Sashe 16
Zaki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Shine abunda ya iya fada cikin kuka, sai daya daga cikin mutanen da ke tsaye ya zo ya dauke shi ya saka a mota wanda na ke kyautata zaton shi ya kade shi. Gidan baya ya bude min na shiga gurin da Lukman yake sannan ya bude mazaunin direba ya zauna na fisgi motar muka doshi specialist hospital wato asibitin daji. Muka isa aka wuce da shi layin yan hadari ni kuma na bi bayansu hankalina a tashe, sai da suka fada min cewar na je na karbo kati na tuna da kudin da suke hannu, ba ko tantama sun fadi tun a lokacin da hadarin ya afku, da sauri na fita emergency din zuwa neman mutumen ko zan ganshi ya taimaka min, sai na nemesa na rasa, wata kila shi kuma ya tafiyarsa. Komawa nai ciki ina rokonsu su taimaka su kula da shi kamin na kawo kudi sai suka ce min wai sai na zo da police za su iya taba shi, haka suka kyale Lukman a wulakance cikin gurin da duban mutane suke sai ihu yake. Ji nai kamar na je na dauke shi nai tafiyata idan kuma na dauke shi ban san inda zan kai shi ba, ba ni da wani magani da zan iya masa.
Tasowa nai na fito daga cikin gurin ina tafiya hawaye masu zafi suna sauko min, yanzu yan kudin da suka rage min da kuma wadanda mukai bara muka samu na zubar saboda kidima, ga shi Lukman ya bugu da mota ga Nana tana asibiti tana jiran na kawo kudin maganin da hoto. Wani abu na ji ya tsaya min a zuciya yana neman numfashina, a take tsayuwa ta gagareni, ba zan iya fadar inda na ke ba, iyakar abunda na sani na ji na zauna saman wani abu mai kamar kaya, sai kuma duhu ya rufe min ido har na soma jin kamar babu sauran numfashi a tare da ni.
Ban san iya awanin ko mintuna dana dauka a gurin ba, kamar wacce aka sakowa numfashi daga sama haka na farka firgigit ina maida numfashin wahala, baren kaina na ji yana min ciwo, gurin da na ke zaune sai sukana ake, hakan yasa na unkura na tashi tsaye sai na lura ashe saman fulawoyin na ke zaune masu kaya, da na soma tafiya sai na ji jiri na ďibata idanuwana kuma suna ta lumshewa kamar mai jin bachi. Haka na fito bakin gate din asibitin ina tafiya kamar marar lafiya, bakin titi na tsaya na tari wani mai Napep yana tare da wata mace a baya, yana tsawa na duka har kasa na hade hannayena ina rokonsa.
“Dan Allah ka taimaka min ba, kanene yai hadari mutumen daya kawo shi asibiti ya gudu ya bar mu, su kuma sun ce baza su duba shi ba sai na kawo police kuma ba ni ko kudin siyen kati”
“Yanzu me kike so?”
Matar da ke baya ta fada tana dage nikab din dake fuskarta.
“So na ke ka taimaka min na dauko shi na saka a ciki na kai shi gida”
“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u, mutane suna ciki hali, ke yanzu kudin Napep din ma ya gagara? Allah ka ba mu karfi da ikon da za mu iya taimakon bayinka marasa shi”
Ta fada tana miko min dubu daya yan dari biyu guda biyar, sannan ya ciro dari biyu ta mikawa mai Napep din.
“Je ka kaita ni zan tari wata na shiga”
“Na gode Allah ya saka miki da alheri”
Tana fita na shiga zauna a ciki mai Napep din ya janyo ta ciki muka shiga har bakin kofar emergency. Da sauri na fita daga napep din na shiga ciki sai na same shi a inda na barshi, sai dai baya motsi babu alamar numfashi a tare da shi.
“Kun kasheshi, kun bar shi nan ba ku taimaka masa ba, ya mutu kun ji dadi”
Shine abunda na fada ina kallon nurses din ina hawaye kamar ba gobe, sannan na duka na saka hannuna biyu na tallabo shi na juyo na fito da shi mai Napep din ya taimaka min ya saka shi a ciki ni kuma na shiga, ina ta shafa fuskarsa ko zai farka amman shiru, can na kai hannuna gurin hancinsa sai na ji babu numfashi ba alamunsa.
Har muka isa Clapperto road kuka kawai na ke ina rike da Lukman, mai Napep din ne ya fito ya saka hannunsa ya dauko shi ya kai shi gurin da na nuna nasa wato cikin kangon gidan nan ya aje min shi sannan na saka hannunsa aljihu ya ciro dari biyar ya miko min.
“Gashi ku kara Allah ya muku mafita”
“Na gode”
Na Fada cikin muryar kuka. Sai ya juya cike da tausayawa ya fice, ni kuma na zauna a gurin ina ta kallon Lukman wai ko zai motsa amman shi, har hannuna na kai na dan matsa gurin kafar inda na ga yana riko dazun ko zai motsa amman shiru. Kaina na daga saman ina hawaye cikin daga murya irin da masu neman dauki nan cikin gaggawa na ce.
“Allah kai ka so haka a garemu, komai ya samemu da saninka ne da yardarka, Allah ka sani ba ni da wata mafita sai ta ka, Allah kana ganin halin da na ke ciki Allah ka kawo min dauki”
Sannan na tashi na je nai alwala nayi Sallah, ban tashi daga gurin ba, sai da na gabatar da sallah la'asar, sannan na mike tsaye ina murza kudin da ke hannuna zuciyata sai wani abu take min babu dadi, da kafa na taka zuwa asibitin uduth wannan karon babu masu gadin dakunan kasancewar la'asar, cike da nauyin kafa na ke taka ward din ina sakesaken abunda zan fadawa Nana, idan ma na boye mata dole zata san gaskiya, idan kuma na fada mata zata iya shiga wani hali sai na kasa za6a tsakanin fada mata da kuma akasin haka.
Kwance na sameta ba kamar dazun da na bar ta jingine ba, ban san hawaye na min zuba ba har sai da ta nuna fuskar tawa.
“Miya saka kike kuka Ataa? Wani abun ya samu Lukman ne?”
Saurin share hawayen nai ina girgiza mata kai.
“Aa babu abunda ya same shi”
“Karki boye min, fada min babu abunda zan iya da lamarin Allah”
“Mota ta kade shi Nana, kuma an kai shi asibiti amman baya motsi na dauko shi na dawo da shi gida, kuma kudin da na samu da ragowar duka sun fadi”
Kamar wacce aka yi ma allurar karfi da kuzari, haka ta tashi zaune kamar ba ita ba.
“Lukman din ya mutu ko?”
“Ban sani ba amman dai baya numfashi kuma yai ta ihu lokacin da aka kade shi ya rike kafarsa yana da kuka sosai”
“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u ”
Ta fada tana mikewa tsaye har mamaki ta bani dan zaka rantse da Allah cewar ba ita ce ke kwance malala dazun ba.
“Mu tafi”
Ta fada tana jan dayan zanen da ke saman gadon ta rufe jikinta. Ni kuma nai saurin rikata n zaunar.
“Ba za su bari mu tafi ba sai mun biya kudin gado Nana, ki zauna zan je samo wasu kudin na biyasu sai mu koma gida”
Zaunawa tai a saman gadon sai ta fashe da wani irin kuka mai taba zuciya. Ni kuma nai saurin fita daga gurin ina sauri kamar zan halde kafafun.
Lokacin da na fito bakin kofar asibitin sai na rasa abunda zan yi, wace hanya zan bi na samu kudi? Baran zan sake komawa ko kuwa sata zanje na yi ko mutuncina zan siyar, idan ma sata zan yi ina kudin suke da har zan sata? Ina mai siyen mutuncin yake da har zai siya, a nawa zai siya, mi zai biyo bayan wannan?
Wani tunanin ya zo min, da sauri ma tari Napep na shiga na ce ya kaini ofishin yan sanda, yana tafe gabana na faduwa abunda da wacce ba ta saba ba, musamman a lokacin dana sauka daga Napep din na doshi cikin ofishin, sai bugun gabana ya karu ina jin kamar ba zan iya ba, ganin irin manyan bingogin da suke rike da su. A haka dai na daure na shiga gurin ina sallama muryata na rawa kamar mai jin sanyi.
“As..sa.. La.mu...Alai..kum.”
Mutum biyu suka amsa min, sauran kuma suna ta kula da wasu mutane da ke kusa da su suna musu wani complain din dabam.
“Wa kike nema?”
Wani mai babban muryar ya tambaya yana kallon yanayina.
“Karar wani likita na kawo”
“Likita kuma? Me yai miki?”
“Kodar mahaifiyata ya cire, ba tare da saninmu ba, kuma ni ban ce ya cire mata ba”
Na fada ina kuka. Sai daya daga cikinsu ya zaro ido.
“What...?”
Sai dayan ya ce.
“Koda? Babbar magana, Robot bude nata file ka dauki statement dinta”
A take na zayyana musu komai yadda ya faru cikin har da maganin da ya bani da kuma abinci, sannan na fadi yadda wacan likitan na uduth ya fada min.
“Amman ke ai ba ki da shaida”
“Amman ai hoton ya nuna bata da koda kamar yadda likitan ya fada, kuma ashe ba ayi ma dafin maciji tiyati ni ban sani ba”
Cikin kuka nake wannan maganar ina share majina da Hijab dina.
“Dan Allah ku taimaka min ku kawto min hakkin mahaifiyata, yanzu haka tana asibiti babu kudin jinya sakamakon kodar nan da ya cire mata”
“Kin san inda likitan ya ke?”
“Ban sani ba, amman na san asibitinsa kuma can yake aiki kusan ma can yake zama kullum”
“To yanzu kin san yadda za ayi kina da na mai?”
Na mika masa dubu da dari biyar din da ke hannuna.
“Wannan kudin ne kawai ban sani ba ko za su isa”
Daya daga cikinsu ya karba sannan ya zagayo tare da wasu polisawan uku suka fito daga ofishin, sai da suka janyo motar yan sanda suka ce da ni na zo na shiga na nuna inda yake, cikin kuzari na shiga motar ina ta jindadi da ganin kamar za su kwato min hakkina ne, ashe ban sani ba gwanwo ne zai juye da mujiya.
_______________
Ayi hakuri na yau be kai yawan na kullum ba, gobe zan cika In-Sha-Allah.
https://my.w.tt/PWohUhlPv9.
*Z A K I*
By Khadeeja Candy
1️⃣1️⃣
Tasowa nai na fito daga cikin gurin ina tafiya hawaye masu zafi suna sauko min, yanzu yan kudin da suka rage min da kuma wadanda mukai bara muka samu na zubar saboda kidima, ga shi Lukman ya bugu da mota ga Nana tana asibiti tana jiran na kawo kudin maganin da hoto. Wani abu na ji ya tsaya min a zuciya yana neman numfashina, a take tsayuwa ta gagareni, ba zan iya fadar inda na ke ba, iyakar abunda na sani na ji na zauna saman wani abu mai kamar kaya, sai kuma duhu ya rufe min ido har na soma jin kamar babu sauran numfashi a tare da ni.
Ban san iya awanin ko mintuna dana dauka a gurin ba, kamar wacce aka sakowa numfashi daga sama haka na farka firgigit ina maida numfashin wahala, baren kaina na ji yana min ciwo, gurin da na ke zaune sai sukana ake, hakan yasa na unkura na tashi tsaye sai na lura ashe saman fulawoyin na ke zaune masu kaya, da na soma tafiya sai na ji jiri na ďibata idanuwana kuma suna ta lumshewa kamar mai jin bachi. Haka na fito bakin gate din asibitin ina tafiya kamar marar lafiya, bakin titi na tsaya na tari wani mai Napep yana tare da wata mace a baya, yana tsawa na duka har kasa na hade hannayena ina rokonsa.
“Dan Allah ka taimaka min ba, kanene yai hadari mutumen daya kawo shi asibiti ya gudu ya bar mu, su kuma sun ce baza su duba shi ba sai na kawo police kuma ba ni ko kudin siyen kati”
“Yanzu me kike so?”
Matar da ke baya ta fada tana dage nikab din dake fuskarta.
“So na ke ka taimaka min na dauko shi na saka a ciki na kai shi gida”
“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u, mutane suna ciki hali, ke yanzu kudin Napep din ma ya gagara? Allah ka ba mu karfi da ikon da za mu iya taimakon bayinka marasa shi”
Ta fada tana miko min dubu daya yan dari biyu guda biyar, sannan ya ciro dari biyu ta mikawa mai Napep din.
“Je ka kaita ni zan tari wata na shiga”
“Na gode Allah ya saka miki da alheri”
Tana fita na shiga zauna a ciki mai Napep din ya janyo ta ciki muka shiga har bakin kofar emergency. Da sauri na fita daga napep din na shiga ciki sai na same shi a inda na barshi, sai dai baya motsi babu alamar numfashi a tare da shi.
“Kun kasheshi, kun bar shi nan ba ku taimaka masa ba, ya mutu kun ji dadi”
Shine abunda na fada ina kallon nurses din ina hawaye kamar ba gobe, sannan na duka na saka hannuna biyu na tallabo shi na juyo na fito da shi mai Napep din ya taimaka min ya saka shi a ciki ni kuma na shiga, ina ta shafa fuskarsa ko zai farka amman shiru, can na kai hannuna gurin hancinsa sai na ji babu numfashi ba alamunsa.
Har muka isa Clapperto road kuka kawai na ke ina rike da Lukman, mai Napep din ne ya fito ya saka hannunsa ya dauko shi ya kai shi gurin da na nuna nasa wato cikin kangon gidan nan ya aje min shi sannan na saka hannunsa aljihu ya ciro dari biyar ya miko min.
“Gashi ku kara Allah ya muku mafita”
“Na gode”
Na Fada cikin muryar kuka. Sai ya juya cike da tausayawa ya fice, ni kuma na zauna a gurin ina ta kallon Lukman wai ko zai motsa amman shi, har hannuna na kai na dan matsa gurin kafar inda na ga yana riko dazun ko zai motsa amman shiru. Kaina na daga saman ina hawaye cikin daga murya irin da masu neman dauki nan cikin gaggawa na ce.
“Allah kai ka so haka a garemu, komai ya samemu da saninka ne da yardarka, Allah ka sani ba ni da wata mafita sai ta ka, Allah kana ganin halin da na ke ciki Allah ka kawo min dauki”
Sannan na tashi na je nai alwala nayi Sallah, ban tashi daga gurin ba, sai da na gabatar da sallah la'asar, sannan na mike tsaye ina murza kudin da ke hannuna zuciyata sai wani abu take min babu dadi, da kafa na taka zuwa asibitin uduth wannan karon babu masu gadin dakunan kasancewar la'asar, cike da nauyin kafa na ke taka ward din ina sakesaken abunda zan fadawa Nana, idan ma na boye mata dole zata san gaskiya, idan kuma na fada mata zata iya shiga wani hali sai na kasa za6a tsakanin fada mata da kuma akasin haka.
Kwance na sameta ba kamar dazun da na bar ta jingine ba, ban san hawaye na min zuba ba har sai da ta nuna fuskar tawa.
“Miya saka kike kuka Ataa? Wani abun ya samu Lukman ne?”
Saurin share hawayen nai ina girgiza mata kai.
“Aa babu abunda ya same shi”
“Karki boye min, fada min babu abunda zan iya da lamarin Allah”
“Mota ta kade shi Nana, kuma an kai shi asibiti amman baya motsi na dauko shi na dawo da shi gida, kuma kudin da na samu da ragowar duka sun fadi”
Kamar wacce aka yi ma allurar karfi da kuzari, haka ta tashi zaune kamar ba ita ba.
“Lukman din ya mutu ko?”
“Ban sani ba amman dai baya numfashi kuma yai ta ihu lokacin da aka kade shi ya rike kafarsa yana da kuka sosai”
“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u ”
Ta fada tana mikewa tsaye har mamaki ta bani dan zaka rantse da Allah cewar ba ita ce ke kwance malala dazun ba.
“Mu tafi”
Ta fada tana jan dayan zanen da ke saman gadon ta rufe jikinta. Ni kuma nai saurin rikata n zaunar.
“Ba za su bari mu tafi ba sai mun biya kudin gado Nana, ki zauna zan je samo wasu kudin na biyasu sai mu koma gida”
Zaunawa tai a saman gadon sai ta fashe da wani irin kuka mai taba zuciya. Ni kuma nai saurin fita daga gurin ina sauri kamar zan halde kafafun.
Lokacin da na fito bakin kofar asibitin sai na rasa abunda zan yi, wace hanya zan bi na samu kudi? Baran zan sake komawa ko kuwa sata zanje na yi ko mutuncina zan siyar, idan ma sata zan yi ina kudin suke da har zan sata? Ina mai siyen mutuncin yake da har zai siya, a nawa zai siya, mi zai biyo bayan wannan?
Wani tunanin ya zo min, da sauri ma tari Napep na shiga na ce ya kaini ofishin yan sanda, yana tafe gabana na faduwa abunda da wacce ba ta saba ba, musamman a lokacin dana sauka daga Napep din na doshi cikin ofishin, sai bugun gabana ya karu ina jin kamar ba zan iya ba, ganin irin manyan bingogin da suke rike da su. A haka dai na daure na shiga gurin ina sallama muryata na rawa kamar mai jin sanyi.
“As..sa.. La.mu...Alai..kum.”
Mutum biyu suka amsa min, sauran kuma suna ta kula da wasu mutane da ke kusa da su suna musu wani complain din dabam.
“Wa kike nema?”
Wani mai babban muryar ya tambaya yana kallon yanayina.
“Karar wani likita na kawo”
“Likita kuma? Me yai miki?”
“Kodar mahaifiyata ya cire, ba tare da saninmu ba, kuma ni ban ce ya cire mata ba”
Na fada ina kuka. Sai daya daga cikinsu ya zaro ido.
“What...?”
Sai dayan ya ce.
“Koda? Babbar magana, Robot bude nata file ka dauki statement dinta”
A take na zayyana musu komai yadda ya faru cikin har da maganin da ya bani da kuma abinci, sannan na fadi yadda wacan likitan na uduth ya fada min.
“Amman ke ai ba ki da shaida”
“Amman ai hoton ya nuna bata da koda kamar yadda likitan ya fada, kuma ashe ba ayi ma dafin maciji tiyati ni ban sani ba”
Cikin kuka nake wannan maganar ina share majina da Hijab dina.
“Dan Allah ku taimaka min ku kawto min hakkin mahaifiyata, yanzu haka tana asibiti babu kudin jinya sakamakon kodar nan da ya cire mata”
“Kin san inda likitan ya ke?”
“Ban sani ba, amman na san asibitinsa kuma can yake aiki kusan ma can yake zama kullum”
“To yanzu kin san yadda za ayi kina da na mai?”
Na mika masa dubu da dari biyar din da ke hannuna.
“Wannan kudin ne kawai ban sani ba ko za su isa”
Daya daga cikinsu ya karba sannan ya zagayo tare da wasu polisawan uku suka fito daga ofishin, sai da suka janyo motar yan sanda suka ce da ni na zo na shiga na nuna inda yake, cikin kuzari na shiga motar ina ta jindadi da ganin kamar za su kwato min hakkina ne, ashe ban sani ba gwanwo ne zai juye da mujiya.
_______________
Ayi hakuri na yau be kai yawan na kullum ba, gobe zan cika In-Sha-Allah.
https://my.w.tt/PWohUhlPv9.
*Z A K I*
By Khadeeja Candy
1️⃣1️⃣