Sashe 92
Zaki Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Yankin Agadez shi ne ya fi kowanne yanki girma a Nijar, yankin Agadez ya hada da hamadar Tenere da Bilma da kuma yankin Air mai cike da tsaunuka. Mafi yawancin jama'ar yankin Abzinawa ne, akwai kuma Tubawa da Fulani da kuma Hausawa, mahaifina shine sarkin Agadaz, babban sarki ne mai tari dukiya da kaddarori da mu kan mu yayansa ba za mu iya fayyace ta a lokaci daya ba, mu goma shar tara mahaifinmu ya haifa a dakinmu mu bakwai ne, mahaifiyarmu ita ce uwargida, bayan ita yana da mata biyu, amman ni kadai Allah ya ba shi mace duka sauran maza ne, na taso a cikin wani irin gata marar misaltuwa, kasancewa ta mace sai ya zama ta ko wane bangare ina samun kulawa, bangaren Mai martaba ba, yayyuna maza har ma da kanena maza idan wani abun burgewa na mata suka gani sai su siyo min, domin ni ban san taso a gidanmu na san wani wai kiyaya ki yan ubanci ba, dukanmu idan ka ganmu zaka dauka uwa ta haife mu, boyona ake bana fita ko'ina sai idan makaranta ne ko wani muhimmin abu, karatun addinin ma malami aka samo a gida yake koya mana komai, a lokacin da na gama karatu matakin na biyu, sai mahaifina ya kai ni faransa domin ci gaba da karatuna, a lokacin ban iya komai ba sai faransanci da buzanci a wacan lokacin, ina dawowa a duk lokacin da hutu ya samu sai dai na kan yi watanni kamin na dawo gida, a wata dawowa da nai sai na samu masarautar mu ta yi sabin gyare gyare cikin har da daukar sababin ma'aikata mahaifinki na daga cikin ma'aikatan da aka dauka, ranar da na sauka masarautar mu mahaifinki ne ya bude min mota”
Ta yi shiru na wani lokaci sanna ta cigaba.
“Yana kyau sosai kamar ki, tun a farkon ganin da nai masa na ni ya kwanta min a rai, duk kuwa da kasancewar ban san soyayya ba, saboda mahaifina baya bari wani namjin ya rabe, saboda mazan gidan ma ma zabin mata ake musu balle kuma mata, amman a lokacin da na ga mahaifinki sai ya shiga raina sosai na kamu da son shi, ba kasafai na ke fitowa a harabar masarautar mu ba, amman zuwan mahaifinki sai na fito na zauna nai ta kallonsa ko kuma na kuma na rika lekensa, ina yin duk wani abu da zai kusantar da ni a gareshi, idan lokacin zuwansa yai be zo na duk sai na bi na damu, har wata na shirya fita ta musamman zuwa gidan gonar Mai Martaba da sunan shakatawa, ni da kaina na zabi wadanda za su raka ni, a ciki na za bi mahaifinki, mutumen ne mai far'a da son mutane, sai dai yana tsoron ko da kallona yai kasacewata yar saurata, sai dai na yi da jansa a jikina ina nuna masa kauna, ya labarta min yan'uwana da kowa na sa da ke garin Agadez, wasa wasa kauna ta shiga tsakaminmu amman a boye bana bari a sani, ina daf da komawa makaranta Mai martaba ya gabatar min da wani dan aminsa atsayin mijin da zan aura idan na kammala karatuna, a lokacin ne na juyawa Mai martaba baya na fada masa kai tsaye cewar mahaifinki ne so, a lokacin ne mai martaba ya cilasta ni kula dan aminsa, mahaifinki kuma aka koreshi daga masarautar, babu yadda mahaifiyata ba tai ba dan ta fahimtar ta shi amman ya ki fahimta, aka cilasta min komawa makaranta a cikin wannan yanayin, na shiga damuwa matuka ina jin cewar da zarar na sakw dawowa a garin mai martaba zai aura min wani ne dabam na ummaruje ba, daga makarantar na dawo nijar ba tare da sanin mai martaba ba, na sauka a wani hotel na chanja shigata nai shigar da ba za a taba iya gane ni ba, na je da kaina har cikin gidan su Ummaruje, tsoro sai ya kama mahaifiyarsa da mahaifinsa da dukan yan gidan kasacewar gidan yawa ne, suna ganin cewar idan mai martaba ya san na zo nan zai iya fusace yai musu wani abun, ni na fada masa durina na guduwa, kuma ya yarda saboda so na sosai daga Agadez muka yi doso gurin wasu yan'uwansa, suma suna ya jin tsoro daker muka samu suka yarda aka daura mana aure a sirrance, sai labarin neman Ummaruje ya fara karade nijar, muka sake guduwa da dan abunda yake hannuna muka dawo kamba, da kudin hannuna muka kama haya, mahaifinki kuma hai shago kofar gida, kuma sai Allah yasa albarka abun ya karbu, sai da na shekara biyar a kamba sannan na haife ki, daga nan sai mutane suka fara tambayar dangina, ganin kowa be zo sunanki ba daga dangin mijina har nawa, daga haka muka fara jin mutane umguwa na zancen wai ni yar sarki ce, sai zaman ya gagare mu a nan saboda tsoro da fargaban abunda zai biyo baya, muna ta ganin kamar Mai martaba zai iya aikowa nemana ko kuma ya saka a kama Ummaruje, ya siyarda komai nasa kudin hayar mu kuma muka barsu nan muka koma argungu, zaman a can be karbe mu ba saboda sanar'a shagon da mahaifinki ya fara yi sai ta soma komawa shiririta, sai muka bar yankin gaba daya muka shiga bodinga, a lokacin ne mahaifinki ya fara sana'ar tura ruwa yana siyarwa, sai dai zaman kaune babu dadi saboda ban saba ba, tun ina jin kunyar na je na yi itace shi kuma ya fita siyar da ruwa har ya zame min jiki, sai na kwana biyu uku ban yi wanka ba, wasa wasa har nai sati kuma babu wanda ya kula ko ya damu da hakan, a hakan ma har na ke ganin na fi wasu tsafta, daga bodinga mahaifina ya rika shigowa cikin sokoto yana haduwa da wasu fulani da kuma buzaye, idan ya dawo sai ya rika ba ni labarin sokoto ita dai kamar kamba tana da tarin yan nijar da yawa a ciki, ya fada min cewar akwai da yawa a cikin fulani da buzaye da suke rabawa a irin gidajen da ba a gama gina ba su zauna, sai nai sha'awar mu yi haka saboda ina son na dawo sokoto da zama daga haka muka tattara muka dawo sokoto, a talatar mafara muka fara sauka, a nan muka fara fakewa a wani tsohon gidan da ba a kare ba, ya cigaba sana'ar siyarda ruwansa, ni kuma ina kulla gida ina siyarwa, kwata kwata na koma kamar ba yar saurata ba, kalar fatata ta canja wahala ta rufe ni ga kuma cikin Lukman da na samu a wannan lokacin, ya sani laulayi har na haife shi, mijina yana nuna min kauna sosai yana kula da ni iya gwargwado, bama cikin matsalar komai domin yana kokarin kawo wa mu ci, har kuka girma ya sakaki a makaranta sai dai yana rasuwa komai ya canja mana Ataa kin sani.... ”
Kuka take kamar yadda nima na ke kukan, hakika na sani na san lokacin lokacin da mahaifina yai bankwana da duniya ba tare da ciwon komai ba a cikin gida muna fira da shi sai kawai muka ji yayi shiru ya risina daga zaunen da yake muka jijjiga shi shiru Nana ta kira sunanshi ta zuba masa ruwa amman shikenan mai kasacewa ta kasance, bayan mutuwarsa muka muka siyar da baronsa da duk wani abu na sa muka bar unguwarsa zuwa gidadawa a nan muka kafa bukkarmu kamar yadda muka ga Baba yayi, muka zauna a gurin har zuwa lokacin da masu gidan suka bukaci abunsu, muka sake tashi, da haka mukai ta yawo zama guri guri Nana kuma na fita tai mana bara ta kawo kudin mu siya abinci, har muka fara zuwa tare da ita da muka tara mai yawa sai ta saka ni a makarantar Yakubu mu'azu ni na fara zuwa lukman kuma ya hakura sai gaba, kudin tsintsiya da kudin pta suka hana ni komawa makarantar sai na cigaba da ya islamiyar ita ma ina haruffa na daina zuwa saboda baran ya shiga kaina na, kuma wani lokacin da yunwa na ke zuwa na dawo, karatun ma sai ya daina zama a kana ya zama bana gane komai, Nana kuma bata damu ba saboda bara kawai ta saka a gaba.
Da haka har karatun ya gagareni na daina zuwa gaba daya, sai Lukman da ke zuwa shi ma jefe jefi.
Mahaifina yana son mu daga ni har Lukman da kuma Nana, na sani a dan zaman da nai da shi na rayuwar da na samu tare da shi ya nuna mana kauna, a kullum burinsa ya zai inganta rayuwarmu da ta Nana, yana yawan fada min cewar dadi na nan zuwa ko ba shi da rai za mu jidadi ni da Nana da Lukman, shi ya tafi Lukman ma ya tafi ni da Nana kawai muka rage.
Ta yi shiru na wani lokaci sanna ta cigaba.
“Yana kyau sosai kamar ki, tun a farkon ganin da nai masa na ni ya kwanta min a rai, duk kuwa da kasancewar ban san soyayya ba, saboda mahaifina baya bari wani namjin ya rabe, saboda mazan gidan ma ma zabin mata ake musu balle kuma mata, amman a lokacin da na ga mahaifinki sai ya shiga raina sosai na kamu da son shi, ba kasafai na ke fitowa a harabar masarautar mu ba, amman zuwan mahaifinki sai na fito na zauna nai ta kallonsa ko kuma na kuma na rika lekensa, ina yin duk wani abu da zai kusantar da ni a gareshi, idan lokacin zuwansa yai be zo na duk sai na bi na damu, har wata na shirya fita ta musamman zuwa gidan gonar Mai Martaba da sunan shakatawa, ni da kaina na zabi wadanda za su raka ni, a ciki na za bi mahaifinki, mutumen ne mai far'a da son mutane, sai dai yana tsoron ko da kallona yai kasacewata yar saurata, sai dai na yi da jansa a jikina ina nuna masa kauna, ya labarta min yan'uwana da kowa na sa da ke garin Agadez, wasa wasa kauna ta shiga tsakaminmu amman a boye bana bari a sani, ina daf da komawa makaranta Mai martaba ya gabatar min da wani dan aminsa atsayin mijin da zan aura idan na kammala karatuna, a lokacin ne na juyawa Mai martaba baya na fada masa kai tsaye cewar mahaifinki ne so, a lokacin ne mai martaba ya cilasta ni kula dan aminsa, mahaifinki kuma aka koreshi daga masarautar, babu yadda mahaifiyata ba tai ba dan ta fahimtar ta shi amman ya ki fahimta, aka cilasta min komawa makaranta a cikin wannan yanayin, na shiga damuwa matuka ina jin cewar da zarar na sakw dawowa a garin mai martaba zai aura min wani ne dabam na ummaruje ba, daga makarantar na dawo nijar ba tare da sanin mai martaba ba, na sauka a wani hotel na chanja shigata nai shigar da ba za a taba iya gane ni ba, na je da kaina har cikin gidan su Ummaruje, tsoro sai ya kama mahaifiyarsa da mahaifinsa da dukan yan gidan kasacewar gidan yawa ne, suna ganin cewar idan mai martaba ya san na zo nan zai iya fusace yai musu wani abun, ni na fada masa durina na guduwa, kuma ya yarda saboda so na sosai daga Agadez muka yi doso gurin wasu yan'uwansa, suma suna ya jin tsoro daker muka samu suka yarda aka daura mana aure a sirrance, sai labarin neman Ummaruje ya fara karade nijar, muka sake guduwa da dan abunda yake hannuna muka dawo kamba, da kudin hannuna muka kama haya, mahaifinki kuma hai shago kofar gida, kuma sai Allah yasa albarka abun ya karbu, sai da na shekara biyar a kamba sannan na haife ki, daga nan sai mutane suka fara tambayar dangina, ganin kowa be zo sunanki ba daga dangin mijina har nawa, daga haka muka fara jin mutane umguwa na zancen wai ni yar sarki ce, sai zaman ya gagare mu a nan saboda tsoro da fargaban abunda zai biyo baya, muna ta ganin kamar Mai martaba zai iya aikowa nemana ko kuma ya saka a kama Ummaruje, ya siyarda komai nasa kudin hayar mu kuma muka barsu nan muka koma argungu, zaman a can be karbe mu ba saboda sanar'a shagon da mahaifinki ya fara yi sai ta soma komawa shiririta, sai muka bar yankin gaba daya muka shiga bodinga, a lokacin ne mahaifinki ya fara sana'ar tura ruwa yana siyarwa, sai dai zaman kaune babu dadi saboda ban saba ba, tun ina jin kunyar na je na yi itace shi kuma ya fita siyar da ruwa har ya zame min jiki, sai na kwana biyu uku ban yi wanka ba, wasa wasa har nai sati kuma babu wanda ya kula ko ya damu da hakan, a hakan ma har na ke ganin na fi wasu tsafta, daga bodinga mahaifina ya rika shigowa cikin sokoto yana haduwa da wasu fulani da kuma buzaye, idan ya dawo sai ya rika ba ni labarin sokoto ita dai kamar kamba tana da tarin yan nijar da yawa a ciki, ya fada min cewar akwai da yawa a cikin fulani da buzaye da suke rabawa a irin gidajen da ba a gama gina ba su zauna, sai nai sha'awar mu yi haka saboda ina son na dawo sokoto da zama daga haka muka tattara muka dawo sokoto, a talatar mafara muka fara sauka, a nan muka fara fakewa a wani tsohon gidan da ba a kare ba, ya cigaba sana'ar siyarda ruwansa, ni kuma ina kulla gida ina siyarwa, kwata kwata na koma kamar ba yar saurata ba, kalar fatata ta canja wahala ta rufe ni ga kuma cikin Lukman da na samu a wannan lokacin, ya sani laulayi har na haife shi, mijina yana nuna min kauna sosai yana kula da ni iya gwargwado, bama cikin matsalar komai domin yana kokarin kawo wa mu ci, har kuka girma ya sakaki a makaranta sai dai yana rasuwa komai ya canja mana Ataa kin sani.... ”
Kuka take kamar yadda nima na ke kukan, hakika na sani na san lokacin lokacin da mahaifina yai bankwana da duniya ba tare da ciwon komai ba a cikin gida muna fira da shi sai kawai muka ji yayi shiru ya risina daga zaunen da yake muka jijjiga shi shiru Nana ta kira sunanshi ta zuba masa ruwa amman shikenan mai kasacewa ta kasance, bayan mutuwarsa muka muka siyar da baronsa da duk wani abu na sa muka bar unguwarsa zuwa gidadawa a nan muka kafa bukkarmu kamar yadda muka ga Baba yayi, muka zauna a gurin har zuwa lokacin da masu gidan suka bukaci abunsu, muka sake tashi, da haka mukai ta yawo zama guri guri Nana kuma na fita tai mana bara ta kawo kudin mu siya abinci, har muka fara zuwa tare da ita da muka tara mai yawa sai ta saka ni a makarantar Yakubu mu'azu ni na fara zuwa lukman kuma ya hakura sai gaba, kudin tsintsiya da kudin pta suka hana ni komawa makarantar sai na cigaba da ya islamiyar ita ma ina haruffa na daina zuwa saboda baran ya shiga kaina na, kuma wani lokacin da yunwa na ke zuwa na dawo, karatun ma sai ya daina zama a kana ya zama bana gane komai, Nana kuma bata damu ba saboda bara kawai ta saka a gaba.
Da haka har karatun ya gagareni na daina zuwa gaba daya, sai Lukman da ke zuwa shi ma jefe jefi.
Mahaifina yana son mu daga ni har Lukman da kuma Nana, na sani a dan zaman da nai da shi na rayuwar da na samu tare da shi ya nuna mana kauna, a kullum burinsa ya zai inganta rayuwarmu da ta Nana, yana yawan fada min cewar dadi na nan zuwa ko ba shi da rai za mu jidadi ni da Nana da Lukman, shi ya tafi Lukman ma ya tafi ni da Nana kawai muka rage.