Sashe 119
Zaki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Lafiya Mama? Miya faru?”
“Wai Ataa tana da ciki, kiji wani al'amari daga Allah, duka abubuwan nan sun zo mana ta hanyar da ba za mu iya nuna farincikinmu ko kulawarmu ba, a da idan wani abun farinciki ya samu Aliyu ni yake fara yi ma albishir kamin kowa, amman yau ya fadawa Nasir wannan albishir din bayan ya san na fi kowa bukatar ya samu haihuwa, be fada min ba saboda yana tunanin bana son Ataa ba zan yi farinciki da samun cikin ba, Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u”
Tashi tai jiki ba gwari ta nufi dakinta, zazzabi ne ya rufe ta gaba daya yamma cin batai shi da dadi ba, da ada ne da yanzu ta fara kiran Momy da duk wani makusancin da labarta masa abun dadi da murna ya samu amman yanzu babu wannan damar, da dare ma kasa runtsawa tai tana son ta kira Aliyu ta yi magana da shi amman tana jin nauyi saboda ta san yana tare da Ataa, kuma tai ta jiran ya kirata be kirata ba har garin Allah ya waye.
Misalin bakwai na safe tana zaune saman carpet din da tai sallah kasancewar jiya da yau ba ita ce da girki ba Ammy ce, Nana kuma ta kwana a bangaren Ammy, ban da Maryam da Rukaiya babu wanda ya san bata jindadi domin Muhseen be shigo gidan ba gaba daya tun da ya ga Ataa ta zo ya sake fita be dawo ba. Wayar Aliyu ringing biyu ya daga da far'asa yai mata sallama.
“Assalamu Alaikum”
Ta amsa mishi da muryar mai karantar da shi damuwarta.
“Aliyu kana tunanin ba zan yi farinciki da samun cikin ba shiyasa baka kira da kanka ka fada min ba?”
“Wallahi ba haka ba ne Mama Nasir ne ya ce kar nai rashin kunya na bari zai kira ku ya fada muku amman ba dan wani abu ba”
“Aliyu yadda na ke son ka haihu ko da karuwa ce ta samu ciki da kai zan yi farinciki, saboda na ce bana son Ataa ba shi yake nufin bana son abunda zata haifa maka ba, ita ma kuma da na san da zuwan wannan abun da ban aikata mata komai ba, ina jin kunyarta da na mahaifiyarta na abunda na aikata musu, amman Wallahi ba zan taba kin jininka ba ba zan taba tsana ki nuna kyama a gurin abunda Ataa zata haifa maka ba, ko da ko ace gaskiyar wacece ita be bayyana ba”
Tana gama fadar hakan ya kashe wayar tana hawaye.
ALIYU POV.
Damuwa ce shimfide a fuskar Aliyu, yadda ya ji muryar Mama Fulani abun be masa dadi ba, yadda baya son wani abu ya dami Momy haka baya son abunda ya taba Mama Fulani.
“Minene?”
“Mama ce, bata jidadin yadda na sanar da Nasir zancen samun cikinki ban sanar mata ba”
Ataa ta aje mug din dake hannunta na tea da ya hada mata tun da azuba tana kallonsa.
“Bata jidadin na samu cikin ba? Ko kuma saboda ni ce na samu cikin yasa ba ta jidadi ba?”
Matsowa yai da ita kusa da shi.
“Mama tana son cikin nan, ko da ko ke ko wata ce wadda ta fiki talauci, ko kuma wacce ta fiki arziki, saboda tana son farincikina, kuma tun kamin Momy ta fara damuwa da rashin haihuwa ta, ita ta fara min zancen karin aure kamin Momy, Mama Fulani bata son wani abun da zai taba ni ko kadan, shiyasa ko a wacan lokacin da na ake fada mata cewar ni ne da matsalar ba Rahma sai ta nuna damuwarta kuma ta nuna min na kara aure idan ban haihuwa sai a barwa Allah ko kuma a cigaba da neman magani”
“Kana da wata matsala ne?”
“Ba ni da wata matsala, Rahma ce mai matsala domin kwa haihuwa baya iya zama a cikin mahaifarta, amman sai na boye mata, da farko wace na ke ni d ita duka ba mu da matsala sai na biya likita kuma na roke shi ya fada mata haka, saboda kar damuwar tai mata yawa, ga ciwonta kuma idan ta ji bata iya haihuwa abun zai nata yawa, daga baya na maida abun kaina na ce mata da kowa cewar ni ne mai matsala ba ita ba, saboda Nasir ya ba ni shawarar yin hakan”
“Amman Aliyu miye alakar da Mama Fulani? Na san Momy ce ta haife ka”
“Momy ce ta haife ni tabbas, amman a hannun Mama na girma, Mama Fulani da Momy aminan juna ne tun a makaranta a lokacin Mama Fulani tana Yola kasancewar ta yar can, Momy kuma yar sokoto amman sai suka hadu a ABU zaria gurin karatu a daki daya suke komai tare suke kamar yadda na samu labari, Daddyn dan'uwan Momy ne Cousin brother dinta ne ta gurin uwa, tun tana makaranta ta fada min wani lokacin a sokoto suke hutu ita da Mama Fulani, wani lokacin kuma a yola suke hutu gidansu Mama Fulani, after sun gama makaranta aka saka ranar aurenta da Daddy, a gurin bikinsu ne Abbah wanda yake kanen ga Daddy ya ga Mama Fulani har ya fara sonta har Allah yai abun ita ya aureta, a sokoto suka zauna dukansu a wacan lokacin shiyasa a lokacin da Momy ta haife ni na isa yaye sai Mama Fulani ta yayeni, daga nan Daddyn ya samu aikin wannan kamfanin suka dawo a nan Abuja sai ta dawo tare da ni, kawaici irin na Momy ya sa ta kasa cewa a bata danta domin har tsawon lokacin da na fara wayo Mama Fulani bata samu ciki ba, sai daga baya aka haifi Muhseen daga shi kuma sai ta dade kamin ta sake haihuwa wanda hakan yasa Abbah ya auro Ammy, sai kuma haihuwar ta zo mata daga baya su kai ta yi tare da Ammy. Mama Fulani ta rike ni tsakani da Allah bata bari wani abun ya same ni ko nai kuka duk wani abun da nake so shi take min, kina da idonki idan wani abun ya shiga tsakanina da Muhseen ni take ba gaskiya, ko da shi ne da gaskiyar, bata taba yarda yaranta su rainani shiyasa na taso bana sake musu fuska saboda kar su raina ni din, har abun ya zame min jiki, kowa a gidan yana saunata ko yin wani abu a gabana ciki har da shi Muhseen din, hakan yasa ba mu jituwa da shi, ba ma san inuwa daya bama fahimtar junanmu, saboda shi yana ganin ina akan kuskure abubuwan da na ke yi ni ma kuma ina ganin yadda yake sakewa yana wasu abubuwan basa burgeni, a ciki kuwa har da tsanar talaka wanda na samu asalinsa daga gurin Mama Fulani, ban taba daukar cewar abunda Momy da Muhseen suke nuna min abu ne mai kyau ba sai haduwa ta da ke”
Yayi shiru sannan ya rumgume ya sumbaci saman kanta.
“Na san ba za ki taba son Mama Fulani ba, amman zan jidadi idan kika aje kiyayyarta a zuciyarki ba tare da kin nuna mata a gabana ba, Mama Fulanu tana da muhimmanci da daraja da kima a gareni wanda Momy ma ba zata so ki wulakantata ba, Mama tana son cikin nan ko da ko bata so ki ba saboda cikin jikinki nawa ne, tana jin kunyarki da mahaifiyarki da tasan da zuwan wannan abun tace da bata aikata miki komai ba”
“Miyasa sai ni Aliyu? Wata kila da asalina be bayyana ba, da har yanzu Mama Fulani ba zata ce tana jin kunyata ba, ko ba ni ba ko wane dan'adam mai daraja ne Aliyu, idan babu talaka wallahi masu kudin ba za su iya rayuwa ba, da babu talaka fada min wa zai zo gurinta nema har ta gane cewar tana da arzikin? Wa zai gina mata gidan da zata zauna? Wa zai tuka mata motar da zata hau? Wa zai mata wanki da guga da gyaran gida ko na sani abun idan ya kama? Wanda ba shi da jinkai yake so da kauna da tausayi ba kyara da tsangwama ba, abun Alfarinka ne ace yau kana da abunda zaka iya dafawa ka bawa wani ko kuma ya taimaki wani a cikin taimakon da Allah yai maka, tarin dukiya ba abun alfahari ba ne tarin imani da yawan taimako da kyakkyawan aiki shine abun tinkaho da bugun gaba, ranar lahira a wareka a bainar jama'a a karramaka akan aikin alherinka shine abun jindadi, ba a tsare ka ana tuhumwar ka da daga inda ka samo dukiyarka ba kuma taya ka kashe ta? Wa ka zalinta da ita waya amfana da ita? Wani aiki kai ita saboda Allah? Aliyu ya zaja ji idan Allah ya tsayarda Mama Fulani a gabansa ya tuhumeta akan zalincin da tai na wani ko musgunawa saboda ita tana da dukiya shi ba shi da ita ba? Wanda ya baka dukiyar da kansa ya tambayi ka dalilin wulakanta wani saboda abunda ya baka shi ya hana shi? Miyasa ba zaka fada mata gaskiya ka nuna nata abunda take ba daidai ba ne? Talaka kan kaurai zai dade da shiga mai kudi yana can yana amsa tamaboyoyin dukiyarsa, ashe ko dukiya da zata saka ka fadin rai da wulakanta wasu ba abun tinkaho ba ce matukar ba ta taimakon bayin Allah ce da addininsa ba”
ATAA POV.
hawaye na ke yayinda na ke maganar ba da Mama Fulani kadai na ke ba, har da Aliyu na ke domin shi ma rayuwarsa kenan kamin yanzu, da kuma duk wani mai halin irin nasa. Yadda na ga jikinsa yai sanyi sosai ya karantar da ji cewar sakona ya isa a inda nake son isar da shi domin hawaye na gani a idonta yana ta kallona.
“Na gode Allah daya bani mata kamar ke, yarinya ce ke amman mai hankali da natsuwa da hangen nesa, ina son ki ina son abunda cikin cikinki”
Ya fada yana murmushi. Hannu na saka da kaina na share masa hawayen na rumgume shi da kaina ina jin wani irin dadi marar misaltuwa.
RAHMA POV.
“Wai Ataa tana da ciki, kiji wani al'amari daga Allah, duka abubuwan nan sun zo mana ta hanyar da ba za mu iya nuna farincikinmu ko kulawarmu ba, a da idan wani abun farinciki ya samu Aliyu ni yake fara yi ma albishir kamin kowa, amman yau ya fadawa Nasir wannan albishir din bayan ya san na fi kowa bukatar ya samu haihuwa, be fada min ba saboda yana tunanin bana son Ataa ba zan yi farinciki da samun cikin ba, Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u”
Tashi tai jiki ba gwari ta nufi dakinta, zazzabi ne ya rufe ta gaba daya yamma cin batai shi da dadi ba, da ada ne da yanzu ta fara kiran Momy da duk wani makusancin da labarta masa abun dadi da murna ya samu amman yanzu babu wannan damar, da dare ma kasa runtsawa tai tana son ta kira Aliyu ta yi magana da shi amman tana jin nauyi saboda ta san yana tare da Ataa, kuma tai ta jiran ya kirata be kirata ba har garin Allah ya waye.
Misalin bakwai na safe tana zaune saman carpet din da tai sallah kasancewar jiya da yau ba ita ce da girki ba Ammy ce, Nana kuma ta kwana a bangaren Ammy, ban da Maryam da Rukaiya babu wanda ya san bata jindadi domin Muhseen be shigo gidan ba gaba daya tun da ya ga Ataa ta zo ya sake fita be dawo ba. Wayar Aliyu ringing biyu ya daga da far'asa yai mata sallama.
“Assalamu Alaikum”
Ta amsa mishi da muryar mai karantar da shi damuwarta.
“Aliyu kana tunanin ba zan yi farinciki da samun cikin ba shiyasa baka kira da kanka ka fada min ba?”
“Wallahi ba haka ba ne Mama Nasir ne ya ce kar nai rashin kunya na bari zai kira ku ya fada muku amman ba dan wani abu ba”
“Aliyu yadda na ke son ka haihu ko da karuwa ce ta samu ciki da kai zan yi farinciki, saboda na ce bana son Ataa ba shi yake nufin bana son abunda zata haifa maka ba, ita ma kuma da na san da zuwan wannan abun da ban aikata mata komai ba, ina jin kunyarta da na mahaifiyarta na abunda na aikata musu, amman Wallahi ba zan taba kin jininka ba ba zan taba tsana ki nuna kyama a gurin abunda Ataa zata haifa maka ba, ko da ko ace gaskiyar wacece ita be bayyana ba”
Tana gama fadar hakan ya kashe wayar tana hawaye.
ALIYU POV.
Damuwa ce shimfide a fuskar Aliyu, yadda ya ji muryar Mama Fulani abun be masa dadi ba, yadda baya son wani abu ya dami Momy haka baya son abunda ya taba Mama Fulani.
“Minene?”
“Mama ce, bata jidadin yadda na sanar da Nasir zancen samun cikinki ban sanar mata ba”
Ataa ta aje mug din dake hannunta na tea da ya hada mata tun da azuba tana kallonsa.
“Bata jidadin na samu cikin ba? Ko kuma saboda ni ce na samu cikin yasa ba ta jidadi ba?”
Matsowa yai da ita kusa da shi.
“Mama tana son cikin nan, ko da ko ke ko wata ce wadda ta fiki talauci, ko kuma wacce ta fiki arziki, saboda tana son farincikina, kuma tun kamin Momy ta fara damuwa da rashin haihuwa ta, ita ta fara min zancen karin aure kamin Momy, Mama Fulani bata son wani abun da zai taba ni ko kadan, shiyasa ko a wacan lokacin da na ake fada mata cewar ni ne da matsalar ba Rahma sai ta nuna damuwarta kuma ta nuna min na kara aure idan ban haihuwa sai a barwa Allah ko kuma a cigaba da neman magani”
“Kana da wata matsala ne?”
“Ba ni da wata matsala, Rahma ce mai matsala domin kwa haihuwa baya iya zama a cikin mahaifarta, amman sai na boye mata, da farko wace na ke ni d ita duka ba mu da matsala sai na biya likita kuma na roke shi ya fada mata haka, saboda kar damuwar tai mata yawa, ga ciwonta kuma idan ta ji bata iya haihuwa abun zai nata yawa, daga baya na maida abun kaina na ce mata da kowa cewar ni ne mai matsala ba ita ba, saboda Nasir ya ba ni shawarar yin hakan”
“Amman Aliyu miye alakar da Mama Fulani? Na san Momy ce ta haife ka”
“Momy ce ta haife ni tabbas, amman a hannun Mama na girma, Mama Fulani da Momy aminan juna ne tun a makaranta a lokacin Mama Fulani tana Yola kasancewar ta yar can, Momy kuma yar sokoto amman sai suka hadu a ABU zaria gurin karatu a daki daya suke komai tare suke kamar yadda na samu labari, Daddyn dan'uwan Momy ne Cousin brother dinta ne ta gurin uwa, tun tana makaranta ta fada min wani lokacin a sokoto suke hutu ita da Mama Fulani, wani lokacin kuma a yola suke hutu gidansu Mama Fulani, after sun gama makaranta aka saka ranar aurenta da Daddy, a gurin bikinsu ne Abbah wanda yake kanen ga Daddy ya ga Mama Fulani har ya fara sonta har Allah yai abun ita ya aureta, a sokoto suka zauna dukansu a wacan lokacin shiyasa a lokacin da Momy ta haife ni na isa yaye sai Mama Fulani ta yayeni, daga nan Daddyn ya samu aikin wannan kamfanin suka dawo a nan Abuja sai ta dawo tare da ni, kawaici irin na Momy ya sa ta kasa cewa a bata danta domin har tsawon lokacin da na fara wayo Mama Fulani bata samu ciki ba, sai daga baya aka haifi Muhseen daga shi kuma sai ta dade kamin ta sake haihuwa wanda hakan yasa Abbah ya auro Ammy, sai kuma haihuwar ta zo mata daga baya su kai ta yi tare da Ammy. Mama Fulani ta rike ni tsakani da Allah bata bari wani abun ya same ni ko nai kuka duk wani abun da nake so shi take min, kina da idonki idan wani abun ya shiga tsakanina da Muhseen ni take ba gaskiya, ko da shi ne da gaskiyar, bata taba yarda yaranta su rainani shiyasa na taso bana sake musu fuska saboda kar su raina ni din, har abun ya zame min jiki, kowa a gidan yana saunata ko yin wani abu a gabana ciki har da shi Muhseen din, hakan yasa ba mu jituwa da shi, ba ma san inuwa daya bama fahimtar junanmu, saboda shi yana ganin ina akan kuskure abubuwan da na ke yi ni ma kuma ina ganin yadda yake sakewa yana wasu abubuwan basa burgeni, a ciki kuwa har da tsanar talaka wanda na samu asalinsa daga gurin Mama Fulani, ban taba daukar cewar abunda Momy da Muhseen suke nuna min abu ne mai kyau ba sai haduwa ta da ke”
Yayi shiru sannan ya rumgume ya sumbaci saman kanta.
“Na san ba za ki taba son Mama Fulani ba, amman zan jidadi idan kika aje kiyayyarta a zuciyarki ba tare da kin nuna mata a gabana ba, Mama Fulanu tana da muhimmanci da daraja da kima a gareni wanda Momy ma ba zata so ki wulakantata ba, Mama tana son cikin nan ko da ko bata so ki ba saboda cikin jikinki nawa ne, tana jin kunyarki da mahaifiyarki da tasan da zuwan wannan abun tace da bata aikata miki komai ba”
“Miyasa sai ni Aliyu? Wata kila da asalina be bayyana ba, da har yanzu Mama Fulani ba zata ce tana jin kunyata ba, ko ba ni ba ko wane dan'adam mai daraja ne Aliyu, idan babu talaka wallahi masu kudin ba za su iya rayuwa ba, da babu talaka fada min wa zai zo gurinta nema har ta gane cewar tana da arzikin? Wa zai gina mata gidan da zata zauna? Wa zai tuka mata motar da zata hau? Wa zai mata wanki da guga da gyaran gida ko na sani abun idan ya kama? Wanda ba shi da jinkai yake so da kauna da tausayi ba kyara da tsangwama ba, abun Alfarinka ne ace yau kana da abunda zaka iya dafawa ka bawa wani ko kuma ya taimaki wani a cikin taimakon da Allah yai maka, tarin dukiya ba abun alfahari ba ne tarin imani da yawan taimako da kyakkyawan aiki shine abun tinkaho da bugun gaba, ranar lahira a wareka a bainar jama'a a karramaka akan aikin alherinka shine abun jindadi, ba a tsare ka ana tuhumwar ka da daga inda ka samo dukiyarka ba kuma taya ka kashe ta? Wa ka zalinta da ita waya amfana da ita? Wani aiki kai ita saboda Allah? Aliyu ya zaja ji idan Allah ya tsayarda Mama Fulani a gabansa ya tuhumeta akan zalincin da tai na wani ko musgunawa saboda ita tana da dukiya shi ba shi da ita ba? Wanda ya baka dukiyar da kansa ya tambayi ka dalilin wulakanta wani saboda abunda ya baka shi ya hana shi? Miyasa ba zaka fada mata gaskiya ka nuna nata abunda take ba daidai ba ne? Talaka kan kaurai zai dade da shiga mai kudi yana can yana amsa tamaboyoyin dukiyarsa, ashe ko dukiya da zata saka ka fadin rai da wulakanta wasu ba abun tinkaho ba ce matukar ba ta taimakon bayin Allah ce da addininsa ba”
ATAA POV.
hawaye na ke yayinda na ke maganar ba da Mama Fulani kadai na ke ba, har da Aliyu na ke domin shi ma rayuwarsa kenan kamin yanzu, da kuma duk wani mai halin irin nasa. Yadda na ga jikinsa yai sanyi sosai ya karantar da ji cewar sakona ya isa a inda nake son isar da shi domin hawaye na gani a idonta yana ta kallona.
“Na gode Allah daya bani mata kamar ke, yarinya ce ke amman mai hankali da natsuwa da hangen nesa, ina son ki ina son abunda cikin cikinki”
Ya fada yana murmushi. Hannu na saka da kaina na share masa hawayen na rumgume shi da kaina ina jin wani irin dadi marar misaltuwa.
RAHMA POV.