Sashe 49
Zaki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Jiya ba ki dawo karbar abincin dare ba, ko da mun fita asibiti amman ni da wuri na dawo saboda Alhaji”
Abubuwa ne suka zo min a rai, zancen Alhaji na san tana da mijin da suke taraiya ita da Mama Fulani domin wani lokacin ina ganin yadda suke kokarin shirya abincin ko wani abunda ya ke nuna mijinsu suke yi ma amman ban taba jin zancensa a bakinsu ba, haka ma a gurin yayansa, ban taba cin karo da shi ba, fitar da shigowarshi duka ban taba gani ba, da wace motar yake fita ko yake shigo cikin gidan ban taba sani ba. Sai kuma zancen zuwa asibiti waye ba lafiya? Kamar ta san abunda na ke sakawa a raina sai na ji ta ce.
“Matar Aliyu ciwon ya tashi Wallahi”
Da sauri na kalleta.
“Miya ke damunta?”
“Wai ciwon koda ne daman tun tana karama haka take har ta girma, to sai daga bayan kododin duka biyu suka lalace, daker aka samu wata aka siya aka saka mata a waje, yanzu kuma wai kodar ta kone, Wallahi ni yarinyar har tausayi take ba ni wannan jarabawar rayuwa”
Wani yanayin na ji, shi ba dadi ba shi kuma na bakinciki ba, a take na girmama Allah a zuciyata lallai sakamakon zalinci ba mai kyau ba ne, koda ta kone abunda ban taba ji ba, sai dai na ji ance ta lalace amman wani iko na Allah yau na ji ance ta kone, lallai Allah ba azzalumin kowa ba ne.
“Lafiya?”
Ta tambaya ashe kallonta nake ta yi tun dazu ni ban ma sani ba. Har na bude baki nai magana sai muka ga an turo kofar falon an shigo, Kamal ne fuskarsa dauke da murmushi yana sanye da uniform din sojoji sun matukar karbarsa abun ka da dogon mutum sai yai kyau da kakin kamar yadda na ganshi a wacan karon. Ledar jiya ce a hannunsa kai tsaye ya nufo inda nake yana gaisawa da Ammy da alama ya saba shigowa gidan, domin ita ma naji tana masa korafin ya daina zuwa kwana biyu kamar yadda Mama Fulani ma na ji tana masa.
“Wallahi aiki ne yai min yawa, yanzu ma kaduna zan je da safen nan sakon kawai zan bawa ba Mamar nan taki”
Kallonsa kawai Ammy take har ya karaso kusa da ni ya mika min ledar.
“Ga kayanki nan”
Tsayawa nai kallon ledar kamar mai shawarar karba, sai ya aje min ita kasa yana kallon agogon hannunsa.
“Zaki bata min lokaci ko? Na shiga can a aka ce kina nan”
Juyawa yai ya nufi kofa yana yi ma Ammy sallama da kallo na bishi har ya fice sannan Ammy ta kalleni tana dariya ta ce
“Ina kika san Kamal?”
“Ranar na fit gate shine ya kira na ce masa nan nake, sai kuma da muka fita da Anty Rukaiya shine ya ce na raka shi mu yi siyayya”
“Ok shine ya kawo miki na ki tsara? Tooo lallai yarinyar nan ashe ko ko zai janyo miki rigimar Maryam, saurayinta ne fa”
Na wara ido.
“Da gaske?”
“Eh yana dan zuwa gurinta can ba a rasa ba, yau kuma ya dawo gurinki? Oh Maza akwai iya son mata”
Ta fada tana dariya ni kuma na nufi inda na dauko turaren na aje sannan na dawo na duka na dauki ledar na fito daga part din na nufo gareji ban tsaya duba komai ba aje kawai nai na dawo part din Mama Fulani dan karasa gyaran kamar yadda na saba, ko da na shiga ita da yayanta suna dinning suna karyawa, fuskar Anty Maryam ta kumbura sosai har gurin idonta daya ya rufe bata iya gani da kyau da shi, wata kila marinta Aliyu yai ta yi ko kuma wani abun ya buga mata a fuska oho, ni dai kallo daya nai mata na dauke kaina na shiga dakunansu na gyara ko'ina na wanke bandakunan sannan saka turare Awwaba na fito na sauko kasa.
“Zo ga abincinki ki dauka”
Ya Muhseen ya fada yana aje min plate din a gefen taburin. Sai da na karasa kusa da shi sannan ya kalleni
“Ya jikinki? Na manta jiya ban saka miki kada ba amman ai baya jini ko?”
“Eh ba ya yi”
Na amsa shi jikina nata rawa domin na lura da yadda Mama Fulani take watsawa Muhseen harara shi kuma be ma gani ba, gaba daya hankalinsa yana gurina, da sauri na karbi abinci naje na zube a plate dina na kawo masa sannan na dawo garejin na zauna ina cin abincin ina duba kayan da ke ledar, kayan da ya siya min ne jaya turare da auduwar mata da man goge baki sai kuma chocolate da biscuit mai madara. Ina jin lokacin da motoci har biyu suka tsaya a harabar gidan, ni dai ban leko ba domin ban damu na san ko suwaye suka zo ba, a cikin jaka ta na saka man goge bakin da sauran kayan biscuit din kuma na aje shi a saman katifa ta da zimmar idan na dawo na ci, sai na dauki plate din da cup na nufi garden dan wankewa, ina cikin wakewa na ji kamshin turaren Aliyu da sauri na waigo sai na ganshi tsaye yana ta kallona cikin yanayin da ke nuna yana cikin tsananin damuwa. Ni ma tsayen nai ina ta jiran na ji idan wani abun zai ce min amman be ce komai ba, ganin hakan yasa na juya na cigaba da wanke plate din sai na ji motsinsa a bayana daf da ni. Mikewa nai tsaye ina kallonsa, sai ya bude ba ki kamar zai yi magana sai kuma ya kasa cewa komai. Daukar plate din nai zan wuce sai ya kira sunana.
“Ataa... ”
Sai na tsaya a tunanina wani abun zai ce na masa, sai kuma yai shiru be ce komai ba ya kawarda fuskarsa yana hade yawu, da alama wasu kalmomin yake hadawa ko kuma yana saka abunda zai ce min ne.
“Matata Rahma bata da lafiya.... ”
Sai kuma yai shiru ya dawo da dubansa a kaina.
“Ataa na san ba a kyauta miki ba am.... ”
“Sai yanzu ka sani? Saboda kodar matarka ta kone ko? So kake a sake cire ta mahaifiya a saka mata?”
Ya girgiza min kai alamar aa.
“So na ke na baki hakuri”
“Kana tunanin Hakuri zai canja zalincin da aka min ne? Kana tunanin hakuri zai saka Rahma ta tashi a take ne? Ko kuma kana tsoro kar matarka ta tafi ta barka ne ka dandana zafin rashi kamar yadda na dandana na rashin dan'uwana saboda kai? Ko tsoron jinya kake kamar yadda nai ta mahaifiyata? Har ka fara tsorata da abunda ya samu matarka tun yanzu? Likitoci sun fada maka zata rayu ko ba zata rayu ba? Ai kana da kudi sai mu gani idan kudinka za su tare mata mutuwa, ko kuma za su sama mata lafiya a take, ko da yake za ku iya neman wani talakan marar gata irina ku cire masa kodar ku saka mata ita ta rayu”
Duk abunda na ke fada masa be ce min komai ba, wani abun mamaki sai ma cika da idonsa sukai da kwalla. Wani mutum ne ya shigo garden din wanda ba zai wuce sa'ar Aliyu ba ya karaso kusa da inda muke tsaye yana ta kallo.
“Ke ce Ataa?”
Na kalleshi
“Wani ya baka labarina ne?”
Sai ya kalli Aliyu ya sake kallona.
“Sunana Nasir ni abokin Aliyu ne kuma Aliyu ya fada min komai akanki, Ataa mun san an zalince amman....”
“Amman me? Amman ba ku gane ba sai yanzu? Ya kasa jure abunda ya same shi ko? Ni na jure jinyar mahaifyarta da kallon halin da take ciki har na tsawon wata daya da wani abu a asibiti, kullum ina ta zullumi zata mutu ko ta rayu? Ban sani ba, yanzu haka mahaifiyata tana can gida na baro ta na zo nan aiki saboda na sama mata kudin magani, wata kila ko da zan koma ta mutu, ko kuma rashin lafiyar ta kara tsanani, tun da na baro garin ban sake jin muryarta sai dai idan na kwanta nai mafarkinta? Saboda abunda mutanen nan suka min, har yau bata san cewa an cire mata koda ba, da wane ido zan kalleta na fada mata? Su wa zan ce suka cire mata? Har yau mahaifiyata bata san gaskiyar ciwonta ba bata san komai a kai ba, kun jefa rayuwata cikin damuwa da bakinciki, amman duk ba ku gane ba sai yanzu da Allah ya jarraba Rahma na dan lokaci, sai ka kasa jurewa? Miye amfanin zuwa da kukai a nan? Na yafe muku? Ko kuma na fada muku Rahma ba Zata mutu ba? Kun cutar da ni Wallahi babu wani dadi bakin da za ku min na yarda da ku, za ku iya cilata ni yin komai saboda ina talaka amman ban da yafiya, ba zan taba yafewa ba.... ”
Na karasa cikin kukan dana fara tun dazu sannan na nufi hanyar fita dGa garden din har bana iya gani da kyau saboda hawayen da suke min zuba.
ZAKI
By Khadeeja Candy
26...
Duk kokarin Kamal na rike ta kar ta kai kasa be saka ya iya taro ta ba har sai da ta kai kasan, be san abunda ya faru ba amman tabbas ya ji karan mari a lokacin da ya kawo bakin kofar falon da zimmar shigowa kawo ma Ataa tsarabarta. Gaba daya falon yai tsif Husnat da Siyama suna ta mamakin zafin rai irin na Fulani, Maryam da Rukaiya kam abun dadi yai musu daman ko su ne za su iya yi mata haka, sai dai suna tsiron kar Aliyu yai musu ba dadi amman idan Mama Fulani ce babu abunda zai yi. Momy ta girgiza kai tana kallon Ataa cike da tausayawa domin ta san ba lallai sai ta yi ma Mama Fulani wani babban abu zata yi mata irin wannan dukan ba, tasan halinta sarai tana da zafin hannu a wajen yayan wasu ban da yayanta, ita kam nata yayan baka isa ko yatsa ka nuna musu ba balle ka ce za ka dake su.
“Mi tai miki kika mata wannan irin marin? Ta suma fa”
Abubuwa ne suka zo min a rai, zancen Alhaji na san tana da mijin da suke taraiya ita da Mama Fulani domin wani lokacin ina ganin yadda suke kokarin shirya abincin ko wani abunda ya ke nuna mijinsu suke yi ma amman ban taba jin zancensa a bakinsu ba, haka ma a gurin yayansa, ban taba cin karo da shi ba, fitar da shigowarshi duka ban taba gani ba, da wace motar yake fita ko yake shigo cikin gidan ban taba sani ba. Sai kuma zancen zuwa asibiti waye ba lafiya? Kamar ta san abunda na ke sakawa a raina sai na ji ta ce.
“Matar Aliyu ciwon ya tashi Wallahi”
Da sauri na kalleta.
“Miya ke damunta?”
“Wai ciwon koda ne daman tun tana karama haka take har ta girma, to sai daga bayan kododin duka biyu suka lalace, daker aka samu wata aka siya aka saka mata a waje, yanzu kuma wai kodar ta kone, Wallahi ni yarinyar har tausayi take ba ni wannan jarabawar rayuwa”
Wani yanayin na ji, shi ba dadi ba shi kuma na bakinciki ba, a take na girmama Allah a zuciyata lallai sakamakon zalinci ba mai kyau ba ne, koda ta kone abunda ban taba ji ba, sai dai na ji ance ta lalace amman wani iko na Allah yau na ji ance ta kone, lallai Allah ba azzalumin kowa ba ne.
“Lafiya?”
Ta tambaya ashe kallonta nake ta yi tun dazu ni ban ma sani ba. Har na bude baki nai magana sai muka ga an turo kofar falon an shigo, Kamal ne fuskarsa dauke da murmushi yana sanye da uniform din sojoji sun matukar karbarsa abun ka da dogon mutum sai yai kyau da kakin kamar yadda na ganshi a wacan karon. Ledar jiya ce a hannunsa kai tsaye ya nufo inda nake yana gaisawa da Ammy da alama ya saba shigowa gidan, domin ita ma naji tana masa korafin ya daina zuwa kwana biyu kamar yadda Mama Fulani ma na ji tana masa.
“Wallahi aiki ne yai min yawa, yanzu ma kaduna zan je da safen nan sakon kawai zan bawa ba Mamar nan taki”
Kallonsa kawai Ammy take har ya karaso kusa da ni ya mika min ledar.
“Ga kayanki nan”
Tsayawa nai kallon ledar kamar mai shawarar karba, sai ya aje min ita kasa yana kallon agogon hannunsa.
“Zaki bata min lokaci ko? Na shiga can a aka ce kina nan”
Juyawa yai ya nufi kofa yana yi ma Ammy sallama da kallo na bishi har ya fice sannan Ammy ta kalleni tana dariya ta ce
“Ina kika san Kamal?”
“Ranar na fit gate shine ya kira na ce masa nan nake, sai kuma da muka fita da Anty Rukaiya shine ya ce na raka shi mu yi siyayya”
“Ok shine ya kawo miki na ki tsara? Tooo lallai yarinyar nan ashe ko ko zai janyo miki rigimar Maryam, saurayinta ne fa”
Na wara ido.
“Da gaske?”
“Eh yana dan zuwa gurinta can ba a rasa ba, yau kuma ya dawo gurinki? Oh Maza akwai iya son mata”
Ta fada tana dariya ni kuma na nufi inda na dauko turaren na aje sannan na dawo na duka na dauki ledar na fito daga part din na nufo gareji ban tsaya duba komai ba aje kawai nai na dawo part din Mama Fulani dan karasa gyaran kamar yadda na saba, ko da na shiga ita da yayanta suna dinning suna karyawa, fuskar Anty Maryam ta kumbura sosai har gurin idonta daya ya rufe bata iya gani da kyau da shi, wata kila marinta Aliyu yai ta yi ko kuma wani abun ya buga mata a fuska oho, ni dai kallo daya nai mata na dauke kaina na shiga dakunansu na gyara ko'ina na wanke bandakunan sannan saka turare Awwaba na fito na sauko kasa.
“Zo ga abincinki ki dauka”
Ya Muhseen ya fada yana aje min plate din a gefen taburin. Sai da na karasa kusa da shi sannan ya kalleni
“Ya jikinki? Na manta jiya ban saka miki kada ba amman ai baya jini ko?”
“Eh ba ya yi”
Na amsa shi jikina nata rawa domin na lura da yadda Mama Fulani take watsawa Muhseen harara shi kuma be ma gani ba, gaba daya hankalinsa yana gurina, da sauri na karbi abinci naje na zube a plate dina na kawo masa sannan na dawo garejin na zauna ina cin abincin ina duba kayan da ke ledar, kayan da ya siya min ne jaya turare da auduwar mata da man goge baki sai kuma chocolate da biscuit mai madara. Ina jin lokacin da motoci har biyu suka tsaya a harabar gidan, ni dai ban leko ba domin ban damu na san ko suwaye suka zo ba, a cikin jaka ta na saka man goge bakin da sauran kayan biscuit din kuma na aje shi a saman katifa ta da zimmar idan na dawo na ci, sai na dauki plate din da cup na nufi garden dan wankewa, ina cikin wakewa na ji kamshin turaren Aliyu da sauri na waigo sai na ganshi tsaye yana ta kallona cikin yanayin da ke nuna yana cikin tsananin damuwa. Ni ma tsayen nai ina ta jiran na ji idan wani abun zai ce min amman be ce komai ba, ganin hakan yasa na juya na cigaba da wanke plate din sai na ji motsinsa a bayana daf da ni. Mikewa nai tsaye ina kallonsa, sai ya bude ba ki kamar zai yi magana sai kuma ya kasa cewa komai. Daukar plate din nai zan wuce sai ya kira sunana.
“Ataa... ”
Sai na tsaya a tunanina wani abun zai ce na masa, sai kuma yai shiru be ce komai ba ya kawarda fuskarsa yana hade yawu, da alama wasu kalmomin yake hadawa ko kuma yana saka abunda zai ce min ne.
“Matata Rahma bata da lafiya.... ”
Sai kuma yai shiru ya dawo da dubansa a kaina.
“Ataa na san ba a kyauta miki ba am.... ”
“Sai yanzu ka sani? Saboda kodar matarka ta kone ko? So kake a sake cire ta mahaifiya a saka mata?”
Ya girgiza min kai alamar aa.
“So na ke na baki hakuri”
“Kana tunanin Hakuri zai canja zalincin da aka min ne? Kana tunanin hakuri zai saka Rahma ta tashi a take ne? Ko kuma kana tsoro kar matarka ta tafi ta barka ne ka dandana zafin rashi kamar yadda na dandana na rashin dan'uwana saboda kai? Ko tsoron jinya kake kamar yadda nai ta mahaifiyata? Har ka fara tsorata da abunda ya samu matarka tun yanzu? Likitoci sun fada maka zata rayu ko ba zata rayu ba? Ai kana da kudi sai mu gani idan kudinka za su tare mata mutuwa, ko kuma za su sama mata lafiya a take, ko da yake za ku iya neman wani talakan marar gata irina ku cire masa kodar ku saka mata ita ta rayu”
Duk abunda na ke fada masa be ce min komai ba, wani abun mamaki sai ma cika da idonsa sukai da kwalla. Wani mutum ne ya shigo garden din wanda ba zai wuce sa'ar Aliyu ba ya karaso kusa da inda muke tsaye yana ta kallo.
“Ke ce Ataa?”
Na kalleshi
“Wani ya baka labarina ne?”
Sai ya kalli Aliyu ya sake kallona.
“Sunana Nasir ni abokin Aliyu ne kuma Aliyu ya fada min komai akanki, Ataa mun san an zalince amman....”
“Amman me? Amman ba ku gane ba sai yanzu? Ya kasa jure abunda ya same shi ko? Ni na jure jinyar mahaifyarta da kallon halin da take ciki har na tsawon wata daya da wani abu a asibiti, kullum ina ta zullumi zata mutu ko ta rayu? Ban sani ba, yanzu haka mahaifiyata tana can gida na baro ta na zo nan aiki saboda na sama mata kudin magani, wata kila ko da zan koma ta mutu, ko kuma rashin lafiyar ta kara tsanani, tun da na baro garin ban sake jin muryarta sai dai idan na kwanta nai mafarkinta? Saboda abunda mutanen nan suka min, har yau bata san cewa an cire mata koda ba, da wane ido zan kalleta na fada mata? Su wa zan ce suka cire mata? Har yau mahaifiyata bata san gaskiyar ciwonta ba bata san komai a kai ba, kun jefa rayuwata cikin damuwa da bakinciki, amman duk ba ku gane ba sai yanzu da Allah ya jarraba Rahma na dan lokaci, sai ka kasa jurewa? Miye amfanin zuwa da kukai a nan? Na yafe muku? Ko kuma na fada muku Rahma ba Zata mutu ba? Kun cutar da ni Wallahi babu wani dadi bakin da za ku min na yarda da ku, za ku iya cilata ni yin komai saboda ina talaka amman ban da yafiya, ba zan taba yafewa ba.... ”
Na karasa cikin kukan dana fara tun dazu sannan na nufi hanyar fita dGa garden din har bana iya gani da kyau saboda hawayen da suke min zuba.
ZAKI
By Khadeeja Candy
26...
Duk kokarin Kamal na rike ta kar ta kai kasa be saka ya iya taro ta ba har sai da ta kai kasan, be san abunda ya faru ba amman tabbas ya ji karan mari a lokacin da ya kawo bakin kofar falon da zimmar shigowa kawo ma Ataa tsarabarta. Gaba daya falon yai tsif Husnat da Siyama suna ta mamakin zafin rai irin na Fulani, Maryam da Rukaiya kam abun dadi yai musu daman ko su ne za su iya yi mata haka, sai dai suna tsiron kar Aliyu yai musu ba dadi amman idan Mama Fulani ce babu abunda zai yi. Momy ta girgiza kai tana kallon Ataa cike da tausayawa domin ta san ba lallai sai ta yi ma Mama Fulani wani babban abu zata yi mata irin wannan dukan ba, tasan halinta sarai tana da zafin hannu a wajen yayan wasu ban da yayanta, ita kam nata yayan baka isa ko yatsa ka nuna musu ba balle ka ce za ka dake su.
“Mi tai miki kika mata wannan irin marin? Ta suma fa”