Sashe 2
Zaki Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Bance komai ba naja tsaki na cigaba da tafiyata, yo daman wa zance wa wani abu tunda ni kadai nake ta tafiya ta. A natse nake tafiya ta har na karyo kwanar dana saba bi idan zanzo gida, ina yanke hanya ne domin abun ya zo min da sauki, sai dai duk da haka ana kiran magariba na soma dosowa unguwarmu ta Clapperto road, a dai dai bakin gate din gidan dan Uti idanuwana sukai arba da kalar motar da wuce ta gabana dazun ta bata min tufafi, kuma wani abun dadi babu mutane a titi sai karar motocin dake kai da kawo.
Sai da naje gaban motar na leka gaba babu kowa a ciki, sannan na kara matsawa ina kara tabbatarwa idan ita dince ko aa, kalar dai daya ce sabuntar ma daya ce sai dai wannan anyi mata hoton ZAKI a jikin number motar kuma an rubuta mata ZAKI 001 da manyan haruffa tsabanin wacan da ban kula da number motar ba ma balle ma na san me aka rubuta.
Komawa nai ta inda na fito ina ta kalle kalle har na hango wani katon dutse da be fi karfina ba, na dauko na zo na jefawa motar ta gurin gilashinta, a take ta fara kuka, ni kuma na ranta cikin na kare, ai daman dai burina na dauki fansa, ko ba shine ya bata min tufafi ba be dame ni ba dan dan'uwansa ne mai kudi sai suji yadda ake ji...
Abunka da marar jiki nan da nan na karya kwana kwana ina ta sauri kamar an biyoni, tsoro ya saka na kasa mikewa kai tsaye na bi titi na isa gida, sai na shiga ta hanyar gidan taba (Gidan azaba) na bulla ta can kwantagora road na karyo ta wata hanyar, domin kawai wahala sannan na bullo da gidajen yan sanda da yake nan na biyo ta bayan gidan Alkali Abu dange wato gidansu Khadeeja Candy na fito titi Clapperto road na doshi gidanmu.
A inda na saba aje kayana na nufa na aje sannan na fito ina kirga kudin dake jakata, kamar ance na waigo ko da na juyo sai na hango wata halitta mai kyau da daukar hankali da kuma ban tsoro tana kallona. Mutum nake hange amman a siffa da fuskarsa, sai dai kwarjininsa da aibarsa kamar wani zaki. Nesa yake da ni amman fuskarsa zooming take min tana kawo min shi kusa kamar yana tsaye a gabana. Annuri ne shimfide a fuskarsa, sai dai ba irin na masu dariya da sakin fuska ba, irin wanda annurin ya zame masa jiki yake bayyana kansa a duk lokacin da mai shi ya kalleka, kwarjinsa ya cika min ido har kure ganina nake ganin kamar daga ni sai ainahin Zakin ne a jeji, wani abu mai zafi naji yana bin kafafunawa, ashe fitsari nake a tsaye ban sani ba, tsabar tsoro ya cika min ciki sai na fadi zaune a gurin na rufe idona kunya ce ta kamani budurwa kamar ni ace tai fitsari sai kuma naji ashe ba kunya ba ce tsoro ne.....
__________________
Who's ready for the next chapter?
#ZAKI
#Vote
#Share
#Comment.
Thanks Share Pls🙏🏻
*Z A K I*
By Khadeeja Candy
2️⃣
Mafarin ko wace Rayuwa numfashi da jini ne, ne numfashin da nake fitarwa ne ya tabbatar da cewar a raye na ke. Sai dai bana iya tantance yadda nawa numfashin yake a yanzu, domin surkinsa da wani kalar iska ne mai dadi shaka. A take na bude idona sai na hango gurin da mutumen yake tsaye kamar anyi ruwa an dauke domin babu alamarsa balle shi din yayi batan dabo bat kamar be taba wanduwa a gurin ba. Wata kila yaji tsoron fuska ta ne dake da bakin gawayi ko kuma rufen idon da nai ya tsorta shi, shiya saka yai hanzarin barin gurin.
Samun kaina nai da murmushin kaina saboda tsoron dana ji, na Lumashe ido ina shakar kamshin turare mai shiga har cikin kwakwalwa ya samawarda natsuwa ga marar ita ga mai ita kuma ya dada masa.
Na risina na dauke kudina da suka zube ina dariyar kaina, domin sai a yanzu abunda nai yake bani dariya na fashe gilashin motar mutane saboda mai motar ya watsa min ruwan kazanta a jiki, wata kila ma ba shi yai ba.
Lokacin dana hango mahaifiyata tana a gaban murhu sai farinciki da jindadi ya lullube ni, domin ba kasafai zaka zo ka tarar an dora girki a gidanmu ba, mun fi siyen garin kwaki mu jika ko muyi kwado (Datu) da kuli mu ci, idan wadatar tai mana yawa muna siyen kanzon tuwon dawa ko na shimkafa mu aje muna ci, hakan yasa na iya sarrafashi ta ko wace siga, idan nai jalof dinsa sam ba zaka ci ka dauka cewar kanzo ka ci ba har sai idan na fada. Ban saba shiga gidanmu da sallama ba, dan haka yin sallamar be dame ni ba sai kawai na karasa gurin mahaifiyata ya kai hannu na bude tukunyar dake kan wuta ina fadin.
“Nana me kike dafawa”
Ba shiri ya yada murfin sakamakon wani azababen zafi da naji a take yan yatsuna sukai ja, sai dai ganin taliya yasa ni manta zafin dana ji duk kuwa da irin halina na raki sai wani farincikin ya kara baibayeni har na hade yawu. Ina son taliya sosai musamman dafuwar masu kudi ba irin tamu ba da sai an sauke muke saka yaji da magi wani lokacin ka gishiri kawai za mu saka mu ci.
“Taliya ce nake dafawa”
Ta bani amsa itama fuskarta dauke da far'a.
“Ina kuka samu kudi?”
“Bayan fitarki Maman Maryam ta aiko mana da ita”
Na yi dariya ina saka hannuna a kwagirina dake kuguna na ciro duk kudin da nai na mika mata, ban san na rage ba balle har na cire wani abu ko da kuwa ina da bukatar siyen wani abu ne, har sai idan Nana ta dauka da kanta ta bani. Gaba daya kudin da nai a yau ba su wuce dari uku da yan canji ba, daman ba ko wace rana ce jumma'a ba.
“Wai Ataa ina kake zuwa baran ne? Kullum kudin da kake samowa be wuce wanda za si abinci da safe ba, da rana haka muke wuni babu komi a ciki inda ba Allah ya kawo mana wani abun ba”
Na yi shiru domin ban san me zan fada mata ba, tana da gaskiya a lokacin da take baran tana tara kudi mai yawa har ma ta siye wani abun ta aje, tsabanin yanzu dana hanata kuma ni bana iya kawo abun kwarai domin ni ba baran na ke ba.
“Nana kin san ni ban iya baran sosai ba, kuma bana son zuwa gurin manyan motoci ba”
“Ka gani Ataa ka cire wannan girman kan, ka raba kanka da girma kai ka ba dan kowa ba, idan za ka dage ka yi bara ka dage domin shi ne komai na mu”
Fada take min amman dariya nake, saboda yadda take kirana namiji kamar yadda take yi ma ko wace mace idan kuma namijin ne sai ta mayarda shi mace, domin ita har yanzu hausarta bata gama fita ba. Sai itama tai dariya domin ta san abunda nake yi ma dariya.
Daga haka na samu na shashantar da maganar na tashi na dauki fassashiyar butar mu na zagaya a inda muka killace na wanke fitsari sannan na fito na saka sabulu na wanke fuskata mai bakin gawayi nai alwala na shiga bukkarmu. Ban samu kanena Lukman a bukkar ba hakan ya tabbatar min da cewar yana islamiya kenan. Iyakar kokarin da nai na canja tufafin jikina ne na saka wasu sannan na soma rama azahar kamin na dora da la'asar. Ba tozarci ba, ni kadaina ina shakkar sallah da muke a bukkarmu domin na taba ji a lokacin da nake zuwa makaranta ana cewa Allah baya karba sai mai tsarki sai dai ban iya banbancewa ba tsarki na fitsari da janaba ko kuwa tsarki irin wannan na tsabtace daki. Babu wanda zai iya zama dakin mu yai minti biyar a ciki saboda zarnin fitsarin Lukma da kuma na kayan daudar da suke bukkarmu ga tarin kwanoni marasa marafe da kuma tarin gwangwayen da Nana take tarawa wai idan suka kai buhu uku zata siyar.
Ina sallamewa kunnuwana suka sato min muryar Lukma dake fadin.
“Nana kin dawo gurin baran?”
Juyo nai da sauri ina kallonsu daga inda nake zaune, daga ita har kanena basu san ina yi ba.
“Nana bara kike zuwa?”
“Ataa idan be je bara ba, da me zan dafa taliyar nan?”
Daga can gaban murhun ta amsa min kai tsaye. Wani abu na ji ya tsaya a kirji wanda ya saba tsaya min a duk lokacin da mahaifiyata taje bara.
“Amman Nana na fada miki zan rika yi ba”
“Ba inda kake zuwa kake zuwa (Nake) kai wani guri kake tafiya dabam”
Sai da naje gaban motar na leka gaba babu kowa a ciki, sannan na kara matsawa ina kara tabbatarwa idan ita dince ko aa, kalar dai daya ce sabuntar ma daya ce sai dai wannan anyi mata hoton ZAKI a jikin number motar kuma an rubuta mata ZAKI 001 da manyan haruffa tsabanin wacan da ban kula da number motar ba ma balle ma na san me aka rubuta.
Komawa nai ta inda na fito ina ta kalle kalle har na hango wani katon dutse da be fi karfina ba, na dauko na zo na jefawa motar ta gurin gilashinta, a take ta fara kuka, ni kuma na ranta cikin na kare, ai daman dai burina na dauki fansa, ko ba shine ya bata min tufafi ba be dame ni ba dan dan'uwansa ne mai kudi sai suji yadda ake ji...
Abunka da marar jiki nan da nan na karya kwana kwana ina ta sauri kamar an biyoni, tsoro ya saka na kasa mikewa kai tsaye na bi titi na isa gida, sai na shiga ta hanyar gidan taba (Gidan azaba) na bulla ta can kwantagora road na karyo ta wata hanyar, domin kawai wahala sannan na bullo da gidajen yan sanda da yake nan na biyo ta bayan gidan Alkali Abu dange wato gidansu Khadeeja Candy na fito titi Clapperto road na doshi gidanmu.
A inda na saba aje kayana na nufa na aje sannan na fito ina kirga kudin dake jakata, kamar ance na waigo ko da na juyo sai na hango wata halitta mai kyau da daukar hankali da kuma ban tsoro tana kallona. Mutum nake hange amman a siffa da fuskarsa, sai dai kwarjininsa da aibarsa kamar wani zaki. Nesa yake da ni amman fuskarsa zooming take min tana kawo min shi kusa kamar yana tsaye a gabana. Annuri ne shimfide a fuskarsa, sai dai ba irin na masu dariya da sakin fuska ba, irin wanda annurin ya zame masa jiki yake bayyana kansa a duk lokacin da mai shi ya kalleka, kwarjinsa ya cika min ido har kure ganina nake ganin kamar daga ni sai ainahin Zakin ne a jeji, wani abu mai zafi naji yana bin kafafunawa, ashe fitsari nake a tsaye ban sani ba, tsabar tsoro ya cika min ciki sai na fadi zaune a gurin na rufe idona kunya ce ta kamani budurwa kamar ni ace tai fitsari sai kuma naji ashe ba kunya ba ce tsoro ne.....
__________________
Who's ready for the next chapter?
#ZAKI
#Vote
#Share
#Comment.
Thanks Share Pls🙏🏻
*Z A K I*
By Khadeeja Candy
2️⃣
Mafarin ko wace Rayuwa numfashi da jini ne, ne numfashin da nake fitarwa ne ya tabbatar da cewar a raye na ke. Sai dai bana iya tantance yadda nawa numfashin yake a yanzu, domin surkinsa da wani kalar iska ne mai dadi shaka. A take na bude idona sai na hango gurin da mutumen yake tsaye kamar anyi ruwa an dauke domin babu alamarsa balle shi din yayi batan dabo bat kamar be taba wanduwa a gurin ba. Wata kila yaji tsoron fuska ta ne dake da bakin gawayi ko kuma rufen idon da nai ya tsorta shi, shiya saka yai hanzarin barin gurin.
Samun kaina nai da murmushin kaina saboda tsoron dana ji, na Lumashe ido ina shakar kamshin turare mai shiga har cikin kwakwalwa ya samawarda natsuwa ga marar ita ga mai ita kuma ya dada masa.
Na risina na dauke kudina da suka zube ina dariyar kaina, domin sai a yanzu abunda nai yake bani dariya na fashe gilashin motar mutane saboda mai motar ya watsa min ruwan kazanta a jiki, wata kila ma ba shi yai ba.
Lokacin dana hango mahaifiyata tana a gaban murhu sai farinciki da jindadi ya lullube ni, domin ba kasafai zaka zo ka tarar an dora girki a gidanmu ba, mun fi siyen garin kwaki mu jika ko muyi kwado (Datu) da kuli mu ci, idan wadatar tai mana yawa muna siyen kanzon tuwon dawa ko na shimkafa mu aje muna ci, hakan yasa na iya sarrafashi ta ko wace siga, idan nai jalof dinsa sam ba zaka ci ka dauka cewar kanzo ka ci ba har sai idan na fada. Ban saba shiga gidanmu da sallama ba, dan haka yin sallamar be dame ni ba sai kawai na karasa gurin mahaifiyata ya kai hannu na bude tukunyar dake kan wuta ina fadin.
“Nana me kike dafawa”
Ba shiri ya yada murfin sakamakon wani azababen zafi da naji a take yan yatsuna sukai ja, sai dai ganin taliya yasa ni manta zafin dana ji duk kuwa da irin halina na raki sai wani farincikin ya kara baibayeni har na hade yawu. Ina son taliya sosai musamman dafuwar masu kudi ba irin tamu ba da sai an sauke muke saka yaji da magi wani lokacin ka gishiri kawai za mu saka mu ci.
“Taliya ce nake dafawa”
Ta bani amsa itama fuskarta dauke da far'a.
“Ina kuka samu kudi?”
“Bayan fitarki Maman Maryam ta aiko mana da ita”
Na yi dariya ina saka hannuna a kwagirina dake kuguna na ciro duk kudin da nai na mika mata, ban san na rage ba balle har na cire wani abu ko da kuwa ina da bukatar siyen wani abu ne, har sai idan Nana ta dauka da kanta ta bani. Gaba daya kudin da nai a yau ba su wuce dari uku da yan canji ba, daman ba ko wace rana ce jumma'a ba.
“Wai Ataa ina kake zuwa baran ne? Kullum kudin da kake samowa be wuce wanda za si abinci da safe ba, da rana haka muke wuni babu komi a ciki inda ba Allah ya kawo mana wani abun ba”
Na yi shiru domin ban san me zan fada mata ba, tana da gaskiya a lokacin da take baran tana tara kudi mai yawa har ma ta siye wani abun ta aje, tsabanin yanzu dana hanata kuma ni bana iya kawo abun kwarai domin ni ba baran na ke ba.
“Nana kin san ni ban iya baran sosai ba, kuma bana son zuwa gurin manyan motoci ba”
“Ka gani Ataa ka cire wannan girman kan, ka raba kanka da girma kai ka ba dan kowa ba, idan za ka dage ka yi bara ka dage domin shi ne komai na mu”
Fada take min amman dariya nake, saboda yadda take kirana namiji kamar yadda take yi ma ko wace mace idan kuma namijin ne sai ta mayarda shi mace, domin ita har yanzu hausarta bata gama fita ba. Sai itama tai dariya domin ta san abunda nake yi ma dariya.
Daga haka na samu na shashantar da maganar na tashi na dauki fassashiyar butar mu na zagaya a inda muka killace na wanke fitsari sannan na fito na saka sabulu na wanke fuskata mai bakin gawayi nai alwala na shiga bukkarmu. Ban samu kanena Lukman a bukkar ba hakan ya tabbatar min da cewar yana islamiya kenan. Iyakar kokarin da nai na canja tufafin jikina ne na saka wasu sannan na soma rama azahar kamin na dora da la'asar. Ba tozarci ba, ni kadaina ina shakkar sallah da muke a bukkarmu domin na taba ji a lokacin da nake zuwa makaranta ana cewa Allah baya karba sai mai tsarki sai dai ban iya banbancewa ba tsarki na fitsari da janaba ko kuwa tsarki irin wannan na tsabtace daki. Babu wanda zai iya zama dakin mu yai minti biyar a ciki saboda zarnin fitsarin Lukma da kuma na kayan daudar da suke bukkarmu ga tarin kwanoni marasa marafe da kuma tarin gwangwayen da Nana take tarawa wai idan suka kai buhu uku zata siyar.
Ina sallamewa kunnuwana suka sato min muryar Lukma dake fadin.
“Nana kin dawo gurin baran?”
Juyo nai da sauri ina kallonsu daga inda nake zaune, daga ita har kanena basu san ina yi ba.
“Nana bara kike zuwa?”
“Ataa idan be je bara ba, da me zan dafa taliyar nan?”
Daga can gaban murhun ta amsa min kai tsaye. Wani abu na ji ya tsaya a kirji wanda ya saba tsaya min a duk lokacin da mahaifiyata taje bara.
“Amman Nana na fada miki zan rika yi ba”
“Ba inda kake zuwa kake zuwa (Nake) kai wani guri kake tafiya dabam”