Sashe 37
Zaki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Inteesar da fada min, ni kuma na tashi na shiga kitchen din a inda na samu abincin dazu nan aka sake aje min wani yanzu ma tuwo ne kamar dazun sai dai wannan miyar ganye ce ba kamar dazunda taie miyar yauki ba. Dauko abincin nai na fito waje falon na zauna na ci sai da na koshi sannan na tashi na maida plate din na wanke hannuna.
Haka rayuwata ta cigaba da tafiya a gidan kullum Mama Fulani da Yayanta cikin nuna min kyama suke, a gurin Ya Muhseen kawai na ke samun sakewa har dadi nake ji idan yana nan, tun ina kin sakewa da shi har na soma sakewa kwanan biyu da nai a gidan sai na ji kamar daman can na basa da gidan, sai na fara sabawa da halin Mama Fulani da kuma Ammy da bata nuna min kyama, sai dai abu daya ke damuna kwana a gareji da kuma wanka idan zan yi sai naje garden na boya a bayan itace sannan nai wanka, da sabulun da Ammy ta ba ni, idan kuma ba haya zan yi sai dai na raba a dakin mai gadin na shiga nai.
Yau ma na yi aikina kamar yadda na saba, bayan na gama da bangaren Mama Fulani na je sashen Ammy nai mata nata sannan na shiga bangaren Ya Muhseen shi ma na gyara masa nasan dakin da falon na goge komai kamar yadda na fara yi masa a jiya na fito na dawo bangaren Mama Fulani, kowa na falon kasancewar Weekend ne Ya Muhseen da Anty Maryam na zaune a kujera daya tana nunawa Ya Muhseen wani abu a wayarta, Mama Fulani kuma na zaune kasa tana mulka fulawa, sama sama nake jin tana firar dan ta nan tafe dole ta dafa masa abunda ya ke so, sai da ta gama mulka fulawar sannan ta kalleni.
“Ke je kitchen ki yanka min kabeji, yana nan a roba”
Na amsa da to ina mikewa tsaye na nufi kitchen din, yana jiyo lokacin da Ya Muhseen ke fadar cewar ina da gashi, har Mama fulani na masa fada wai yana ta abu kamar be tana ganin kyakkyawar mace ba. Karamar kujera na samu na zauna na dauko daya daga cikin wukaken da suke hade guri daya na soma yanka kabejin, ban ankara ba na yanke kaina sai jini, ban san lokacin da na kwala wani uban ihu ba na mike tsaye da sauri jikina nata rawa abun ka da mao tsoro ga shi ban saba da amfani da wuka sosai ba, rabon da naji ciwo har jini ya fito haka har na manta.
Cikin sauri Ya Muhseen ya shigo kitchen din.
“Daman na san yankewa kikai”
Ya fada yana kallon yadda jinin ya samu hanya sai bulbulowa yake, ni ko ina ta kuka kamar hannun ya cire gaba daya, wanda hakan yasa Anty Maryam shigowa kitchen din tana tambayar ba'asi. Wani dogon tsaki taja ganin ganin a yatsa ne kawai na yanke amman nake wannan ihun. Hannun nawa Ya Muhseen ya riko muka fito daga kitchen din ina ta kuka sosai muka nufi kofar fita jinin nata zuba. Bangarensa yaje da ni ya dauko wani dan karamin akwati ya bude ya saka ruwan nan masu shegen zafi ya goge min gurin ya saka min wani maganin sannan ya saka min kada ya rufe min yatsan.
“Sarkin raki”
Ya fada yana kallon yadda hawaye suka bata min fuska, na turo baki waje kamar yadda yara suke idan sun ji ciwo.
“Kadan ne fa kika ji ciwon amman kin cika mana gida da ihu ke sagartacciya ko?”
Na yi kasa ta kaina ina kallon yadda yake aiko min da murmushi.
“Shikenan zaki iya tafiya”
Ina juyowa shi ma ya tashi tsaye muka fito tare, ina gaba yana bayana har muka shiga part din Mama Fulani.
“Muhseen karka sake shiga safgar yarinyar nan”
“Mi akai?”
“Na dai fada maka? Ba ita ba kai daga yau, ke kuma dauko Mopper ki goge jinin nan”
Ta karasa tana kallona, sai na nufi inda mopper take na dauko na goge duk inda jinin ya diga sannan na koma kitchen din, zan cigaba da yanka Anty Maryam ta shigo wai na zubar da wannan kabejin basa son sa na yanka wani sabo. A kwandon shara na zuba kabejin na dauko wani a freezer dake kwance na soma yankawa, a hankali nake har na gama sannan na aje mata shi na fito na nufi part din Ammy. A lokacin da na shiga falon ita kuma tana kitchen tana hada fruits salad, a falon nai zamana har aka yi azahar sannan ta fito ta miko min plate da spoon.
“Ga abincin ki”
Hannu biyu na saka na karba ina mata godiya. A gurin na zauna na ci sannan na aje mata plate din a kitchen, na fito na nufi garden na wanke hannuna da fanfan gurin, nai zamana gurin ina ta kallo wasu kananna tsuntsaye dake cikin keji suna cin giďa, ina jin lokacin da motacin har biyu suka tsaya a habarar gidan amman ban tashi ba sai da na gaji da zaman na fito na ratsa motocin zan shiga part din Mama Fulani sai na soma jin kamshin wani turare mai dadi, da na taba ji sai dai ba zan iya tuna inda na ji shi ba. Tura kofar falon nai na shiga da sallamata babu wanda ya amsa min sai Ya Muhseen, Anty Maryam da Anty Rukaiya duk sun sha jinin jikinsu ko motsin kirki basa yi, Mama Fulani kuma na zaune a kujera daya da wani saurayi tana bare masa abaya ba tana mika masa, da na kalleshi da kyau sai na ga she mutumen da nai ma aiki kamin na dawo Abuja hakimce a kujera yana kallona da mugun mamaki.
*Z A K I -it's not free, pay 300 to 0314795884 Abubakar Gt bank, then send the evidence via 08036126660*
Idan ba ki biya ba karki karanta hakkin wani. Idan kuma kin ji zaki iya Bismillah.
20.
Ba ni kadai yake kallo ba, gaba dayan jikina da duk wani motsi takun da nake na karasa gurin da na saba zama na zauna yake kallo. Nima idona na kansa ina ta mamakin abunda ya kawo shi gida, da alama yana da kyakkyawar alaka da mutanen gidan, domin yadda na ga Mama Fulani na bare ayaba tana bashi yana ci kamar wani karamin yaro ya nuna yana da muhimmanci sosai a gareta duk da ban san alakarsu ba.
“Ke bana son kallo”
Ya fada yana kallona, sai duk suka juyo suka kalli inda na ke kokarin zama.
“Haka ta ke da shegen kallo kamar yar kauye”
Anty Maryam ta fada tana watsa min harara. Ya Muhseen yaja tsaki.
“Aliyu kana da matsala Wallahi, taya akai kai kaga tana kallon ka? Haka kawai za ka ce kar ta kalleka kai kuma ka kalleta?”
“How dare you zaka fada min wannan maganar sa'an ka ne ni?”
Aliyun ya fada yana mikewa tsaye cikin zafin rai kamar zai da ki Ya Muhseen. Ya Muhseen ya mike tsaye yana kara jan tsakin.
“Rayuwarku batai ba Wallahi, arziki ai ba hauka ba ne, shikenan dan tana talaka bata da gata kallon ma sai an shar'anta mata kalar da za tai?”
“Muhseen enough! Wai Aliyu ba yayanka ba ne kake fada masa wannan maganar?”
Mama Fulani ta fada tana mikewa tsaye tare da shiga tsakaninsu.
“Shikenan dan ya girmeni yayi ba daidai ba ba za ayi magana ba? Waye shi?”
“Amman ka san Aliyu ba ita ya hana kallonsa ba, ko su Maryam da Batulu da suke kannensa basa tsare shi da ido ko? Ina ruwanka da shi ne? Wai ku kullum kuka hadu a waje daya sai fada ya shiga tsakaninku? Kamar kare da Mage! Haba sai ka ce wasu abokan adawa”
Mama Fulani ta fada cikin yanayin da ke nuna damuwarta karara. Ya Muhseen be sake cewa komai ba ya watsawa Aliyu harara ya fice daga falon, sai da ya fice sannan Aliyu ya koma ya zauna sai ya maida idonsa a kaina, ni dai nai kasa da idona gudun kar Mama Fulani ta ce na yi laifi, amman idan ta shi ne bana tsoron duk abunda zai fada, lokaci zuwa lokaci idan na dago na sai na ga ni yake kallo, ka ji wani tsantsar zalinci amman ni ya ce ba zan kalleshi ba. A dago ta hudu da nai muka hada na watsa masa harara kadan sannan na maida idona kasa.
“Ke tashi ki fita bakar munafuka”
Mama Fulani ta fada min a tsawace tana watsa min harara, ba musu na tashi na fice daga falon, na koma garejen na zauna abuna ina ta jin zafin kalmar munafuka da Mama Fulani ta kira ni da ita. Zaune nai a gurin na rumgume hannayena ina turo baki kamar an min wani abun bayan wannan, ina jin motsin shigowar Ya Muhseen a garejin nai saurin gyara zamana.
“Pretty ta so muje part din Ammy”
Ya fada yana zuba duka hannayensa aljihu, ni kuma na mike tsaye na karasa inda yake ba tare da na san bakina yana nan a yadda na turo shi ba.
“Fushin ne har yanzu? Ki daina damuwa da lamarin Mama haka rayuwarta take, amman Aliyu idan yai miki ki rama”
“Idan na rama ai Mama Fulani fada za ta min, ko kuma shi ya dake ni”
“Ba zai dake ki ba, wai baya dukan mata sai maza, Aliyu ba shi da kirki ko kadan”
Ban sake cewa komai ba muka jero ni da shi muna tafiya har muka isa part din Ammy, Anty Humaira ce zaune ita da Inteesar suna playing wani gate da ke cikin plate da wani abu mulmulalle, kusa da Anty Humaira Ya Muhseen ya zauna ni kuma na zauna daga can gurin kofar shigowa falon ina kallonsu, Anty Humaira aka fara ci kamin aci Ya Muhseen abun gwanin sha'awa sai dariya na ke.
“Zo mu yi”
Haka rayuwata ta cigaba da tafiya a gidan kullum Mama Fulani da Yayanta cikin nuna min kyama suke, a gurin Ya Muhseen kawai na ke samun sakewa har dadi nake ji idan yana nan, tun ina kin sakewa da shi har na soma sakewa kwanan biyu da nai a gidan sai na ji kamar daman can na basa da gidan, sai na fara sabawa da halin Mama Fulani da kuma Ammy da bata nuna min kyama, sai dai abu daya ke damuna kwana a gareji da kuma wanka idan zan yi sai naje garden na boya a bayan itace sannan nai wanka, da sabulun da Ammy ta ba ni, idan kuma ba haya zan yi sai dai na raba a dakin mai gadin na shiga nai.
Yau ma na yi aikina kamar yadda na saba, bayan na gama da bangaren Mama Fulani na je sashen Ammy nai mata nata sannan na shiga bangaren Ya Muhseen shi ma na gyara masa nasan dakin da falon na goge komai kamar yadda na fara yi masa a jiya na fito na dawo bangaren Mama Fulani, kowa na falon kasancewar Weekend ne Ya Muhseen da Anty Maryam na zaune a kujera daya tana nunawa Ya Muhseen wani abu a wayarta, Mama Fulani kuma na zaune kasa tana mulka fulawa, sama sama nake jin tana firar dan ta nan tafe dole ta dafa masa abunda ya ke so, sai da ta gama mulka fulawar sannan ta kalleni.
“Ke je kitchen ki yanka min kabeji, yana nan a roba”
Na amsa da to ina mikewa tsaye na nufi kitchen din, yana jiyo lokacin da Ya Muhseen ke fadar cewar ina da gashi, har Mama fulani na masa fada wai yana ta abu kamar be tana ganin kyakkyawar mace ba. Karamar kujera na samu na zauna na dauko daya daga cikin wukaken da suke hade guri daya na soma yanka kabejin, ban ankara ba na yanke kaina sai jini, ban san lokacin da na kwala wani uban ihu ba na mike tsaye da sauri jikina nata rawa abun ka da mao tsoro ga shi ban saba da amfani da wuka sosai ba, rabon da naji ciwo har jini ya fito haka har na manta.
Cikin sauri Ya Muhseen ya shigo kitchen din.
“Daman na san yankewa kikai”
Ya fada yana kallon yadda jinin ya samu hanya sai bulbulowa yake, ni ko ina ta kuka kamar hannun ya cire gaba daya, wanda hakan yasa Anty Maryam shigowa kitchen din tana tambayar ba'asi. Wani dogon tsaki taja ganin ganin a yatsa ne kawai na yanke amman nake wannan ihun. Hannun nawa Ya Muhseen ya riko muka fito daga kitchen din ina ta kuka sosai muka nufi kofar fita jinin nata zuba. Bangarensa yaje da ni ya dauko wani dan karamin akwati ya bude ya saka ruwan nan masu shegen zafi ya goge min gurin ya saka min wani maganin sannan ya saka min kada ya rufe min yatsan.
“Sarkin raki”
Ya fada yana kallon yadda hawaye suka bata min fuska, na turo baki waje kamar yadda yara suke idan sun ji ciwo.
“Kadan ne fa kika ji ciwon amman kin cika mana gida da ihu ke sagartacciya ko?”
Na yi kasa ta kaina ina kallon yadda yake aiko min da murmushi.
“Shikenan zaki iya tafiya”
Ina juyowa shi ma ya tashi tsaye muka fito tare, ina gaba yana bayana har muka shiga part din Mama Fulani.
“Muhseen karka sake shiga safgar yarinyar nan”
“Mi akai?”
“Na dai fada maka? Ba ita ba kai daga yau, ke kuma dauko Mopper ki goge jinin nan”
Ta karasa tana kallona, sai na nufi inda mopper take na dauko na goge duk inda jinin ya diga sannan na koma kitchen din, zan cigaba da yanka Anty Maryam ta shigo wai na zubar da wannan kabejin basa son sa na yanka wani sabo. A kwandon shara na zuba kabejin na dauko wani a freezer dake kwance na soma yankawa, a hankali nake har na gama sannan na aje mata shi na fito na nufi part din Ammy. A lokacin da na shiga falon ita kuma tana kitchen tana hada fruits salad, a falon nai zamana har aka yi azahar sannan ta fito ta miko min plate da spoon.
“Ga abincin ki”
Hannu biyu na saka na karba ina mata godiya. A gurin na zauna na ci sannan na aje mata plate din a kitchen, na fito na nufi garden na wanke hannuna da fanfan gurin, nai zamana gurin ina ta kallo wasu kananna tsuntsaye dake cikin keji suna cin giďa, ina jin lokacin da motacin har biyu suka tsaya a habarar gidan amman ban tashi ba sai da na gaji da zaman na fito na ratsa motocin zan shiga part din Mama Fulani sai na soma jin kamshin wani turare mai dadi, da na taba ji sai dai ba zan iya tuna inda na ji shi ba. Tura kofar falon nai na shiga da sallamata babu wanda ya amsa min sai Ya Muhseen, Anty Maryam da Anty Rukaiya duk sun sha jinin jikinsu ko motsin kirki basa yi, Mama Fulani kuma na zaune a kujera daya da wani saurayi tana bare masa abaya ba tana mika masa, da na kalleshi da kyau sai na ga she mutumen da nai ma aiki kamin na dawo Abuja hakimce a kujera yana kallona da mugun mamaki.
*Z A K I -it's not free, pay 300 to 0314795884 Abubakar Gt bank, then send the evidence via 08036126660*
Idan ba ki biya ba karki karanta hakkin wani. Idan kuma kin ji zaki iya Bismillah.
20.
Ba ni kadai yake kallo ba, gaba dayan jikina da duk wani motsi takun da nake na karasa gurin da na saba zama na zauna yake kallo. Nima idona na kansa ina ta mamakin abunda ya kawo shi gida, da alama yana da kyakkyawar alaka da mutanen gidan, domin yadda na ga Mama Fulani na bare ayaba tana bashi yana ci kamar wani karamin yaro ya nuna yana da muhimmanci sosai a gareta duk da ban san alakarsu ba.
“Ke bana son kallo”
Ya fada yana kallona, sai duk suka juyo suka kalli inda na ke kokarin zama.
“Haka ta ke da shegen kallo kamar yar kauye”
Anty Maryam ta fada tana watsa min harara. Ya Muhseen yaja tsaki.
“Aliyu kana da matsala Wallahi, taya akai kai kaga tana kallon ka? Haka kawai za ka ce kar ta kalleka kai kuma ka kalleta?”
“How dare you zaka fada min wannan maganar sa'an ka ne ni?”
Aliyun ya fada yana mikewa tsaye cikin zafin rai kamar zai da ki Ya Muhseen. Ya Muhseen ya mike tsaye yana kara jan tsakin.
“Rayuwarku batai ba Wallahi, arziki ai ba hauka ba ne, shikenan dan tana talaka bata da gata kallon ma sai an shar'anta mata kalar da za tai?”
“Muhseen enough! Wai Aliyu ba yayanka ba ne kake fada masa wannan maganar?”
Mama Fulani ta fada tana mikewa tsaye tare da shiga tsakaninsu.
“Shikenan dan ya girmeni yayi ba daidai ba ba za ayi magana ba? Waye shi?”
“Amman ka san Aliyu ba ita ya hana kallonsa ba, ko su Maryam da Batulu da suke kannensa basa tsare shi da ido ko? Ina ruwanka da shi ne? Wai ku kullum kuka hadu a waje daya sai fada ya shiga tsakaninku? Kamar kare da Mage! Haba sai ka ce wasu abokan adawa”
Mama Fulani ta fada cikin yanayin da ke nuna damuwarta karara. Ya Muhseen be sake cewa komai ba ya watsawa Aliyu harara ya fice daga falon, sai da ya fice sannan Aliyu ya koma ya zauna sai ya maida idonsa a kaina, ni dai nai kasa da idona gudun kar Mama Fulani ta ce na yi laifi, amman idan ta shi ne bana tsoron duk abunda zai fada, lokaci zuwa lokaci idan na dago na sai na ga ni yake kallo, ka ji wani tsantsar zalinci amman ni ya ce ba zan kalleshi ba. A dago ta hudu da nai muka hada na watsa masa harara kadan sannan na maida idona kasa.
“Ke tashi ki fita bakar munafuka”
Mama Fulani ta fada min a tsawace tana watsa min harara, ba musu na tashi na fice daga falon, na koma garejen na zauna abuna ina ta jin zafin kalmar munafuka da Mama Fulani ta kira ni da ita. Zaune nai a gurin na rumgume hannayena ina turo baki kamar an min wani abun bayan wannan, ina jin motsin shigowar Ya Muhseen a garejin nai saurin gyara zamana.
“Pretty ta so muje part din Ammy”
Ya fada yana zuba duka hannayensa aljihu, ni kuma na mike tsaye na karasa inda yake ba tare da na san bakina yana nan a yadda na turo shi ba.
“Fushin ne har yanzu? Ki daina damuwa da lamarin Mama haka rayuwarta take, amman Aliyu idan yai miki ki rama”
“Idan na rama ai Mama Fulani fada za ta min, ko kuma shi ya dake ni”
“Ba zai dake ki ba, wai baya dukan mata sai maza, Aliyu ba shi da kirki ko kadan”
Ban sake cewa komai ba muka jero ni da shi muna tafiya har muka isa part din Ammy, Anty Humaira ce zaune ita da Inteesar suna playing wani gate da ke cikin plate da wani abu mulmulalle, kusa da Anty Humaira Ya Muhseen ya zauna ni kuma na zauna daga can gurin kofar shigowa falon ina kallonsu, Anty Humaira aka fara ci kamin aci Ya Muhseen abun gwanin sha'awa sai dariya na ke.
“Zo mu yi”