Sashe 89
Zaki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kasa cewa komai Muhseen yai sai kallon Mama Fulani yake hawaye na sauko masa kamar ba shi ba. A fusace ta bar masa gurin ta haye sama dakinta. Ya dade zaune a gurin sannan ya mike tsaye ya nufi part dinsa, keys bude dakin ma daker ya iya sakawa ya bude yana shiga ya zube a falo zaune saman kananan cushion dinsa.
Abunda ya faru ne ya tsaya masa a rai, ta ina ne be kyautawa Momy ba? Miye illar abunda yai? Har ga Allah be ga da inda yake da wata matsala ba, Momy ta nuna masa son kai, kuma maganar da ya fada mata babu laifi a ciki, ta sani sarai yana son Ataa taya zata juyar abun akan Aliyu saboda yana danta? Ya sani be kyautawa Ataa na fada mata maganar kai tsaye a gaban mahaifiyarta ba, sai dai be san cewa mahaifiyarta bata sani ba da be aikata abunda ya aikata har ta furta kalmar tsana a gareshi ba, wannan babin kam ya yarda yayi kuskure amman da wanne zai ji rashin goyon bayan Momy ko kuwa yanke masa hukunci da mari da Mama Fulani tai, ko kuwa auren Ataa da Aliyu zai yi? Anya ma zai iya zai iya kallon Ataa da Aliyu a guri daya bayan shi ya fi cancanta ya zauna da ita? Domin shi ya ce yana son ta kuma yana da tabbacin tana son sa.
A daren be yi bachi ba duk kuwa da irin gajiyar da ke tattare da shi na tafiya mota amman tunani ya hana shi bachi kamar wacan karo, ta ina yake da matsala ina zai samu mafita? Ta ina zai shirya da Ataa? It's necessary ya koma sokoto ko gobe? Asubar fari ya fita daga gidan zuwa masallaci be dawo ba sai takwas da wani abu na safe, kamar zai wuce part dinsa sai kuka ya shigo part din Mama Fulani ita ya samu tana share falon da kanta Maryam da Rukaiya na zaune sai aikin danna waya suke.
“Mama ina kwana?”
Ta yi kamar ba ta ji shi ba sai cigaba tai da aikinta.
“Mama Muhseen na gaisheshe ki”
Maryam ta fada a zatonta bata ji abunda Muhseen yace ba ne.
“Na ji ai”
Ta fada ba tare da ta kalleshi ba. Shi kuma ya mike tsaye cikin rashin jindadi ya fice daga falon.“Gaskiya Mama be kamata ki ga laifin Ya Muhseen ba, har ga Allah Momy be kamata tai supporting Ya Aliyu ta bar Ya Muhseen ba”
Mama Fulani ta dago tana kallon Maryam wacce tai maganar tana nuna ta da tsintsiya.
“Baki san komai a kan rayuwar yara ba, babu ruwanki a ciki duk wanda zai ce kushe min Momy zai yi to zai jawa kansa bakin jini ne kawai, ai Aliyu ya fi cancantar karin aure yanzu fiye da Muhseen ko dan saboda Rahma, sannan Momy mai zaba masu matar aure ne, waya sani ko ta zaba masa wata ne shi Muhseen din ya ce baya so sai ta Aliyu, ai Amina ta fada min mafarin fadan duk akan wata yarinya ne”
“Haka ne kuma, su ma dai ban da abun su miye abun fada kan mace ga mata nan da yawa a gari, dama Ya Aliyu ya bar masa ko wacece ya zo ya auri Rukaiya”
“ai na ga kamar bata masa ne shiyasa ban matsa ba bana son abunda zai jawa Aliyu matsala, kuma namiji kara dai ka jira har kawo maka wacce yake so da wacce kai kake so, kin san dai duk yarinyar da Aliyu zai so classic lady ce, ai ko dan ya ba wa wannan yar iskar Rahma haushi zan zo ya aure ta”
Rukaiya ta yi kunce tana danna wayarta ta ce
“Uhmm ni jikina na ba ni Ataa ce suke wannan rigimar akanta Wallahi, kin san fa tun tana gidan nan suka fara wani zafi zafi akanta”
Mama Fulani ta dan yi shiru kamin ta kalli Rukaiyah.
“Ai ko kowa zai yi ban da Aliyu, ai sam ba zai taba son wannan banlagarar yarinyar ba”
“Mama tana da kyau fa sosai, kuma nan zai iya rudarsu, shi dai Ya Muhseen tun da a nan ai ya furta”
“Ai yau Momyn zata zo za mu idan ita ce din, amman ni nasan Aliyu ba zai taba son irin wannan yarinyar ba”
“Uhm Mama ba ki sani ba kenan, ai Wallahi Ya Aliyu zai iya jin cewar zai gyarata ya zauna da ita”
“Yarinyar da ke bara a titi dan Allah ki bar ma wannan maganar bakinki ya sari danyen kashi amman dai ba akan yayana ba Wallahi”
Mama Fulani ta karasa tana tofarda yawu, a take ranta ya bace domin ko maganar Ataa bata son a mata a yanzu sam ta ma manta da ita a duniyarta.Misalin goma na safe Momy da Aliyu suka sauka Abuja, suna sauka yai ma Nasir waya ya zo da mota ya dauke su zuwa gidan Mama Fulani, a motar ne Nasir yake karantar damuwar Aliyu domim tsakanin jiya zuwa yau har wata rama yai idonsa sun dan fada kana ganinsa kasan akwai damuwa a tare da shi, sai dai fuskarsa na nan a daure kamar ko yaushe. Suna isa gida Aliyu ya fara bude motar ya zai fita sai Nasir ya hana shi ta hanyar ce masa.
“Aliyu ina son mu yi magana da kai”
Jim hakan yasa shi zaunawa a motar Momy kuma ta bude gidan baya ta fita zuwa cikin gidan sai da ta shige sannan Nasir ya kalli Aliyu ya ce.
“Wani abun ne kuma ya sake faruwa?”
“Babu komai Nasir”
“Ga fuskarka nan ta nuna damuwa”
“Ina jin zaman jirgi ne”
“Zaman jirgi daga sokoto zuwa Abuja zai saka cikin damuwa”
“Babu wata damuwa a tare da ni Nasir kai ne kake ganin haka”
Yana fadar hakan ya fice daga motar zuwa cikin gidan, yana jin cewar matsalarsa da Rahma private matsala ne da ba lallai sai aminnsa ya ji irin zaman da suke ba, matsalarsa da Muhseen ma yana jin ta su ce ta cikin gida da wani be kamata ya ji ba, balle kuma na son Ataa daya hana shi walwala wata kila ma idan ya fada masa dariya zai masa.
Ko da ya shiga Momy na falo zaune ita da Mama Fulani ta jera mata fruits domin abincin rana be kai ba kuma bata jin zasu fito ba su karya ba. Kusa da Mama Fulani Aliyu ya zauna yana murmushi karfin hali.
“Mama ba ki fada min maganar Kamfanin nan ba sai a gurin Momy na ji”
“Ai da gangan na ki fada maka, wai ka tashi ta wuce sokoto ta waya ma kake fada min cewar ka wuce sokoto kai mai mata duk inda take kafarka na nan”
Dariya yai ya ahafa kansa yana kallon Maryam da Rukaiya da suka dauko kular farfesu Maryam kuma ta dauko plates da spoons. Maryam ce ta fara gaishe shi kamin Rukaiya ta dora da nata sai ya amsa musu fuska a hade kamar yadda ya saba.“Oh to sai na zuba masa ido yai miki rashin kunya kuma na kyale shi? Dan kin zaba masa mata ma ya isa ya ce ba zai aureta ba balle kuma dan kin zabawa Aliyu ita, yau ba ni burin da ya wuce na Aliyu ya kara aure”
“Wannan dalilin ne yasa na so Aliyu ya aureta amman ai Muhseen ya kasa fahimtata, kwana biyu da suka wuce Rahma dai fushi...... ”
Momy ta labartawa Mama Fulani abunda ya faru ciki har da jawabin da Mahaifiyar Rahma tai mata, a take ran Mama Fulani ya bace
“Uban me suke takama da shi a duniyar nan? Su har suna da bakin yi ma mutane iskanci? Ai shiyasa na ke son ya kara aure mu nunawa amaryar kauna in yaso ita sai ta mutu, ya yana bukatar aure ko Allah zai ba shi haihuwa ma, ta san da maganar auren ne? Amman zan cen ba aza ayi kishi da talaka ba kam tana da gaskiyarta wa yake son rabar talaka”
Momy ta hade yawun bakinta kana ta ce.
“Bata sani ba, yanzu haka tana dubai taje hutu”
“Ahhh hutu ko? Aiko kamin ta dawo za ayi auren nan, idan ma ni Aliyu zai dauki shawarata ya aika mata da saki kawai ni fa bana son rai ni”
“Ba sai ya sake ta ba, kin san halinndan ki ai ba lallai ne ya ce zai yarda ya sake ta ba, amman ko auren ya kara ai sai samu saukinta, amman yanzu ni na janye maganar auren ma kara dai ta zaba tsakanin shi da Muhseen duk wanda take kauna sai a aura mata shi idan ma wani take so ba shi ba sai a aura mata?”
“Wacece wai?”
“Ataa”
“Ataa”
Mama Fulani ta maimaita tana kallon Momy baki sake.
“Kam uban nan”
Ta daki kirji ta buga kafa da kasa.
“Dan Allah idan wasa kike ma ki daina”
“Babu zancen wasa a ciki Wallahi gaskiya na ke fada miki, Ataa ce”
“Ataa dai wacce tai aiki a karkashinmu? Ita ta samu wannan damar da har Muhseen da Aliyu suke ribibinta ko kuwa dai wata Ataa dabam, yar aikin gidansu? Yar talakawa yar bara a titi? Dan kari, ita ce kike cewa za ki bata dama ta zaba? Har kike tunanin bata Aliyu? Ko dai kin manta wacece ita?”“Miye abun mantuwa a ciki? Yarinyar da a hannuna ta ke yanzu, talauci ba illa ba ne”
“Aa Wallahi illa ne idan kina da talaucin anya kina ganin za ki iya shiga jirgi ki zo Abuja yau? Na dauka yar wata manyan mutane ce a cikin sokoto ko nigeria ma”
“A haka dai yayanki suke sonta”
“Lalala ban yarda ba, ina dalilin jayaya akan wannan banzar yarinyar? To ko dai ta shanye ku ne gaba daya? Daman ance buzayen nan mayu ne, ke kira min Aliyu yanzu nan”
Mama Fulani ta karasa tana kallon Rukaiya a take Rukaiya ta kira a waya ta sanar masa Mama Fulani na son ganinsa, daman yana garden yana ta kallon gurin da Ataa ta saba tsayawa ta wanke plate dinta gani yake kamar tana a gurin. Be bata lokaci ba ya shigo falon.
“Aliyu Ataa kake so? Ko kuwa Momy ce take son taka maka ita ta cilasta maka?”
Abunda ya faru ne ya tsaya masa a rai, ta ina ne be kyautawa Momy ba? Miye illar abunda yai? Har ga Allah be ga da inda yake da wata matsala ba, Momy ta nuna masa son kai, kuma maganar da ya fada mata babu laifi a ciki, ta sani sarai yana son Ataa taya zata juyar abun akan Aliyu saboda yana danta? Ya sani be kyautawa Ataa na fada mata maganar kai tsaye a gaban mahaifiyarta ba, sai dai be san cewa mahaifiyarta bata sani ba da be aikata abunda ya aikata har ta furta kalmar tsana a gareshi ba, wannan babin kam ya yarda yayi kuskure amman da wanne zai ji rashin goyon bayan Momy ko kuwa yanke masa hukunci da mari da Mama Fulani tai, ko kuwa auren Ataa da Aliyu zai yi? Anya ma zai iya zai iya kallon Ataa da Aliyu a guri daya bayan shi ya fi cancanta ya zauna da ita? Domin shi ya ce yana son ta kuma yana da tabbacin tana son sa.
A daren be yi bachi ba duk kuwa da irin gajiyar da ke tattare da shi na tafiya mota amman tunani ya hana shi bachi kamar wacan karo, ta ina yake da matsala ina zai samu mafita? Ta ina zai shirya da Ataa? It's necessary ya koma sokoto ko gobe? Asubar fari ya fita daga gidan zuwa masallaci be dawo ba sai takwas da wani abu na safe, kamar zai wuce part dinsa sai kuka ya shigo part din Mama Fulani ita ya samu tana share falon da kanta Maryam da Rukaiya na zaune sai aikin danna waya suke.
“Mama ina kwana?”
Ta yi kamar ba ta ji shi ba sai cigaba tai da aikinta.
“Mama Muhseen na gaisheshe ki”
Maryam ta fada a zatonta bata ji abunda Muhseen yace ba ne.
“Na ji ai”
Ta fada ba tare da ta kalleshi ba. Shi kuma ya mike tsaye cikin rashin jindadi ya fice daga falon.“Gaskiya Mama be kamata ki ga laifin Ya Muhseen ba, har ga Allah Momy be kamata tai supporting Ya Aliyu ta bar Ya Muhseen ba”
Mama Fulani ta dago tana kallon Maryam wacce tai maganar tana nuna ta da tsintsiya.
“Baki san komai a kan rayuwar yara ba, babu ruwanki a ciki duk wanda zai ce kushe min Momy zai yi to zai jawa kansa bakin jini ne kawai, ai Aliyu ya fi cancantar karin aure yanzu fiye da Muhseen ko dan saboda Rahma, sannan Momy mai zaba masu matar aure ne, waya sani ko ta zaba masa wata ne shi Muhseen din ya ce baya so sai ta Aliyu, ai Amina ta fada min mafarin fadan duk akan wata yarinya ne”
“Haka ne kuma, su ma dai ban da abun su miye abun fada kan mace ga mata nan da yawa a gari, dama Ya Aliyu ya bar masa ko wacece ya zo ya auri Rukaiya”
“ai na ga kamar bata masa ne shiyasa ban matsa ba bana son abunda zai jawa Aliyu matsala, kuma namiji kara dai ka jira har kawo maka wacce yake so da wacce kai kake so, kin san dai duk yarinyar da Aliyu zai so classic lady ce, ai ko dan ya ba wa wannan yar iskar Rahma haushi zan zo ya aure ta”
Rukaiya ta yi kunce tana danna wayarta ta ce
“Uhmm ni jikina na ba ni Ataa ce suke wannan rigimar akanta Wallahi, kin san fa tun tana gidan nan suka fara wani zafi zafi akanta”
Mama Fulani ta dan yi shiru kamin ta kalli Rukaiyah.
“Ai ko kowa zai yi ban da Aliyu, ai sam ba zai taba son wannan banlagarar yarinyar ba”
“Mama tana da kyau fa sosai, kuma nan zai iya rudarsu, shi dai Ya Muhseen tun da a nan ai ya furta”
“Ai yau Momyn zata zo za mu idan ita ce din, amman ni nasan Aliyu ba zai taba son irin wannan yarinyar ba”
“Uhm Mama ba ki sani ba kenan, ai Wallahi Ya Aliyu zai iya jin cewar zai gyarata ya zauna da ita”
“Yarinyar da ke bara a titi dan Allah ki bar ma wannan maganar bakinki ya sari danyen kashi amman dai ba akan yayana ba Wallahi”
Mama Fulani ta karasa tana tofarda yawu, a take ranta ya bace domin ko maganar Ataa bata son a mata a yanzu sam ta ma manta da ita a duniyarta.Misalin goma na safe Momy da Aliyu suka sauka Abuja, suna sauka yai ma Nasir waya ya zo da mota ya dauke su zuwa gidan Mama Fulani, a motar ne Nasir yake karantar damuwar Aliyu domim tsakanin jiya zuwa yau har wata rama yai idonsa sun dan fada kana ganinsa kasan akwai damuwa a tare da shi, sai dai fuskarsa na nan a daure kamar ko yaushe. Suna isa gida Aliyu ya fara bude motar ya zai fita sai Nasir ya hana shi ta hanyar ce masa.
“Aliyu ina son mu yi magana da kai”
Jim hakan yasa shi zaunawa a motar Momy kuma ta bude gidan baya ta fita zuwa cikin gidan sai da ta shige sannan Nasir ya kalli Aliyu ya ce.
“Wani abun ne kuma ya sake faruwa?”
“Babu komai Nasir”
“Ga fuskarka nan ta nuna damuwa”
“Ina jin zaman jirgi ne”
“Zaman jirgi daga sokoto zuwa Abuja zai saka cikin damuwa”
“Babu wata damuwa a tare da ni Nasir kai ne kake ganin haka”
Yana fadar hakan ya fice daga motar zuwa cikin gidan, yana jin cewar matsalarsa da Rahma private matsala ne da ba lallai sai aminnsa ya ji irin zaman da suke ba, matsalarsa da Muhseen ma yana jin ta su ce ta cikin gida da wani be kamata ya ji ba, balle kuma na son Ataa daya hana shi walwala wata kila ma idan ya fada masa dariya zai masa.
Ko da ya shiga Momy na falo zaune ita da Mama Fulani ta jera mata fruits domin abincin rana be kai ba kuma bata jin zasu fito ba su karya ba. Kusa da Mama Fulani Aliyu ya zauna yana murmushi karfin hali.
“Mama ba ki fada min maganar Kamfanin nan ba sai a gurin Momy na ji”
“Ai da gangan na ki fada maka, wai ka tashi ta wuce sokoto ta waya ma kake fada min cewar ka wuce sokoto kai mai mata duk inda take kafarka na nan”
Dariya yai ya ahafa kansa yana kallon Maryam da Rukaiya da suka dauko kular farfesu Maryam kuma ta dauko plates da spoons. Maryam ce ta fara gaishe shi kamin Rukaiya ta dora da nata sai ya amsa musu fuska a hade kamar yadda ya saba.“Oh to sai na zuba masa ido yai miki rashin kunya kuma na kyale shi? Dan kin zaba masa mata ma ya isa ya ce ba zai aureta ba balle kuma dan kin zabawa Aliyu ita, yau ba ni burin da ya wuce na Aliyu ya kara aure”
“Wannan dalilin ne yasa na so Aliyu ya aureta amman ai Muhseen ya kasa fahimtata, kwana biyu da suka wuce Rahma dai fushi...... ”
Momy ta labartawa Mama Fulani abunda ya faru ciki har da jawabin da Mahaifiyar Rahma tai mata, a take ran Mama Fulani ya bace
“Uban me suke takama da shi a duniyar nan? Su har suna da bakin yi ma mutane iskanci? Ai shiyasa na ke son ya kara aure mu nunawa amaryar kauna in yaso ita sai ta mutu, ya yana bukatar aure ko Allah zai ba shi haihuwa ma, ta san da maganar auren ne? Amman zan cen ba aza ayi kishi da talaka ba kam tana da gaskiyarta wa yake son rabar talaka”
Momy ta hade yawun bakinta kana ta ce.
“Bata sani ba, yanzu haka tana dubai taje hutu”
“Ahhh hutu ko? Aiko kamin ta dawo za ayi auren nan, idan ma ni Aliyu zai dauki shawarata ya aika mata da saki kawai ni fa bana son rai ni”
“Ba sai ya sake ta ba, kin san halinndan ki ai ba lallai ne ya ce zai yarda ya sake ta ba, amman ko auren ya kara ai sai samu saukinta, amman yanzu ni na janye maganar auren ma kara dai ta zaba tsakanin shi da Muhseen duk wanda take kauna sai a aura mata shi idan ma wani take so ba shi ba sai a aura mata?”
“Wacece wai?”
“Ataa”
“Ataa”
Mama Fulani ta maimaita tana kallon Momy baki sake.
“Kam uban nan”
Ta daki kirji ta buga kafa da kasa.
“Dan Allah idan wasa kike ma ki daina”
“Babu zancen wasa a ciki Wallahi gaskiya na ke fada miki, Ataa ce”
“Ataa dai wacce tai aiki a karkashinmu? Ita ta samu wannan damar da har Muhseen da Aliyu suke ribibinta ko kuwa dai wata Ataa dabam, yar aikin gidansu? Yar talakawa yar bara a titi? Dan kari, ita ce kike cewa za ki bata dama ta zaba? Har kike tunanin bata Aliyu? Ko dai kin manta wacece ita?”“Miye abun mantuwa a ciki? Yarinyar da a hannuna ta ke yanzu, talauci ba illa ba ne”
“Aa Wallahi illa ne idan kina da talaucin anya kina ganin za ki iya shiga jirgi ki zo Abuja yau? Na dauka yar wata manyan mutane ce a cikin sokoto ko nigeria ma”
“A haka dai yayanki suke sonta”
“Lalala ban yarda ba, ina dalilin jayaya akan wannan banzar yarinyar? To ko dai ta shanye ku ne gaba daya? Daman ance buzayen nan mayu ne, ke kira min Aliyu yanzu nan”
Mama Fulani ta karasa tana kallon Rukaiya a take Rukaiya ta kira a waya ta sanar masa Mama Fulani na son ganinsa, daman yana garden yana ta kallon gurin da Ataa ta saba tsayawa ta wanke plate dinta gani yake kamar tana a gurin. Be bata lokaci ba ya shigo falon.
“Aliyu Ataa kake so? Ko kuwa Momy ce take son taka maka ita ta cilasta maka?”