Sashe 57
Zaki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kallon kawai yake har ta zagayo ta hau saman gadon ya lullube da bedsheet ta juya masa baya. Mikewa yai shi ma ya kashe wutar dakin ya dawo bayanta ya kwanta ya rumgumeta ta baya, lumshe ido yai ba dan bachi ba sai dan tausayin Ataa daya cika masa zuciya a yanzu ya fi tausayinta fiye da Rahma, sai yanzu yake ji da ma ace Kamal be dawo fa ita ba da Mama Fulani bata koreta ba, wata kila ma ba zata iya gane hanya ba amman an tura zuwa garin be san ina take ba, maybe tai hadari ko ta gadu da wani abun be sani ba. Wannan tunanin ne ya hana shi bachi har asuba, for the first time yau ya kwanta gado daya da Rahma kuma rumgume da ita amman zuciyarsa tana gurin Ataa. Sai da yai sallah asuba sannan ya kwanta dakinsa shi kadai saboda nauyin da idonsa da kansa suke masa wai ko zai samu yin bachin da be yi ba jiya.
*** *** ***
A haka Mama Fulani ta kwana cikin rashin sakewa wanda ya bawa kowa mamaki ciki kuwa har da Momy da bata sake ganin walwalarta ba, gaba daya aka hadu dinning gurin cin abinci har Muhseen amman ban da Mama Fulani da ta gama shirya abinci ta koma dakinta tana karyawar.
“Husna kui yi ku gama mu shirya da wuri kusan 10 jirginmu zai tashi”
Momy ta fada tana mikewa tsaye ta daga dinning din ta koma falo ta zauna tana kiran wayar Aliyu dan ta tambayi jikin matarsa. Muhseen ya kalli Maryam.
“Wai ina Mama?”
“A dakinta take karyawa wai bata jindadi”
“Ataa fa? Yau ba tai shara ba ban ma ta shigo ba, kuma tun jiya da dare na duba ganta a gareji ba ban ga kayanta ba”
“Mama ta maida ita gida”
Muhseen ya kalli Rukaiya da sauri wacce ke bashi amsar.
“Saboda me?”
“Ta gaji da ita, kuma abunda ya faru daman Mama ta ce ba zata kwanar mata a gida ba”
Sai a yanzu ya abunda Aliyu yake tambayar Mama Fulani jiya har take ce masa bata san inda take ba. Jan kujerarsa yai baya ya nufi dakin Mama Fulani. Kishingide ya same ta tana cin fruit tana duba wayarta.
“Mama kin kori Ataa? Mi tai?”
“Ba tai komai ba, na gaji da aikinta kar kuma ka sake min maganar abunda ya shafe ta last warning”
Ta fada masa sannan ta cigaba da abunda take, sai da yai kamar zai sake ce mata wani abu sai kuma yarfar da hannunsa ya juya cikin rashin jindadi ya fice daga dakin.
ALIYU POV.
Be farka sai sha biyu saura na rana, ya dade kwance a saman gadon idonsa biyu yana kallon silin sannan ya unkura ya tashi zaune ya sauko da kafafunsa daga kan gadon, agogon dakin ya fara kallo yana ganin sha biyu ta kusa yai hanzarin mikewa tsaye ya fice daga dakin zuwa dakin Rahma, be same ta a ciki ba sai yar takardar da ta bar masa saman gado.
_Kana bachi bana son na tashe ka, Mommy ta kirani zan je na same ta a gidansu sai mu wuce see you soon_
Yana gama karanta takardar ya cikawa bakinsa iska ya busar cike da rashin jindadin yadda yau Rahma tai masa, be taba damuwa da fita ba tare da ta tambayeshi ba sai yau, yana ganin kamar ta wulakanta shi. Hannu ya kai ya dauki wayarsa da ya bari a dakin jiya sai ya ga miss calls din Momy da Husna da Maryam misalin tara da wani abu na safe kiran wayar yai sai ya ji bata shiga, hakan yasa ya kira wayar Maryam din sai ta shiga.
“Hello Ya Aliyu daman Momy ce ta ce na kira domin ta yi ta kira wayarka bata shiga”
“Ina Momy take?”
“Ta wuce tun ten suka tashi”
Ya kashe wayarsa yana fadin.
“Jirgi daya suka shiga da Rahma kenan”
Fitowa yai daga dakin zuwa dakinsa dan yin wanka ya shirya yaje gurin Mama Fulani, kamin ya shiga dakinsa ya kira wayar Nasir ring uku tai sannan Nasir ya daga.
“Na kira wayarka baka daga ba ya jikin Rahma?”
“Tana hanyar sokoto”
“What ta jin sauki ne ko kuma wani ciwon ne?”
“Sun sallame ta jiya, mahaifiyarta ta ce da ita za su je, and yau bata ma jira na tashi ba kuma bata tashe ni ba suka wuce”
“Kun samu matsala da Rahma ne?”
“Ba wani matsala kawai dai na mata maganar Ataa ne kuma taga laifina, Wallahi Nasir tunanin yarinyar nan hana ni bachi yai, Mama ta koreta tun jiya yanzu ban san halin da take ciki ba”
“Garin ya miya faru?”
Aliyu ya labartawa Nasir abunda ya faru sannan ya dora da.
“Mama ba zata fada min inda zan same ta ba, domin jiya konda na baro gidan ranta a bace yake, amman yanzu ina son ka nema min jirgi zan je sokoto gobe, zan koma gidan nan na sake bincikawa”
“Ko ba ka je da kanka ba za ka iya sakawa ayi maka Aliyu”
“Yeah ina son na je da kaina ko dan Rahma”
“Okay idan an gama komai zan sanar da kai”
Kai ya gyada kamar ance Nasir yana gabansa sannan ya kashe wayar.
Misalin biyu da rabi ya shiga part din Mama Fulani sai ya samu bata nan Baby ce kawai a gidan ita bata dade da dawowa daga scul ba. A saman Sofa ya zauna ya kira Mama Fulani a waya ringing tai sai da ta kusa katsewa sannan ta daga.
“Mama na zo ba ki gida”
“Eh munje gurin kamu ni da su Maryam kuma za mu shopping kamin mu dawo”
“Mama ina son magana da ke”
“Idan na dawo za mu yi”
“Yaushe za ku dawo sai da yamma”
Daga haka kai hanging wayar. Sannan ya nufi kitchen ya hadawa kansa Lipton ya sha ya fito shiga bangaren Ammy, a harabar gidan ya samu Batula tana fira da wani saurayi tana ganinshi ta sha jinin jikinta saurayin kuma ya gaishe shi Aliyu ya amsa mishi ciki ciki sannan ya wuce falon Ammy. Sai da suka gaisa sannan take koro masa da zancen tafiyar Momy.
“Ko da suka wuce ina bachi, Ammy ba ki san gidansu yarinyar nan Ataa ba?”
“Wallahi ban sani ba Aliyu, bata fada min ba nima dazun nake jin zancen tafiyarta gurin Muhseen yana tambaya wai ko na san inda take”
Aliyu yai shiru kamar be ji ba sai kuma ya mike tsaye yana saka hannayensa aljihu dan be son Ammy taja zancen da tsawo.
“Zan leka office”
“To Allah ya tsare”
Ko da ya fito part din Ammy wayarsa na vibration kiran Nasir na shigowa picking yai yana bude motarsa ya shiga.
“Aliyu an samu jirgin da zai tashi da yamma nan zuwa Kebbi idan kana so, daga Kebbi sai ka shiga mota zuwa sokoto, domin gobe babu jirgi sai jibi shi ma kuma da safe zai tashi na san kuma ba son tafiyar safe kake ba”
“Karfe nawa jirgin zai tashi?”
“5 idan kana so sai a siya maka ticket”
“Siya min gani nan zuwa office din ma”
“Okay sai na iso”
Yana kashe wayar ya shiga motarsa ya dauki hanyar kamfaninsu. Be bar kamfanin ba sai da ya rage minti talatin jirginsu ya tashi duk kuma jiran da yai na Mama Fulani ko zata dawo da wuri ne yai magana da ita dan be gane wannan fushin da ta soma yi da shi ba. Amman hakan be samu ba sai dai a waya ya kirata ya fada mata zai je sokoto tai masa Allah ya tsare.
ATAA POV.
Ina ta tunanin samun mafita har garin Allah ya waye, ban samu bachi ba saboda tunani da kuma nishin da Nana take yi. Bayan na gama sallah na dauki kofi naje na siyo mata koko da kosai da suga na saka mata na bata kokon kawai ta sha shima dan ina bata ne, ta ki ta ci kosan ni ma na kasa cin komai. Sai da na tabbatar ta koshi sannan na fito da ita na gyara mata jikinta na sake gyara dakim na saka Hijab dina na nufi titi, Napep na tara na hau na kama hanyar gidansu Rahma, da kudirin da ke zuciyata duk da kasancewar na san bata nan ina son naje ne na bar wa mai gadinsu sako ya fada musu domin na san ba zai rasa number da yake kiransu ba. Bakim gate din gidan Mai Napep ya aje ni na bashi kudinsa sannan na buga gate din mai gadin ya leko ya ganni sai na ga yai murmushi.
“Ahh wannan na manta sunanki ke ce”
“Ni ce”
Na amsa masa cikin damuwa. Sai ya bude min gate din na shiga ciki.
“Dan Allah so na ke ka kira matar gidan nan da mijinta a waya ka fada musu cewar akwai wata koda ta siyar idan suna so, ko kuma ka bani number wayarsu”
Ya daki kirji yana kallona
“Koda?”
“Eh”
“Ina kika samu koda?”
Na yi shiru ban ce masa komai ba.
“Allah yasa ba taki ce ba, kin abunda kike kuwa?”
“Na sani ni dai ka kirasu kawai”
“Sai dai a kira matar a waya amman Alhaji yana nan cikin gidan ai jiya da dare ya dawo”
“Ba suna Abuja ba?”
“Eh shi jiya da dare ya dawo bari na miki sallama da shi”
Ya fada yana nufar cikin gidan. Ni dai ina tsaye kusa da gate din har ya shiga ciki sai na hango Aliyu ya fito sanye da Jallabiya daga can ya tsaya yana kallona kamin ya sauko ya doso inda nake tsaye.
“Za ki siyar da koda?”
Na gyada kai ina matsa yatsun hannuna.
“Waya ce miki muna bukatar koda?”
“Na san ai kodar matarka ta kone, dole wata za ku nema”
“Saboda mi za ki siyar da kodar ki?”
“Saboda na nema ma mahaifiyata lafiya”
“Idan kuma ke kika mutu fa ko kika samu matsala?”
*** *** ***
A haka Mama Fulani ta kwana cikin rashin sakewa wanda ya bawa kowa mamaki ciki kuwa har da Momy da bata sake ganin walwalarta ba, gaba daya aka hadu dinning gurin cin abinci har Muhseen amman ban da Mama Fulani da ta gama shirya abinci ta koma dakinta tana karyawar.
“Husna kui yi ku gama mu shirya da wuri kusan 10 jirginmu zai tashi”
Momy ta fada tana mikewa tsaye ta daga dinning din ta koma falo ta zauna tana kiran wayar Aliyu dan ta tambayi jikin matarsa. Muhseen ya kalli Maryam.
“Wai ina Mama?”
“A dakinta take karyawa wai bata jindadi”
“Ataa fa? Yau ba tai shara ba ban ma ta shigo ba, kuma tun jiya da dare na duba ganta a gareji ba ban ga kayanta ba”
“Mama ta maida ita gida”
Muhseen ya kalli Rukaiya da sauri wacce ke bashi amsar.
“Saboda me?”
“Ta gaji da ita, kuma abunda ya faru daman Mama ta ce ba zata kwanar mata a gida ba”
Sai a yanzu ya abunda Aliyu yake tambayar Mama Fulani jiya har take ce masa bata san inda take ba. Jan kujerarsa yai baya ya nufi dakin Mama Fulani. Kishingide ya same ta tana cin fruit tana duba wayarta.
“Mama kin kori Ataa? Mi tai?”
“Ba tai komai ba, na gaji da aikinta kar kuma ka sake min maganar abunda ya shafe ta last warning”
Ta fada masa sannan ta cigaba da abunda take, sai da yai kamar zai sake ce mata wani abu sai kuma yarfar da hannunsa ya juya cikin rashin jindadi ya fice daga dakin.
ALIYU POV.
Be farka sai sha biyu saura na rana, ya dade kwance a saman gadon idonsa biyu yana kallon silin sannan ya unkura ya tashi zaune ya sauko da kafafunsa daga kan gadon, agogon dakin ya fara kallo yana ganin sha biyu ta kusa yai hanzarin mikewa tsaye ya fice daga dakin zuwa dakin Rahma, be same ta a ciki ba sai yar takardar da ta bar masa saman gado.
_Kana bachi bana son na tashe ka, Mommy ta kirani zan je na same ta a gidansu sai mu wuce see you soon_
Yana gama karanta takardar ya cikawa bakinsa iska ya busar cike da rashin jindadin yadda yau Rahma tai masa, be taba damuwa da fita ba tare da ta tambayeshi ba sai yau, yana ganin kamar ta wulakanta shi. Hannu ya kai ya dauki wayarsa da ya bari a dakin jiya sai ya ga miss calls din Momy da Husna da Maryam misalin tara da wani abu na safe kiran wayar yai sai ya ji bata shiga, hakan yasa ya kira wayar Maryam din sai ta shiga.
“Hello Ya Aliyu daman Momy ce ta ce na kira domin ta yi ta kira wayarka bata shiga”
“Ina Momy take?”
“Ta wuce tun ten suka tashi”
Ya kashe wayarsa yana fadin.
“Jirgi daya suka shiga da Rahma kenan”
Fitowa yai daga dakin zuwa dakinsa dan yin wanka ya shirya yaje gurin Mama Fulani, kamin ya shiga dakinsa ya kira wayar Nasir ring uku tai sannan Nasir ya daga.
“Na kira wayarka baka daga ba ya jikin Rahma?”
“Tana hanyar sokoto”
“What ta jin sauki ne ko kuma wani ciwon ne?”
“Sun sallame ta jiya, mahaifiyarta ta ce da ita za su je, and yau bata ma jira na tashi ba kuma bata tashe ni ba suka wuce”
“Kun samu matsala da Rahma ne?”
“Ba wani matsala kawai dai na mata maganar Ataa ne kuma taga laifina, Wallahi Nasir tunanin yarinyar nan hana ni bachi yai, Mama ta koreta tun jiya yanzu ban san halin da take ciki ba”
“Garin ya miya faru?”
Aliyu ya labartawa Nasir abunda ya faru sannan ya dora da.
“Mama ba zata fada min inda zan same ta ba, domin jiya konda na baro gidan ranta a bace yake, amman yanzu ina son ka nema min jirgi zan je sokoto gobe, zan koma gidan nan na sake bincikawa”
“Ko ba ka je da kanka ba za ka iya sakawa ayi maka Aliyu”
“Yeah ina son na je da kaina ko dan Rahma”
“Okay idan an gama komai zan sanar da kai”
Kai ya gyada kamar ance Nasir yana gabansa sannan ya kashe wayar.
Misalin biyu da rabi ya shiga part din Mama Fulani sai ya samu bata nan Baby ce kawai a gidan ita bata dade da dawowa daga scul ba. A saman Sofa ya zauna ya kira Mama Fulani a waya ringing tai sai da ta kusa katsewa sannan ta daga.
“Mama na zo ba ki gida”
“Eh munje gurin kamu ni da su Maryam kuma za mu shopping kamin mu dawo”
“Mama ina son magana da ke”
“Idan na dawo za mu yi”
“Yaushe za ku dawo sai da yamma”
Daga haka kai hanging wayar. Sannan ya nufi kitchen ya hadawa kansa Lipton ya sha ya fito shiga bangaren Ammy, a harabar gidan ya samu Batula tana fira da wani saurayi tana ganinshi ta sha jinin jikinta saurayin kuma ya gaishe shi Aliyu ya amsa mishi ciki ciki sannan ya wuce falon Ammy. Sai da suka gaisa sannan take koro masa da zancen tafiyar Momy.
“Ko da suka wuce ina bachi, Ammy ba ki san gidansu yarinyar nan Ataa ba?”
“Wallahi ban sani ba Aliyu, bata fada min ba nima dazun nake jin zancen tafiyarta gurin Muhseen yana tambaya wai ko na san inda take”
Aliyu yai shiru kamar be ji ba sai kuma ya mike tsaye yana saka hannayensa aljihu dan be son Ammy taja zancen da tsawo.
“Zan leka office”
“To Allah ya tsare”
Ko da ya fito part din Ammy wayarsa na vibration kiran Nasir na shigowa picking yai yana bude motarsa ya shiga.
“Aliyu an samu jirgin da zai tashi da yamma nan zuwa Kebbi idan kana so, daga Kebbi sai ka shiga mota zuwa sokoto, domin gobe babu jirgi sai jibi shi ma kuma da safe zai tashi na san kuma ba son tafiyar safe kake ba”
“Karfe nawa jirgin zai tashi?”
“5 idan kana so sai a siya maka ticket”
“Siya min gani nan zuwa office din ma”
“Okay sai na iso”
Yana kashe wayar ya shiga motarsa ya dauki hanyar kamfaninsu. Be bar kamfanin ba sai da ya rage minti talatin jirginsu ya tashi duk kuma jiran da yai na Mama Fulani ko zata dawo da wuri ne yai magana da ita dan be gane wannan fushin da ta soma yi da shi ba. Amman hakan be samu ba sai dai a waya ya kirata ya fada mata zai je sokoto tai masa Allah ya tsare.
ATAA POV.
Ina ta tunanin samun mafita har garin Allah ya waye, ban samu bachi ba saboda tunani da kuma nishin da Nana take yi. Bayan na gama sallah na dauki kofi naje na siyo mata koko da kosai da suga na saka mata na bata kokon kawai ta sha shima dan ina bata ne, ta ki ta ci kosan ni ma na kasa cin komai. Sai da na tabbatar ta koshi sannan na fito da ita na gyara mata jikinta na sake gyara dakim na saka Hijab dina na nufi titi, Napep na tara na hau na kama hanyar gidansu Rahma, da kudirin da ke zuciyata duk da kasancewar na san bata nan ina son naje ne na bar wa mai gadinsu sako ya fada musu domin na san ba zai rasa number da yake kiransu ba. Bakim gate din gidan Mai Napep ya aje ni na bashi kudinsa sannan na buga gate din mai gadin ya leko ya ganni sai na ga yai murmushi.
“Ahh wannan na manta sunanki ke ce”
“Ni ce”
Na amsa masa cikin damuwa. Sai ya bude min gate din na shiga ciki.
“Dan Allah so na ke ka kira matar gidan nan da mijinta a waya ka fada musu cewar akwai wata koda ta siyar idan suna so, ko kuma ka bani number wayarsu”
Ya daki kirji yana kallona
“Koda?”
“Eh”
“Ina kika samu koda?”
Na yi shiru ban ce masa komai ba.
“Allah yasa ba taki ce ba, kin abunda kike kuwa?”
“Na sani ni dai ka kirasu kawai”
“Sai dai a kira matar a waya amman Alhaji yana nan cikin gidan ai jiya da dare ya dawo”
“Ba suna Abuja ba?”
“Eh shi jiya da dare ya dawo bari na miki sallama da shi”
Ya fada yana nufar cikin gidan. Ni dai ina tsaye kusa da gate din har ya shiga ciki sai na hango Aliyu ya fito sanye da Jallabiya daga can ya tsaya yana kallona kamin ya sauko ya doso inda nake tsaye.
“Za ki siyar da koda?”
Na gyada kai ina matsa yatsun hannuna.
“Waya ce miki muna bukatar koda?”
“Na san ai kodar matarka ta kone, dole wata za ku nema”
“Saboda mi za ki siyar da kodar ki?”
“Saboda na nema ma mahaifiyata lafiya”
“Idan kuma ke kika mutu fa ko kika samu matsala?”