Sashe 19
Zaki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Aa zata iya guduwa da su, baka san halin irin mabaratan nan ba, idan kin shirya ki shigo ciki ki fara aikin”
Tana fadar hakan ta juya ya shige ciki, ni kuma na tako dan stairs din da ke gurin da zimmar shiga ciki sai kuma nai tsaye ganin yadda mijinta ya tsaya a kofar yana ta min kallon kyama.
“Ki koma gida ki wanke wannan bakin na fuskarka ki and make sure kin canja kayanki kin yi wanka kin fito fresh sannan ki dawo aikin nan”
Ya fada yana jefo min kudin da nake saka ran sun fi dubu takwas din ya juya ya shigewarsa, ni kuma na duka da sauri na kwashi yan dari biyar biyar din jikina har rawa yake...
*Z A K I*
By Khadeeja Candy
1️⃣2️⃣
Kamar wacce akai wa kyauta makka yana na nufo gida farinciki ya cika min zuciya. Ina tafe fuskarta dauke da murmushi duk wanda ya kalleni ya san ina cikin farinciki a yau. Sallamar shiga gidansu Farida ma da karfi nai ta Mahaifiyar Farida na tsakar gida zaune tana gyara Alayyahu har kasa na risina na gaishe ta sai ta masa sama-sama sannan ta bawa banza ajiyata ni kuma na tashi na nufi kitchen da Nana take. Kwance na same ta kamar yadda na fita na barta. Kusa da ita na zauna ina washe hakora.
“Nana na samo kudi har dubu takwas”
Dan dagowa tai ta kalleni cike da mamaki.
“Ina kika kudi har haka, bara ki kai?”
“A'a ai ba zan sake yin bara ba, sanadin raban nan aka kade Lukman, bana ma marmarin sake komawa bara, wani gida naje na ce musu zan yi musu aiki, amman sai sun fara bani kudi sannan na fara, na fada musu cewar Mahaifiyata bata da lafiya”
“Kuma suka yarda suka ba ki?”
“Matar ba ta yarda ba, mijin ne ya ba ni”
Hannu ta shafa kaina tana murmushi.
“Allah ya miki albarka, wannan kalubale da kika fuskata tun a yanzu da kurciyarki Allah ya tallafa miki ya baki wanda zai mutunta ki ya zame miki gata”
Kasa amsawa nai a fili saboda kunya, sai a zuciyata na amsa da Amin.
“Nana ina takardar msganin take sai naje na siyo”
“Ban zo da takardar ba, komai a can ya bar asibiti”
“Kai amman ban jidadi ba, yanzu ya zamu yi kenan?”
“Ataa ki daina dorawa kanki damuwa da wahalar da kanki a kaina”
“Idan ban miki ba wa zan yi ma, ba ni da kowa a yanzu sai ke, idan na rasa ki ban san iya halin da zan shiga ba”
Na fada idona tab da hawaye. Sai tai murmushi tana ta kallona cike da kauna.
“Ko asibintin za mu koma?”
“Asibiti babu komai sai cin kudi, kara ma kije gurin masu magani ki siyo abunda ya sawwaka, sauran kudin ki siyo mana abinci da su”
“Amman maganin chemist anya zai yi kuwa?Ai kara dai mu koma asibintin zai fi”
“Ataa na gaji da zaman asibitin nan, kuma wannan kudin idan ma muje karewa zai yi”
“Ko ya kare indai kin samu lafiya ba matsala ba ne”
“Aa kara dai mu ci abinci da su zai fi mana”
“Amman Nana rashin sha maganin zai iya janyo miki matsala fa”
“Da muje a kashe kudin ba a samu biyan bukata ba kara dai mu san mun saka a ciki, tun da kika fita ba ki ci komai ba, ni ma da nake nan ban cin ba, magani ma ai ba yayi sai da abinci”
Gaskiya ta fada, sai dai ni na fi damuwa da ciwonta fiye da abincin, na san kudin ba zai isa maganin duka ba.
Ta shi nai na fita daga dakin cikin rashin jindadin duk farinciki da murnar da na ke sai suka koma ciki.
Wani shagon provision na nufa na siyo mata biredi da madara da gwangwanin suga, ni kuma na siyo ma kaina gari da gida da suga sannan na dawo gidan, wannan karon Maman Farida ba tsakar gidan, hakan yasa ni jindadin wucewa na shigewa inda Nana ta ke na mika mata ledar sannan na fito da dauki kofi biyu da ruwa na koma dakin, ita na fara hadawa da ruwan sanye sannan ni kuma na hada nawa garin na saka suga na sha, yadda take fisgar biredin tana sai ka rantse da Allah ta shekara bata ci abinci ba. Tausayinta ne ya lullube, an cire mata koda daya dan zalinci, ga yunwa tana fama da ita babu mai bata sai Allah, dan ya tafi ya barta a garin nema yafiyarta. Tabbas ba zan taba manta Doc Asim ba, ba kuma zan taba yafe masa ba, sanadinsa na kwana a cell, na rasa kanena, ga mahaifiyata a halin da ba zan iya juye ganinta a haka ba.
Idan zan yi tunani sai na rasa da wanne zan fara abubuwan duniya sun taru sun min tsaye a raina, har wani zafi na ke jin kirjina yana yi idan ina tunani, na rika jin zuciyata kamar zata fasa kirjina ta fito.
Bayan mun gama na dauki kofunan na kai waje na wanke na aje mata a inda na gansu, ashe ta hangi lokacin da na aje sai ganinta nai ta fito rai a bace tana ta masifa wai mun taba mata kofi kazamai da mu, a kan idona ta dauki kofunan ta wilgar bayan gidan, na ji zafi sosai amman ban nuna mata ba, domin fadanta akan gaskiya ne, ni na taba mata abu da ban taba ba da bata min wannan maganar ba.
Kitchen da muka raba na koma na dauko duka kayan wanke wanken na fito da su tsakar gidan, na je na siyo omo na debo ruwa a rijiyar gidan na zauna na wake su tas, na dauka na kai kitchen din wanda zan iya cewa dakinmu. Sannan na fito rike da soson wankanmu na dibi ruwan a robarmu na shiga bandakin tsakar gidan nai wanka, na wanka jiki sau uku sannan na saka ruwa na dauraye na fito fes da ni ni kaina har wata ni'ima na ke jin tana shiga jikina. Ban ssmu na shafa mai ba saboda yanayin garin da zafi, sai kawai na saka daya daga cikin tufafin da na ke ji da su, na dauki bakin dankwalina nai nikab da shi sannan na saka Hijab sama na duka inda kudin sukd na dauki naira dari na dan hawan acha6a, domin akwai tazara a tsakanin unguwar mu da tasu.
“Nana zan tafi”
“Yau za ki fara aikin?”
“To Allah ya taimaka ya tsare a dawo lafiya”
“Amin, ki aje wannan kudin muna cin abinci da su, idan na samu wasu wadanda suka yarda nai aikin yamma sai na rika zuwa ina musu kin ga idan an ban kudi sai na hada da wannan mu koma asibitin”
“To Allah ya nufa”
Duk maganar da nai mata da hausa nai ta ita kuma sa ta maida min da yaren da tafi kwarewa akai wato buzanci. Sai da nai mata sallama sannan na fita, ban yi nisa sosai na samu mashin na tara na hau yana sauke ni na bashi hansi ya karba ya wuce ni kuma na buga kofar gate din a hankali. Mai gadin ne ya leko yana ganina sai ya fito gaba daya.
“Baiwar Allah lafiya”
“Lafiya kalau, ni ce wacce na zo neman aiki dazu kuma suka ce sun dauke amman sai naje na shirya”
Wani kallo yai min tun daga sama na har kasa, nasan kallon baya rasa nasaba da bakin kyallen da na saka na rufe fuskata, wata kila yana munanamin zato ne.
“Bari dai na fara fada musu tukuna”
Haka ya barni tsaye a gurin ya koma ciki, ba dauki dogon lokaci ba sai gashi ya dawo ya bude min gate din.
“Ance kin shigo”
“Na gode”
Na fada ina saka kafata cikin gidan, sai a yanzu ne nake kara kare masa kallo babban gida ne da za ayi iya kiransa da aljannar duniya, ko a harabar gidan kadai aka barka zaka sha kallo tun daga kan furanni da kuma manyan motocin da ke gidan, ko wace kofa an kawata ta da furanni. A inda na naga sun fito dazun na na bi stairs din na isa gaban katuwar kofar mai kyau na yi knocked a hankali, shiru ban ji an bude kofar ba, hakan yasa na sake knocked, nan ma shiru ba a bude min ba, sai da na yi na ukun sannan aka soma motsa kofar aka bude. Mijin matar ne ya bude min yana sanye da kananan kayan, bakin wando da jar t-shirt, fukarsa kamar ta kullum babu alamar murmushi ma balle kuma ayi zancen dariya.
“Ina wuni”
Be amsa min ba, sai kallon fuskata yake kamar nai son tantace abu, ni kuma nai tsaye a gurin cike da tsawalla, gabana sai faduwa yake ina jin kamar cewa zai yi ya fasa baya so. Sakin kofar yai ya juya ya koma ciki ya barni a gurin tsaye shi be cena shigo ba, kuma be ce min na tafi ba, ganin hakan yasa na yi tsaye agurin kamar an dasani, har sai da na ji muryar matar tana ce min na shigo.
Kamar wata hawainiya haka na rika taka tile din mai tsantsi gudun kar na taba da karfi su ce na musu ba daidai. A kan wata babban kujera suke zaune tun na shigo falon daga ita har shi babau wanda ya kalleni balle ya ce min wani abu. Haka ma zauna a gurin kamar daman sun biyana dan na zo na zauna gabansu ne.
“Ke anya macen kwarai ce? Miyasa kika rufe fuskarki?”
Matar ta fada tana min wani kallon uku saura kwata.
“Ba komai, na fi jindadi idan na rufe fuskar ne shiyasa na rufe, ina da konuwa a fuskar ne”
Ta tabe baki.
“Bedrooms din mu za ki fara shiga ki gyara komai da nan falon sannan ki shiga kitchen ki gyara kuma ki wanke duka kayan da suke can sannan ki yi mopping ki saka mana turaren kanshi”
“To ina dakunan suke?”
Da yatsanta ta nuna inda yake har na mike tsaye sai kuma ya kira ni.
“Keee ban da sata kar ki kuskura daukar mana wani a gida”
“Ban taba sata ba a rayuwa”
Tana fadar hakan ta juya ya shige ciki, ni kuma na tako dan stairs din da ke gurin da zimmar shiga ciki sai kuma nai tsaye ganin yadda mijinta ya tsaya a kofar yana ta min kallon kyama.
“Ki koma gida ki wanke wannan bakin na fuskarka ki and make sure kin canja kayanki kin yi wanka kin fito fresh sannan ki dawo aikin nan”
Ya fada yana jefo min kudin da nake saka ran sun fi dubu takwas din ya juya ya shigewarsa, ni kuma na duka da sauri na kwashi yan dari biyar biyar din jikina har rawa yake...
*Z A K I*
By Khadeeja Candy
1️⃣2️⃣
Kamar wacce akai wa kyauta makka yana na nufo gida farinciki ya cika min zuciya. Ina tafe fuskarta dauke da murmushi duk wanda ya kalleni ya san ina cikin farinciki a yau. Sallamar shiga gidansu Farida ma da karfi nai ta Mahaifiyar Farida na tsakar gida zaune tana gyara Alayyahu har kasa na risina na gaishe ta sai ta masa sama-sama sannan ta bawa banza ajiyata ni kuma na tashi na nufi kitchen da Nana take. Kwance na same ta kamar yadda na fita na barta. Kusa da ita na zauna ina washe hakora.
“Nana na samo kudi har dubu takwas”
Dan dagowa tai ta kalleni cike da mamaki.
“Ina kika kudi har haka, bara ki kai?”
“A'a ai ba zan sake yin bara ba, sanadin raban nan aka kade Lukman, bana ma marmarin sake komawa bara, wani gida naje na ce musu zan yi musu aiki, amman sai sun fara bani kudi sannan na fara, na fada musu cewar Mahaifiyata bata da lafiya”
“Kuma suka yarda suka ba ki?”
“Matar ba ta yarda ba, mijin ne ya ba ni”
Hannu ta shafa kaina tana murmushi.
“Allah ya miki albarka, wannan kalubale da kika fuskata tun a yanzu da kurciyarki Allah ya tallafa miki ya baki wanda zai mutunta ki ya zame miki gata”
Kasa amsawa nai a fili saboda kunya, sai a zuciyata na amsa da Amin.
“Nana ina takardar msganin take sai naje na siyo”
“Ban zo da takardar ba, komai a can ya bar asibiti”
“Kai amman ban jidadi ba, yanzu ya zamu yi kenan?”
“Ataa ki daina dorawa kanki damuwa da wahalar da kanki a kaina”
“Idan ban miki ba wa zan yi ma, ba ni da kowa a yanzu sai ke, idan na rasa ki ban san iya halin da zan shiga ba”
Na fada idona tab da hawaye. Sai tai murmushi tana ta kallona cike da kauna.
“Ko asibintin za mu koma?”
“Asibiti babu komai sai cin kudi, kara ma kije gurin masu magani ki siyo abunda ya sawwaka, sauran kudin ki siyo mana abinci da su”
“Amman maganin chemist anya zai yi kuwa?Ai kara dai mu koma asibintin zai fi”
“Ataa na gaji da zaman asibitin nan, kuma wannan kudin idan ma muje karewa zai yi”
“Ko ya kare indai kin samu lafiya ba matsala ba ne”
“Aa kara dai mu ci abinci da su zai fi mana”
“Amman Nana rashin sha maganin zai iya janyo miki matsala fa”
“Da muje a kashe kudin ba a samu biyan bukata ba kara dai mu san mun saka a ciki, tun da kika fita ba ki ci komai ba, ni ma da nake nan ban cin ba, magani ma ai ba yayi sai da abinci”
Gaskiya ta fada, sai dai ni na fi damuwa da ciwonta fiye da abincin, na san kudin ba zai isa maganin duka ba.
Ta shi nai na fita daga dakin cikin rashin jindadin duk farinciki da murnar da na ke sai suka koma ciki.
Wani shagon provision na nufa na siyo mata biredi da madara da gwangwanin suga, ni kuma na siyo ma kaina gari da gida da suga sannan na dawo gidan, wannan karon Maman Farida ba tsakar gidan, hakan yasa ni jindadin wucewa na shigewa inda Nana ta ke na mika mata ledar sannan na fito da dauki kofi biyu da ruwa na koma dakin, ita na fara hadawa da ruwan sanye sannan ni kuma na hada nawa garin na saka suga na sha, yadda take fisgar biredin tana sai ka rantse da Allah ta shekara bata ci abinci ba. Tausayinta ne ya lullube, an cire mata koda daya dan zalinci, ga yunwa tana fama da ita babu mai bata sai Allah, dan ya tafi ya barta a garin nema yafiyarta. Tabbas ba zan taba manta Doc Asim ba, ba kuma zan taba yafe masa ba, sanadinsa na kwana a cell, na rasa kanena, ga mahaifiyata a halin da ba zan iya juye ganinta a haka ba.
Idan zan yi tunani sai na rasa da wanne zan fara abubuwan duniya sun taru sun min tsaye a raina, har wani zafi na ke jin kirjina yana yi idan ina tunani, na rika jin zuciyata kamar zata fasa kirjina ta fito.
Bayan mun gama na dauki kofunan na kai waje na wanke na aje mata a inda na gansu, ashe ta hangi lokacin da na aje sai ganinta nai ta fito rai a bace tana ta masifa wai mun taba mata kofi kazamai da mu, a kan idona ta dauki kofunan ta wilgar bayan gidan, na ji zafi sosai amman ban nuna mata ba, domin fadanta akan gaskiya ne, ni na taba mata abu da ban taba ba da bata min wannan maganar ba.
Kitchen da muka raba na koma na dauko duka kayan wanke wanken na fito da su tsakar gidan, na je na siyo omo na debo ruwa a rijiyar gidan na zauna na wake su tas, na dauka na kai kitchen din wanda zan iya cewa dakinmu. Sannan na fito rike da soson wankanmu na dibi ruwan a robarmu na shiga bandakin tsakar gidan nai wanka, na wanka jiki sau uku sannan na saka ruwa na dauraye na fito fes da ni ni kaina har wata ni'ima na ke jin tana shiga jikina. Ban ssmu na shafa mai ba saboda yanayin garin da zafi, sai kawai na saka daya daga cikin tufafin da na ke ji da su, na dauki bakin dankwalina nai nikab da shi sannan na saka Hijab sama na duka inda kudin sukd na dauki naira dari na dan hawan acha6a, domin akwai tazara a tsakanin unguwar mu da tasu.
“Nana zan tafi”
“Yau za ki fara aikin?”
“To Allah ya taimaka ya tsare a dawo lafiya”
“Amin, ki aje wannan kudin muna cin abinci da su, idan na samu wasu wadanda suka yarda nai aikin yamma sai na rika zuwa ina musu kin ga idan an ban kudi sai na hada da wannan mu koma asibitin”
“To Allah ya nufa”
Duk maganar da nai mata da hausa nai ta ita kuma sa ta maida min da yaren da tafi kwarewa akai wato buzanci. Sai da nai mata sallama sannan na fita, ban yi nisa sosai na samu mashin na tara na hau yana sauke ni na bashi hansi ya karba ya wuce ni kuma na buga kofar gate din a hankali. Mai gadin ne ya leko yana ganina sai ya fito gaba daya.
“Baiwar Allah lafiya”
“Lafiya kalau, ni ce wacce na zo neman aiki dazu kuma suka ce sun dauke amman sai naje na shirya”
Wani kallo yai min tun daga sama na har kasa, nasan kallon baya rasa nasaba da bakin kyallen da na saka na rufe fuskata, wata kila yana munanamin zato ne.
“Bari dai na fara fada musu tukuna”
Haka ya barni tsaye a gurin ya koma ciki, ba dauki dogon lokaci ba sai gashi ya dawo ya bude min gate din.
“Ance kin shigo”
“Na gode”
Na fada ina saka kafata cikin gidan, sai a yanzu ne nake kara kare masa kallo babban gida ne da za ayi iya kiransa da aljannar duniya, ko a harabar gidan kadai aka barka zaka sha kallo tun daga kan furanni da kuma manyan motocin da ke gidan, ko wace kofa an kawata ta da furanni. A inda na naga sun fito dazun na na bi stairs din na isa gaban katuwar kofar mai kyau na yi knocked a hankali, shiru ban ji an bude kofar ba, hakan yasa na sake knocked, nan ma shiru ba a bude min ba, sai da na yi na ukun sannan aka soma motsa kofar aka bude. Mijin matar ne ya bude min yana sanye da kananan kayan, bakin wando da jar t-shirt, fukarsa kamar ta kullum babu alamar murmushi ma balle kuma ayi zancen dariya.
“Ina wuni”
Be amsa min ba, sai kallon fuskata yake kamar nai son tantace abu, ni kuma nai tsaye a gurin cike da tsawalla, gabana sai faduwa yake ina jin kamar cewa zai yi ya fasa baya so. Sakin kofar yai ya juya ya koma ciki ya barni a gurin tsaye shi be cena shigo ba, kuma be ce min na tafi ba, ganin hakan yasa na yi tsaye agurin kamar an dasani, har sai da na ji muryar matar tana ce min na shigo.
Kamar wata hawainiya haka na rika taka tile din mai tsantsi gudun kar na taba da karfi su ce na musu ba daidai. A kan wata babban kujera suke zaune tun na shigo falon daga ita har shi babau wanda ya kalleni balle ya ce min wani abu. Haka ma zauna a gurin kamar daman sun biyana dan na zo na zauna gabansu ne.
“Ke anya macen kwarai ce? Miyasa kika rufe fuskarki?”
Matar ta fada tana min wani kallon uku saura kwata.
“Ba komai, na fi jindadi idan na rufe fuskar ne shiyasa na rufe, ina da konuwa a fuskar ne”
Ta tabe baki.
“Bedrooms din mu za ki fara shiga ki gyara komai da nan falon sannan ki shiga kitchen ki gyara kuma ki wanke duka kayan da suke can sannan ki yi mopping ki saka mana turaren kanshi”
“To ina dakunan suke?”
Da yatsanta ta nuna inda yake har na mike tsaye sai kuma ya kira ni.
“Keee ban da sata kar ki kuskura daukar mana wani a gida”
“Ban taba sata ba a rayuwa”