta shigo dakin ta tsaya jikin kofa tana kiran Aliyu.
“Aliyu magana nake son yin da kai fa”
Tashi Aliyu yai ya bi bayanta suka nufi dakin Baby a ciki suka zauna. Ta kalle irin duban bana wasa ba ta ce.
“Rahma ta ce matsalar daga gareka ne?”
“Matsalar me ba?”
Yayi kamar be fahimci abunda take magana akai ba.
“Ba mu da matsayin da zaka fada mana matsalar ka ne Aliyu? Ko kuma ka boye mana gaskiya ne saboda ka kare matar ka?”
“Ba ko daya, na san idan na fada muku za ku damu, ni kuma ba haka na ke so ba, kuma ko da matsalar daga ni ne idan Allah ya rubuta zan haihu zan haihu”
“Da gaske ne kenan?”
“Gaskiya ne Mama”
Mama Fulani ta rufe baki idonta cike da kwalla.
“Aliyu da gaske fa ka ce”
Na gyada mata kai.
“Gaskiya ne Mama, sun ce kwayoyin halittafa ba su da karfin da za su rayu a mahaifar Rahma”
“Kuma babu wani abun da za a iya yi? Babu wata mafita”
Ta tambaya cikinnmuryar kuka domin har ga Allah bata son abunda ya taba Aliyu, balle kuma haihuwa da take babbar abu.
“Mafita kawai addu'a kuma zan cigaba da neman magani ko Allah zai saka a dace”
Dafe kai tai cike da tausayinsa. Tashi Aliyu yai ya koma kusa da ita ya zauna.
“Mama ki daina damuwa ba komai”
“Akwai komai Aliyu, haihuwa tana da muhimmanci sosai za mu so muga jikokinka, kuma ba zan so wata macen ta ki ka saboda rashin haihuwa ba”
“Miya kawo wannan maganar kuma?”
“Kana tunanin Rahma zata zauna da kai a haka? Gashi ta fara korafi tun yanzu, shiyasa na so ka kara auren tun tuni amman ka ki”
“Babu zance aure a gabana Mama, ni bana iya zama da mace sama da daya bana iya rayuwa da mata biyu”
“Ba ni kadai ba Aliyu Momynka ma ta damu kuma duk wanda yake kaunar ka idan yaji wannan maganar dole zai damu da matsalarka”
“Ko wane bawa da akwai abunda ake kaddara masa Mama wata kila ni irin jarrabata kenan”
“Haka ne”
Ta fada tana share hawayenta sannan ta ce.
“Kuma ina son na fada maka karka taba yarda ko tunanin daukar kodarka ka ce zaka bawa Rahma dan na san halinka”
Murmushi yai mai sauti.
“Mi ya kawo wannan maganar kuma Mama? Idan na na bata ai Rahma matata ce”
“Eh matarka ce amman mu iyayenka ba ku yarda ka bata ba, kar ma ka taba wannan tunanin a rayuwarka, sai dai a nema mata magani ko kuma a samu wata dabam a siya mata amman ba taka ba sam ba mu aminta ba...”