Sashe 5
Zaki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Can da yamma Nana ta dawo har da biredinta a hannu, Lukman na bayanta da gorar ruwansa rataye a wuyansa. Biredin kawai muka ci muka sha ruwa sannan ya dauko kudin da ta zo da su da sauran kudin da suke rage mana idan mun siye abinci gaba daya kudin ba su wuce dubu uku da yan kai ba.
“Wadannan kudi ba zasu iya mu kama haya ba, ni ban san yadda za mu yi ba”
Magana take ina karantar tashin hankalin dake zuciyarta har yake bayyana kansa a fuskarta, ni dai na yi shiru ina ta tunanin sama mana mafita.
“Nana ko mu nemi gadi wani gida? Ta yadda zamu samu gurin zama”
“Wa zai ba mace gadi? Idan mu mun samu ni ina zan iya tare barawo?”
“Ai dan mu samu gurin zama ne”
“Hakan ba zai yi ba, sai dai na bincika wani gurin ko Allah zai sa mu samu”
Tun daga ranar kullum Nana cikin neman gurin da zamu koma mu raba take amman ba mu samu ba, yawancin inda muke samu duka filaye ne mu kuma muna tsoron zama a fili sai dai a kangon gidan da aka fara aka bari ko kuma ba a karasa ba ko ya kuma ginin daya soma zubewa.
A kullum da fargabar zuwan Alhajin muke kwana mu tashi muna ta zuba ido ko zai zo amman shiru be sake zuwa ba har aka kwashe kwana kusan goma shabiyar, hakan yasa muka koma muna rayuwarmu ta yau da gobe cikin kwanciyar hankali. Musamman ni da ban sake saka wannan bakin mutumen a idona na ba. Yau ma da gari muka karya duk kuwa da kasancewar bana sonsa amman babu yadda na iya dole na ci ko babu dadi, bayan mun gama sha ne na tashi nai alwalar isha'i na kabbatar sallah. Ina cikin sallah na ji ihun Nana waccw ta kewa a bandaki kasa karasa sallar nai jin ihun yayi yawa na dauki fitilar hannu dake dakin na fito waje da sauri ni da Lukman muka nufi kewan ina Haskawa sai na hango katon maciji ya nade gurin daya yana ta zuro mana kansa, Nana kuma ta fadi gefe daya tana ta murje murje da alama cizonta yai ko kuma sara, Lukman ya saka kara ni kuma na saki fitilar a firgice na ruga izuwa titi cikin hudun hangon gidan ina neman masu taimaka mana, daman na san ba za a rasa irin wadannan abubuwan ba a guri kamar wannan, musamman da dare ba hudu yake zageyemu har sai idan mun kunna kara ko fita ko kuma hasken farin wata, wutar nepa kan sai dai mu hangota a manyan gidaje. Da ihu da karaji na isa titin gawon nama ina ta neman wadanda zasu taimaka mana, mazan da suke zama a gurin titi suka yo kaina da sauri ni kuma na shiga gaba ina gudu suna gudu har muka dawo cikin kangon gidan dake cike da hudu, masu wayoyi suka kunna wayarsu suka haske bandakin sai Nana aka gani babu macijin babu labarinsa, motsin kirki ma bata iya yi da sauri wani yace a bashi kyale sai ya daure inda yake zaton macijin ya tsareta wato kafar data rike.
“Ku nemo Napep? A kaita asibiti”
Daya daga cikinsu ya fada ni da Lukam babu abunda muke sai kuka ni ina rike da ita Lukman kuma yana tsaye bayana, a gurin wasu samarin ke kallo domin yau babu wannan bakin gentleman n a fuskata mai hana kowa ganin ainahin kyawo na. Ban san wanda ya kira Napep din ba nadai ga an shigo da ita har gurin Bukkarmu samarin suka rikata suka sakata ciki ni Lukman na shiga gaba ni kuma na zauna baya tare da ita ina hawaye kamar ba gobe.
Ko wane motsi nata jinsa nake cikin kashina ji nake kamar ciwon a jikina yake, mahaifiyata ita ce duniyata, na gwada kokarina akan tsagaita kukana sai na gano ashe ni ba ba Jaruma ba ce a gafen dauri. Wata asibitin kudi mai zaman kanta Mai Napep din ya kaimu a lokacin da muka isa emergency sai suka karbe mu da gaggawa aka wuce da ita ciki Mai Napep ya juya yai tafiyarsa ni da Lukman sai muka yi tsaye waje. Har sai da Nurse din ta dawo kirana ta dauki sunan Nana ta bukaci naje wani guri na karbo kati sai na tuna da babu sisi a tare da ni, adole na bar Lukman a gurin na fita na hau achaba na je na dauko kudinta gaba daya na dawo naje na biya kudin katin sai kuma aka ce likita na son ganina. Da sauri na nufi inda Nurse din ta nuna na tura kofar office din na shiga hankalina a tashe fuskata duk hawaye ya bata ta, hannuna rike da yar jakar da Nana take zuwa da ita bara wacce kudin suke ciki.
“Nurse tace kana son ganina”
“Ke ce wa?”
Likitan ya tambayata yana min wani kallo daga sama zuwa kasa, duk wanda ya kalli sutura baya bukatar na fada masa cewar ba mu da shi, tufafin da nake saye da su kawai sun isa su isarda sakon talaucin da muke tare da shi.
“Mamata na kawo wacce maciji ya tsara”
“ina Babanku?”
“Babanmu ya rasu”
“To ina yan'uwanku da ke zan yi Magana”
“Ko minene likita ka Fada min mamata bata da kowa a nan sai ni, duka yan'uwan mu suna nijar”
Na Fada idona na sake cika da kwalla. Kallo yai sai ya sake kallona sannan yace.
“Okay wannan allurar za ki siyo naira dubu ashirin da daya za ki kashe”
Ya Fada yana mika min wata farar takarda. Ina karba na juya jiki ba kwari zan fice sai na ji ya ce.
“Kina da kudin ne? Idan ba ki kawo maganin nan da wasu hours ba Mamaki zata iya mutuwa”
Juyowa nai idona na zubar da kwalla ma girgiza masa kai dan bana ko iya magana.
“Babu?”
Na gyada masa kai.
“Bude baki kiyi magana wannan asibiti na ce zan iya taimaka miki idan baki da su”
“Wallahi ba ni da su ban san inda zan samo ba, bara mu muke kamin mu saye abincin”
Shiru yai kamar mai nazari, sannan ya kalleni ya ce.
“Shikenan zan mata allurar kuma zan ya mata tiyata na cire dafin macijin”
Da sauri na risina kasa ina masa godiya wani irin jindadi ya rufe jin za a ceci mahaifiyata sai dai ban taba jin inda akai wa wani tiyata aka cire dafin maciji ba sai dai allura.
“Taso muje ki saka hannu a file”
Da sauri na mike tsaye ina share hawayena, yana gaba ina binsa har muka shiga wani daki mai cike da nurse da yawa ya dauko wata takardar ya miko tare da nuna min inda zan saka hannu. Hannunsa ya dora saman nawa yana yimin sigh din yadda zan hi daidai, ina daho kaina nai arba da wata nurse tana girgiza min kai alamar kai, sai dai ban gane abunda take nufi ba na tausayi ne ko kuwa na kar nai yi ne oho ni dai fatana a ceto mahaifiyata....
https://my.w.tt/GuQH5GZKb9
*Z A K I*
By Khadeeja Candy
4️⃣
Misalin goma aka shigo da ita tiyata amman basu fito ba sai karfe uku da wani abu na dare.
Anyi mata tiyata cikin nasarar Allah da iyawarsa, saidai a halin da naga mahaifiyata sai na kara matso da maraicin mu kusa ni da Lukman. A wani dakin mai kyau aka ajeta kamar matar wani babban mutum ko kuma wata hajiya, a jikinta an manna mata wasu na'urori har a hancinta a wani abu mai kamar kwanfuwuta nake kallon tafiyar numfashinta, sai dai tana kwance a gurin kamar gawa jikinta babu tufafi sai wani zanen asibiti da aka saka a lulluba mata.
Ina tare da ita har asuba ban runtsa ba, gani nake kamar zata iya farkowa ta bukuci wani abun ko da yake babu komai a tare da ni wanda zata iya ci ko ta sha, lukman ne kawai ke ta bachinsa hankalinsa kwance.
Misalin takwas da rabi likitan ya shigo cikin shiga ta kananan kaya da rigar likitoci a samansu fuskarsa a sake yana ta min murmushi kamar mun saba.
“Ina kwana?”
Na gaisheshi cikin girmamawa. Sai ya amsa min kamar be gane ni ba, ba kuma kallon rashin ganewar bane, wata kila sai a yau ne yake tantance irin hallittar da Allah yai ta kyau mai daukar hankalin mace balle kuma namiji.
“Miye sunanki?”
“Aisha amman ana kirana Ataa”
“A nan kuka kwana?”
Ya tambaya yana kara tantance kyawun surar jikina.
“Eh”
“Ayyah ban sani ba ai da na kawo muku abun shimfida ko kina da shi”
Na girgiza kai alamar aa a cikin yanayin dake nuna dukan hankalina da damuwata tana gurin mahaifiyata ne.
“Da gaske baki da kowa a nan Nigeria? Ku yan nijar ba naga akwai wadanda suke da yan'uwa a nan ba?”
“Ni ba mu da su, ba a mu da kowa a nan”
Na fada masa cike da gundira da tambayoyinsa. Sai naga yayi murmushi kamar wanda jin hakan yai masa dadi, sai ya saka hannunsa aljihu ya nufi mahaifiyata yana dubata.
“Ki samo riga ki saka mata da zanen da zai iya rufe kafafunta, na bada a siyo mata maganin dubu dari da bakwai manyan magunguna ne masu tsada yadda mahaifiyarki za tai saurin jin sauki kuma an mata allurar bayan na mata sai nai mata operation na cire mata dafin macijin”
Wani irin dadi ne ya lullube ni sai na rasa ta inda zan fara masa godiya, hawayen farinciki suka cika ido har naji kamar na dauke shi na hade, a rayuwata ta duniya tunda Nana ta haife ni ban taba karo ko ganin mutum mai tausayi da jinkan masarasa irinmu ba kamar wannan likitan.
“Na gode Allah ya biyaka ya saka mata da alheri, Allah ya daukaka asibitinku Ya saka maka da aljanna ka taimaki rayuwata sosai ba zan taba manta ka ba”
Murmushi yai yasa hannunsa aljihu ya ciro kudin da za su kai dubu goma ya miko min.
“Ga wannan, ki je ki siya abinci ki yi duk abunda kike bukata, kuma idan mahaifiyarki ta farka ki kirani karki bata komai”
“Wadannan kudi ba zasu iya mu kama haya ba, ni ban san yadda za mu yi ba”
Magana take ina karantar tashin hankalin dake zuciyarta har yake bayyana kansa a fuskarta, ni dai na yi shiru ina ta tunanin sama mana mafita.
“Nana ko mu nemi gadi wani gida? Ta yadda zamu samu gurin zama”
“Wa zai ba mace gadi? Idan mu mun samu ni ina zan iya tare barawo?”
“Ai dan mu samu gurin zama ne”
“Hakan ba zai yi ba, sai dai na bincika wani gurin ko Allah zai sa mu samu”
Tun daga ranar kullum Nana cikin neman gurin da zamu koma mu raba take amman ba mu samu ba, yawancin inda muke samu duka filaye ne mu kuma muna tsoron zama a fili sai dai a kangon gidan da aka fara aka bari ko kuma ba a karasa ba ko ya kuma ginin daya soma zubewa.
A kullum da fargabar zuwan Alhajin muke kwana mu tashi muna ta zuba ido ko zai zo amman shiru be sake zuwa ba har aka kwashe kwana kusan goma shabiyar, hakan yasa muka koma muna rayuwarmu ta yau da gobe cikin kwanciyar hankali. Musamman ni da ban sake saka wannan bakin mutumen a idona na ba. Yau ma da gari muka karya duk kuwa da kasancewar bana sonsa amman babu yadda na iya dole na ci ko babu dadi, bayan mun gama sha ne na tashi nai alwalar isha'i na kabbatar sallah. Ina cikin sallah na ji ihun Nana waccw ta kewa a bandaki kasa karasa sallar nai jin ihun yayi yawa na dauki fitilar hannu dake dakin na fito waje da sauri ni da Lukman muka nufi kewan ina Haskawa sai na hango katon maciji ya nade gurin daya yana ta zuro mana kansa, Nana kuma ta fadi gefe daya tana ta murje murje da alama cizonta yai ko kuma sara, Lukman ya saka kara ni kuma na saki fitilar a firgice na ruga izuwa titi cikin hudun hangon gidan ina neman masu taimaka mana, daman na san ba za a rasa irin wadannan abubuwan ba a guri kamar wannan, musamman da dare ba hudu yake zageyemu har sai idan mun kunna kara ko fita ko kuma hasken farin wata, wutar nepa kan sai dai mu hangota a manyan gidaje. Da ihu da karaji na isa titin gawon nama ina ta neman wadanda zasu taimaka mana, mazan da suke zama a gurin titi suka yo kaina da sauri ni kuma na shiga gaba ina gudu suna gudu har muka dawo cikin kangon gidan dake cike da hudu, masu wayoyi suka kunna wayarsu suka haske bandakin sai Nana aka gani babu macijin babu labarinsa, motsin kirki ma bata iya yi da sauri wani yace a bashi kyale sai ya daure inda yake zaton macijin ya tsareta wato kafar data rike.
“Ku nemo Napep? A kaita asibiti”
Daya daga cikinsu ya fada ni da Lukam babu abunda muke sai kuka ni ina rike da ita Lukman kuma yana tsaye bayana, a gurin wasu samarin ke kallo domin yau babu wannan bakin gentleman n a fuskata mai hana kowa ganin ainahin kyawo na. Ban san wanda ya kira Napep din ba nadai ga an shigo da ita har gurin Bukkarmu samarin suka rikata suka sakata ciki ni Lukman na shiga gaba ni kuma na zauna baya tare da ita ina hawaye kamar ba gobe.
Ko wane motsi nata jinsa nake cikin kashina ji nake kamar ciwon a jikina yake, mahaifiyata ita ce duniyata, na gwada kokarina akan tsagaita kukana sai na gano ashe ni ba ba Jaruma ba ce a gafen dauri. Wata asibitin kudi mai zaman kanta Mai Napep din ya kaimu a lokacin da muka isa emergency sai suka karbe mu da gaggawa aka wuce da ita ciki Mai Napep ya juya yai tafiyarsa ni da Lukman sai muka yi tsaye waje. Har sai da Nurse din ta dawo kirana ta dauki sunan Nana ta bukaci naje wani guri na karbo kati sai na tuna da babu sisi a tare da ni, adole na bar Lukman a gurin na fita na hau achaba na je na dauko kudinta gaba daya na dawo naje na biya kudin katin sai kuma aka ce likita na son ganina. Da sauri na nufi inda Nurse din ta nuna na tura kofar office din na shiga hankalina a tashe fuskata duk hawaye ya bata ta, hannuna rike da yar jakar da Nana take zuwa da ita bara wacce kudin suke ciki.
“Nurse tace kana son ganina”
“Ke ce wa?”
Likitan ya tambayata yana min wani kallo daga sama zuwa kasa, duk wanda ya kalli sutura baya bukatar na fada masa cewar ba mu da shi, tufafin da nake saye da su kawai sun isa su isarda sakon talaucin da muke tare da shi.
“Mamata na kawo wacce maciji ya tsara”
“ina Babanku?”
“Babanmu ya rasu”
“To ina yan'uwanku da ke zan yi Magana”
“Ko minene likita ka Fada min mamata bata da kowa a nan sai ni, duka yan'uwan mu suna nijar”
Na Fada idona na sake cika da kwalla. Kallo yai sai ya sake kallona sannan yace.
“Okay wannan allurar za ki siyo naira dubu ashirin da daya za ki kashe”
Ya Fada yana mika min wata farar takarda. Ina karba na juya jiki ba kwari zan fice sai na ji ya ce.
“Kina da kudin ne? Idan ba ki kawo maganin nan da wasu hours ba Mamaki zata iya mutuwa”
Juyowa nai idona na zubar da kwalla ma girgiza masa kai dan bana ko iya magana.
“Babu?”
Na gyada masa kai.
“Bude baki kiyi magana wannan asibiti na ce zan iya taimaka miki idan baki da su”
“Wallahi ba ni da su ban san inda zan samo ba, bara mu muke kamin mu saye abincin”
Shiru yai kamar mai nazari, sannan ya kalleni ya ce.
“Shikenan zan mata allurar kuma zan ya mata tiyata na cire dafin macijin”
Da sauri na risina kasa ina masa godiya wani irin jindadi ya rufe jin za a ceci mahaifiyata sai dai ban taba jin inda akai wa wani tiyata aka cire dafin maciji ba sai dai allura.
“Taso muje ki saka hannu a file”
Da sauri na mike tsaye ina share hawayena, yana gaba ina binsa har muka shiga wani daki mai cike da nurse da yawa ya dauko wata takardar ya miko tare da nuna min inda zan saka hannu. Hannunsa ya dora saman nawa yana yimin sigh din yadda zan hi daidai, ina daho kaina nai arba da wata nurse tana girgiza min kai alamar kai, sai dai ban gane abunda take nufi ba na tausayi ne ko kuwa na kar nai yi ne oho ni dai fatana a ceto mahaifiyata....
https://my.w.tt/GuQH5GZKb9
*Z A K I*
By Khadeeja Candy
4️⃣
Misalin goma aka shigo da ita tiyata amman basu fito ba sai karfe uku da wani abu na dare.
Anyi mata tiyata cikin nasarar Allah da iyawarsa, saidai a halin da naga mahaifiyata sai na kara matso da maraicin mu kusa ni da Lukman. A wani dakin mai kyau aka ajeta kamar matar wani babban mutum ko kuma wata hajiya, a jikinta an manna mata wasu na'urori har a hancinta a wani abu mai kamar kwanfuwuta nake kallon tafiyar numfashinta, sai dai tana kwance a gurin kamar gawa jikinta babu tufafi sai wani zanen asibiti da aka saka a lulluba mata.
Ina tare da ita har asuba ban runtsa ba, gani nake kamar zata iya farkowa ta bukuci wani abun ko da yake babu komai a tare da ni wanda zata iya ci ko ta sha, lukman ne kawai ke ta bachinsa hankalinsa kwance.
Misalin takwas da rabi likitan ya shigo cikin shiga ta kananan kaya da rigar likitoci a samansu fuskarsa a sake yana ta min murmushi kamar mun saba.
“Ina kwana?”
Na gaisheshi cikin girmamawa. Sai ya amsa min kamar be gane ni ba, ba kuma kallon rashin ganewar bane, wata kila sai a yau ne yake tantance irin hallittar da Allah yai ta kyau mai daukar hankalin mace balle kuma namiji.
“Miye sunanki?”
“Aisha amman ana kirana Ataa”
“A nan kuka kwana?”
Ya tambaya yana kara tantance kyawun surar jikina.
“Eh”
“Ayyah ban sani ba ai da na kawo muku abun shimfida ko kina da shi”
Na girgiza kai alamar aa a cikin yanayin dake nuna dukan hankalina da damuwata tana gurin mahaifiyata ne.
“Da gaske baki da kowa a nan Nigeria? Ku yan nijar ba naga akwai wadanda suke da yan'uwa a nan ba?”
“Ni ba mu da su, ba a mu da kowa a nan”
Na fada masa cike da gundira da tambayoyinsa. Sai naga yayi murmushi kamar wanda jin hakan yai masa dadi, sai ya saka hannunsa aljihu ya nufi mahaifiyata yana dubata.
“Ki samo riga ki saka mata da zanen da zai iya rufe kafafunta, na bada a siyo mata maganin dubu dari da bakwai manyan magunguna ne masu tsada yadda mahaifiyarki za tai saurin jin sauki kuma an mata allurar bayan na mata sai nai mata operation na cire mata dafin macijin”
Wani irin dadi ne ya lullube ni sai na rasa ta inda zan fara masa godiya, hawayen farinciki suka cika ido har naji kamar na dauke shi na hade, a rayuwata ta duniya tunda Nana ta haife ni ban taba karo ko ganin mutum mai tausayi da jinkan masarasa irinmu ba kamar wannan likitan.
“Na gode Allah ya biyaka ya saka mata da alheri, Allah ya daukaka asibitinku Ya saka maka da aljanna ka taimaki rayuwata sosai ba zan taba manta ka ba”
Murmushi yai yasa hannunsa aljihu ya ciro kudin da za su kai dubu goma ya miko min.
“Ga wannan, ki je ki siya abinci ki yi duk abunda kike bukata, kuma idan mahaifiyarki ta farka ki kirani karki bata komai”