Sashe 12
Zaki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Na fada ina kallon fuskokinsu na marasa imani da ganinsu irin yan sara sukan nan ne ya turo mana marasa tarbiya. (Area boys)
Aiko kamar jiran suke nai magana sai biyu daga cikinsu suka dauki Nana suka kai ta can kusa da gate suka aje dayan kuma ya turani waje da karfi, Lukman da tsoro tuni na nufi inda Nana take da sauri idonta cike da tsoro, sai kuma suka shiga ciki suka fara shuri da kayan mu da ke ciki sai da suka fitar da komai da kafa sannan suka fito suka nufo inda na ke tsaye ni da Nana muna muka suka ce mana idan muka sake shiga ciki duk suka dawo sai sun sassara mu, kuma mu nemi wani wajen tun kan dare yai mana mu bar gurin kwanon da aka saka dan fara zagayewa kamar za ayi gate.
A gurin muka tsaya ni da Nana da Lukman har aka fara ruwa, daga ni har Nana babu abunda muke sai hawaye Lukman na tsaye yana ta kallon ta bata fuska sosai kamar ya fasa kuka. Sai da naji an fara yayyafi sannan na rika Nana da zimmar mu koma ciki sai ta rike hannuna ta girgiza min ka alamar ba zata koma ba.
“Idan an gama ruwa sai mu fito”
Na fada da muryata ta kuka, sai ta girgiza min kai alamar ba zata ba, hakan yasa na nufi kayanmu na dauko bargon da likitan ya siya dan mu rika kwantawa ni da Lukman akai na lulluba mata na shiga ciki Lukman ma shigo muka fake a ciki ruwa na dukan kanmu. Wani abun Allah kuma sai akai ruwan da kama da bakin kwaya ga sanyi sosai domin har da kankanra suke. A take Nana ta fara tari jikinta na ta karkarwa jin hakan yasa nai saurin bude bargon sai na ga jini duk ya bata mata baki har ya sauko saman rigarta ashe tarin da take jini take fitarwa, rumgume ta nai na fashe da kuka ina daga kaina ina kallon ruwan saman da ke saukowa kamar a cikinsu wani zai kawo mana dauki....
Wayyo Nana 😪
https://my.w.tt/PWohUhlPv9.
*Z A K I*
By Khadeeja Candy
8️⃣
Sai da ruwan suka dan tsagaita sannan na samu damar mikewa tsaye ina daga Nana daga jikina. Ta galabaita sosai har wani lumshe ido take tana budewa amman wani abun mamaki idan ta kalleni sai tai min murmushi, wata kila so take ta kwantar min da hankali ganin irin yadda na ke ta kuka kamar ba gobe, a saman bargon na kwantar da ita duk kuwa da irin sanyin ruwa sama da ke jikinshi na nufi inda kayanmu suke na dauki Hijab dina da shima ya gama jikewa na saka a haka na fita daga kangon gidan da gudu zuwa nemam nepep, bakin titin gawon nama na fito duk wacce na tara bata tsayawa wata kila saboda ruwan be gama daukewa ba gashi dare ne, daker na samu wata wacce babu kowa a ciki ta tsaya da sauri na shiga ciki ina fadin.
“Mu bi ta nan marar lafiya za mu dauko”
Kamar yasan halin da nake ciki sai ya shiga kwanar Clapperto road da gudu muna kawowa kangon gidan na ce ya shigo ciki, da taimakon mai napep din muka saka ta ciki sannan na nufi jakar da kudin suke ciki na bude na daukosu gaba daya sun jike har sun hade guri daya, ni da Lukman muka shiga da sauri mai Napep din ya ja zuwa Uduth wato Usmanu dan fodio teaching Hospital, kamar yasan daman can nake son kaita. Ta sabon gate din emergency ya shiga da mu, ba laifi nurse din sun karbo mu hannu biyu sannan suka ce na je na karbo kati, da gudu na bazama cikin asibitin neman inda ake siyar da katin domin ban sani ba, hasali ma ban taba zuwa asibitin sai dai na bi na wuce, wata mace ce ta nuna min gurin da na isa ban samu layi sosai sai yan kwarorin mutane wata kila saboda yana dare ne. Amman a haka sai na kasa bin dan karamin layin na shiga rokonsu ina ta kuka.
“Dan Allah ku taimaka min na karbi kati mamana zata mutu dan Allah”
“Zo nan a baki”
Wanda ke layin gaba ya fada sauran kuwa kallona kawai suke jikina shakaf da ruwa har diga suke a kasa. Gabansa na shiga na mika dari biyar a bani katin sai ya ce min basa son kudinbda suke jike, mutumen nan ya ciro dubu daya sabuwa hul ya miki na karba hannu biyu na ba mai bayar da katin sannan na rubuta sunanta ya miko min katin da chanjina kusan dari hudu ya cire har da yan kai, a wautata sai na mikawa mutumen canjin.
“No rike, Allah bata lafiya”
“Amin na gode”
Na juyo da sauri zuwa inda mahaifiyata take, ina isowa likitan ya hau min tambayar ciwonta nai mishi bayani.
“Maciji ne ya tsare ta wata biyu da yan kwanuka da suka wuce, shi ne na kaita asibiti likitan yai mata tiyata ya cire dafin macijin, amman yace ta daina taba ruwa bata son sanyi shine yau ruwan sama ya doketa ta fara tarin jini”
“Dafin maciji ake yiwa tiyata? Allura dai ko?”
“Aa tiyata yana nan a cikinta ma”
Na fada ina girgiza masa kai. A take ya rubuta mana wasu abubuwan ya dauko wata takarda ya miko min.
“Ku dauke ta yanzu kuje a mata hoto”
Sai nurses din suka dora min ita akan wheelchair na soma turara muka fito daga dakin ina rike da takardar, daman Lukman na tsaye bakin kofar be shiga ciki ba. Da tambaya na isa gurin da aks hoto sai suka ce sai naje can wani guri na biya kudin sannan na kawo musu shaidar biyan, haka na barta a gurin na isa inda suka kwantanta min na bashi takardar da wacan mai hoton ya bani sai ya fada min kudin da zan biya.
“Dubu biyu da dari bakwai”
Na ciro kudin na bashi shi ma sai ya ki karba wadanda suka jiken wai basa son irinsu.
“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u”
Shine abunda na fada na ji kamar na dora hannuna a kai na kurma ihu iya karfina.
“Kawo kudin haka”
Ya fada yana mikon min hannunsa wata kila yaji tausayi na ne, a haka na mika masa dubu uku ya bani canji tare da shaidar biyan kudin sannan na juyo da guduna na dawo na kawo ma mai dauka hoton, sai da akai ma mutun hudu sannan aka shiga da ita aka dorata akan wani gado suka shafa mata wani mai a jiki suka dora mata wani abu mai kamar dutsin guga suna ta yawo da shi a cikinta. Bayan sun gama suka dora a kan kujerar wheelchair suka ce na fara zuwa na kaita can gurin likitan sai na dawo na karbi hoton.
Haka na turata na koma da ita a dakin da ke cike da majiyanta na tsaya a inda likitan ya saka aka sauketa dazun na kira wasu nurses suka zo suka taimaka na dorata saman gadon, sannan na kama hanyar komawa, abun ka da mai hankali tashe sai hanyar ta bace min ita kaure mutane ba tare da na kula ba. Har na kai ga yin kaura da wani likita zan wuce na ji an fisgoni an dawo da ni.
“Ke ba ki ga ni ne hala?”
Sai na kalleshi amman bana iya ganin fuskarsa saboda hawaye na cika min ido.
“Hoto zan karbo kuma gurin ya bace min”
Na fada cikin kuka mai karfi.
“Wow cute girl”
Ya fada kadan-kadan sannan ya nuna min gurin.
“Doc Muhseen yi sauri pls”
Wani mutumen mai sanye da uniform din nurse ya fada sai mutumen ya sake ni da sauri yai gaba ni kuma na nufi inda ya nuna min. Ko da na koma har an fitar da hoton sai kawai na karbo ma juyo na dawo inda nurse din suke na mika musu sai suka nuna min dakin likita.
“Can za ki shiga ki kai”
Na doshi dakin da sauri na tura na shiga ina sallama can ciki saboda kuka.
“Ga hoton”
Na mika masa sai ya karba yana ta turanci da wani mutumen dake zaune a daya daga cikin visitors chairs, likita yai rubutu cikin wata farar takarda ya miko min.
“Idan ki siyo ka bawa nurse su saka mata”
Na karba da sauri sannan na fice duk abunda nake Lukman na biye da ni a baya a duk inda na saka kafata dana dauke sai ya saka tasa. A nan ma sai da na tambaya aka nuna min pharmacy sannan na kai takadar su ma suka ce sai na je wani guri kusa da inda ake bata kati na biya kudin maganin da suka rubuta min a jikin takardar, haka na juyo cike da jin haushi irin tsarin na nu na wahalar da mai rai na je na mika takardar sai ya fada min cewar zan ba shi dubu biyar da dari uku da naira arba'in, a nan ma sai da nai ta roko sannan ya karbi jikakkun kudin ya bani yan canjina sai na koma can na kaiwa mai pharmacy ya bani amfanin da ledar sakawa. Kamar yadda likita ya fada min haka na mikawa nurses din sai suka hau dora mata ruwan suna saka maganin a ciki sukai nata allurai sannan suka dora ragowar maganin akan wani dan karamin abu mai kamar bedside drawer, sai ta sauke wani irin ajiyar zuciya bachi yai gaba da ita. Ni kuma na koma dakin likitan Lukman na biye da ni a baya na tura na shiga, har yanzu magana yake ta yi da mutuman dazun.
“Na ba su sun saka mata”
Sai ya dago ya kalleni yana dago hoton ya ce.
“Ba dafin maciji ke damun matar nan ba, gurin da aka cire mata koda ne ke mata zafi maybe ayi aikin yadda ya kamata ba”
Ji nai kamar ban ji abunda ya fada daidai ba, har sai da na sake tambaya cike da tantamar.
“Ban gane ba koda kuma?”
“Yes an yi mata tiyatar koda ko?”
“Aa ba ayi ba”
“Gashi nan hoto na nuna matar nan bata da koda ďaya, kuma gurin da aka cire kodar ne ke mata ciwo”
Aiko kamar jiran suke nai magana sai biyu daga cikinsu suka dauki Nana suka kai ta can kusa da gate suka aje dayan kuma ya turani waje da karfi, Lukman da tsoro tuni na nufi inda Nana take da sauri idonta cike da tsoro, sai kuma suka shiga ciki suka fara shuri da kayan mu da ke ciki sai da suka fitar da komai da kafa sannan suka fito suka nufo inda na ke tsaye ni da Nana muna muka suka ce mana idan muka sake shiga ciki duk suka dawo sai sun sassara mu, kuma mu nemi wani wajen tun kan dare yai mana mu bar gurin kwanon da aka saka dan fara zagayewa kamar za ayi gate.
A gurin muka tsaya ni da Nana da Lukman har aka fara ruwa, daga ni har Nana babu abunda muke sai hawaye Lukman na tsaye yana ta kallon ta bata fuska sosai kamar ya fasa kuka. Sai da naji an fara yayyafi sannan na rika Nana da zimmar mu koma ciki sai ta rike hannuna ta girgiza min ka alamar ba zata koma ba.
“Idan an gama ruwa sai mu fito”
Na fada da muryata ta kuka, sai ta girgiza min kai alamar ba zata ba, hakan yasa na nufi kayanmu na dauko bargon da likitan ya siya dan mu rika kwantawa ni da Lukman akai na lulluba mata na shiga ciki Lukman ma shigo muka fake a ciki ruwa na dukan kanmu. Wani abun Allah kuma sai akai ruwan da kama da bakin kwaya ga sanyi sosai domin har da kankanra suke. A take Nana ta fara tari jikinta na ta karkarwa jin hakan yasa nai saurin bude bargon sai na ga jini duk ya bata mata baki har ya sauko saman rigarta ashe tarin da take jini take fitarwa, rumgume ta nai na fashe da kuka ina daga kaina ina kallon ruwan saman da ke saukowa kamar a cikinsu wani zai kawo mana dauki....
Wayyo Nana 😪
https://my.w.tt/PWohUhlPv9.
*Z A K I*
By Khadeeja Candy
8️⃣
Sai da ruwan suka dan tsagaita sannan na samu damar mikewa tsaye ina daga Nana daga jikina. Ta galabaita sosai har wani lumshe ido take tana budewa amman wani abun mamaki idan ta kalleni sai tai min murmushi, wata kila so take ta kwantar min da hankali ganin irin yadda na ke ta kuka kamar ba gobe, a saman bargon na kwantar da ita duk kuwa da irin sanyin ruwa sama da ke jikinshi na nufi inda kayanmu suke na dauki Hijab dina da shima ya gama jikewa na saka a haka na fita daga kangon gidan da gudu zuwa nemam nepep, bakin titin gawon nama na fito duk wacce na tara bata tsayawa wata kila saboda ruwan be gama daukewa ba gashi dare ne, daker na samu wata wacce babu kowa a ciki ta tsaya da sauri na shiga ciki ina fadin.
“Mu bi ta nan marar lafiya za mu dauko”
Kamar yasan halin da nake ciki sai ya shiga kwanar Clapperto road da gudu muna kawowa kangon gidan na ce ya shigo ciki, da taimakon mai napep din muka saka ta ciki sannan na nufi jakar da kudin suke ciki na bude na daukosu gaba daya sun jike har sun hade guri daya, ni da Lukman muka shiga da sauri mai Napep din ya ja zuwa Uduth wato Usmanu dan fodio teaching Hospital, kamar yasan daman can nake son kaita. Ta sabon gate din emergency ya shiga da mu, ba laifi nurse din sun karbo mu hannu biyu sannan suka ce na je na karbo kati, da gudu na bazama cikin asibitin neman inda ake siyar da katin domin ban sani ba, hasali ma ban taba zuwa asibitin sai dai na bi na wuce, wata mace ce ta nuna min gurin da na isa ban samu layi sosai sai yan kwarorin mutane wata kila saboda yana dare ne. Amman a haka sai na kasa bin dan karamin layin na shiga rokonsu ina ta kuka.
“Dan Allah ku taimaka min na karbi kati mamana zata mutu dan Allah”
“Zo nan a baki”
Wanda ke layin gaba ya fada sauran kuwa kallona kawai suke jikina shakaf da ruwa har diga suke a kasa. Gabansa na shiga na mika dari biyar a bani katin sai ya ce min basa son kudinbda suke jike, mutumen nan ya ciro dubu daya sabuwa hul ya miki na karba hannu biyu na ba mai bayar da katin sannan na rubuta sunanta ya miko min katin da chanjina kusan dari hudu ya cire har da yan kai, a wautata sai na mikawa mutumen canjin.
“No rike, Allah bata lafiya”
“Amin na gode”
Na juyo da sauri zuwa inda mahaifiyata take, ina isowa likitan ya hau min tambayar ciwonta nai mishi bayani.
“Maciji ne ya tsare ta wata biyu da yan kwanuka da suka wuce, shi ne na kaita asibiti likitan yai mata tiyata ya cire dafin macijin, amman yace ta daina taba ruwa bata son sanyi shine yau ruwan sama ya doketa ta fara tarin jini”
“Dafin maciji ake yiwa tiyata? Allura dai ko?”
“Aa tiyata yana nan a cikinta ma”
Na fada ina girgiza masa kai. A take ya rubuta mana wasu abubuwan ya dauko wata takarda ya miko min.
“Ku dauke ta yanzu kuje a mata hoto”
Sai nurses din suka dora min ita akan wheelchair na soma turara muka fito daga dakin ina rike da takardar, daman Lukman na tsaye bakin kofar be shiga ciki ba. Da tambaya na isa gurin da aks hoto sai suka ce sai naje can wani guri na biya kudin sannan na kawo musu shaidar biyan, haka na barta a gurin na isa inda suka kwantanta min na bashi takardar da wacan mai hoton ya bani sai ya fada min kudin da zan biya.
“Dubu biyu da dari bakwai”
Na ciro kudin na bashi shi ma sai ya ki karba wadanda suka jiken wai basa son irinsu.
“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u”
Shine abunda na fada na ji kamar na dora hannuna a kai na kurma ihu iya karfina.
“Kawo kudin haka”
Ya fada yana mikon min hannunsa wata kila yaji tausayi na ne, a haka na mika masa dubu uku ya bani canji tare da shaidar biyan kudin sannan na juyo da guduna na dawo na kawo ma mai dauka hoton, sai da akai ma mutun hudu sannan aka shiga da ita aka dorata akan wani gado suka shafa mata wani mai a jiki suka dora mata wani abu mai kamar dutsin guga suna ta yawo da shi a cikinta. Bayan sun gama suka dora a kan kujerar wheelchair suka ce na fara zuwa na kaita can gurin likitan sai na dawo na karbi hoton.
Haka na turata na koma da ita a dakin da ke cike da majiyanta na tsaya a inda likitan ya saka aka sauketa dazun na kira wasu nurses suka zo suka taimaka na dorata saman gadon, sannan na kama hanyar komawa, abun ka da mai hankali tashe sai hanyar ta bace min ita kaure mutane ba tare da na kula ba. Har na kai ga yin kaura da wani likita zan wuce na ji an fisgoni an dawo da ni.
“Ke ba ki ga ni ne hala?”
Sai na kalleshi amman bana iya ganin fuskarsa saboda hawaye na cika min ido.
“Hoto zan karbo kuma gurin ya bace min”
Na fada cikin kuka mai karfi.
“Wow cute girl”
Ya fada kadan-kadan sannan ya nuna min gurin.
“Doc Muhseen yi sauri pls”
Wani mutumen mai sanye da uniform din nurse ya fada sai mutumen ya sake ni da sauri yai gaba ni kuma na nufi inda ya nuna min. Ko da na koma har an fitar da hoton sai kawai na karbo ma juyo na dawo inda nurse din suke na mika musu sai suka nuna min dakin likita.
“Can za ki shiga ki kai”
Na doshi dakin da sauri na tura na shiga ina sallama can ciki saboda kuka.
“Ga hoton”
Na mika masa sai ya karba yana ta turanci da wani mutumen dake zaune a daya daga cikin visitors chairs, likita yai rubutu cikin wata farar takarda ya miko min.
“Idan ki siyo ka bawa nurse su saka mata”
Na karba da sauri sannan na fice duk abunda nake Lukman na biye da ni a baya a duk inda na saka kafata dana dauke sai ya saka tasa. A nan ma sai da na tambaya aka nuna min pharmacy sannan na kai takadar su ma suka ce sai na je wani guri kusa da inda ake bata kati na biya kudin maganin da suka rubuta min a jikin takardar, haka na juyo cike da jin haushi irin tsarin na nu na wahalar da mai rai na je na mika takardar sai ya fada min cewar zan ba shi dubu biyar da dari uku da naira arba'in, a nan ma sai da nai ta roko sannan ya karbi jikakkun kudin ya bani yan canjina sai na koma can na kaiwa mai pharmacy ya bani amfanin da ledar sakawa. Kamar yadda likita ya fada min haka na mikawa nurses din sai suka hau dora mata ruwan suna saka maganin a ciki sukai nata allurai sannan suka dora ragowar maganin akan wani dan karamin abu mai kamar bedside drawer, sai ta sauke wani irin ajiyar zuciya bachi yai gaba da ita. Ni kuma na koma dakin likitan Lukman na biye da ni a baya na tura na shiga, har yanzu magana yake ta yi da mutuman dazun.
“Na ba su sun saka mata”
Sai ya dago ya kalleni yana dago hoton ya ce.
“Ba dafin maciji ke damun matar nan ba, gurin da aka cire mata koda ne ke mata zafi maybe ayi aikin yadda ya kamata ba”
Ji nai kamar ban ji abunda ya fada daidai ba, har sai da na sake tambaya cike da tantamar.
“Ban gane ba koda kuma?”
“Yes an yi mata tiyatar koda ko?”
“Aa ba ayi ba”
“Gashi nan hoto na nuna matar nan bata da koda ďaya, kuma gurin da aka cire kodar ne ke mata ciwo”