Sashe 60
Zaki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Daga Arkilla ya koma uduth din, duk wani abu da ake ma patient kamin a shiga da shi ganin likita shi yai kama daga karba kati da kaiwa a bude file. Sannan ya kira Doc Bukar ya fada masa cewar ya kawo ta har an shiga da ita ciki, ba bata lokaci Doc Bukar ya iso asibitin sai da Aliyu yai masa bayanin cewar matsalar koda ce sannan ya shiga dakin da aka kaita ya soma bata taimakon gaggauwa shi da wani likitan. Bayan sun fito Doc Bukar ya saka wasu nurses din suka kaita akai mata hoto a aka debi jininta sannan ya canja mata daki aka kaita wani dakin na musamman.
“Aliyu ya akai aka bar matar nan haka? Ciwon nan yana kokarin cinye ta?”
Lokacin da suka jero suka fito daga emergency ne Bukar ke masa wannan tambayar.
“I can't tell yanzu fada min ba zata samu sauki ba?”
“Zata samu mana, amman dole sai mun jira Doc Muhseen ya zo shi kadai zai mata aikin nan tun da Doc Mustapha yana waje, daman sune likitocin da suka fi kwarewa wannan fannin”
“Ka kira shi?”
“No na yi request a kira shi dai, ai ba mu muke kira ba, kuma ko bayan nata ai zai zo ya duba wasu patients daman amman sai next week”
“Kana tunanin zata kai gobe?”
“Yes zata iya kaiwa next year ma a haka, daman yanzu jini da ruwa ne abunda ta fi bukata, to mun saka mata ruwa jinin kuma na saka a bincika idan kawai wanda yai daidai da nata ko kuma zai iya zama a jikinta”
“Ka gwada nawa mana idan zai yi”
Doc Bukar ya kalleshi.
“Seriously?”
“Yes ina son rayuwar matar nan Bukar, ko me za ayi dai i need her alive”
“Then ka kira dan uwanka ka fada masa idan zai iya ya zo ya duba ta yau ma, idan yai mata aiki ina da tabbacin nan da two weeks zata koma normal”
Wani guntun numfashi Aliyu yaja ya sauke sannan ya kalli Doc Bukar din ya ce.
“Muje a gwada jinin”
Tare suka juya suka zuwa lap a can aka gwada jininsa da na Nana aka ga zai shiga sai ya kwanta aka cire gora uku a jikinsa aka sannan ya taso ya fito Doc Bukar ma bashi gangon madara.
“Ya jikin Rahma tana ta samun sauki dai ko?”
“Ka ji bata da lafiya ne?”
“Yes ba mahaifinta ya saka cigiya gurin likitoci cewar yana bukatar kodar siyarwa ba, sai dai samun koda yanzu ba abu ne mai sauki ba ba kowa ke iya siyarda wani bangare na jikinsa ba, kamar wannan maybe ita ta siyar muku da na farkon gashi yanzu sai an sake mata aiki”
Sai da Aliyu ya shaye madarar sannan ya jefar da gongon ya kalli Doc Bukar kamar zai yi magana sai kuma yai shiru dan yasan daya fadi gaskiya kara ma kawai yai shiru dan babu wanda zai yarda cewar ba da amincewar Doc Asim ya cire kodar ba.
“What is better now is ka kira Muhseen ka fada masa cewar kana da patient ya zo ya duba maka ita, na san zai yi ai”
“Zan kira”
Ya bashi amsa sannan ya rako shi har gurin motarsa ya shiga ya sannan Doc Bukar ya juya ya koma cikin asibiti Aliyu kuma ya amsa wayar da Rahma take masa.
“Aliyu ka shigo garin nan?”
“Eh”
“Amman ban sani ba”
“Shigowar dare nai, ya jikinki?”
“Aliyu yarinyar nan ka biyo ko?”
Yayi shiru be ce mata komai ba.
“Aliyu wai ba zaka fita harkar yarinyar nan ba? Shikenan daga yarinya ta zo tayi karya kai kuma ka zauna akai ka yarda cewar hakan din ne?”
“Babu ruwanki a cikin lamarin nan, ban nemi shawararki ba akaran kaina nake komai, and bana son yadda kike min magana kamar kina saka ni nai dole”
Ajiyar zuciya ta sauke daga can cikin wayar sannan ta dora da dalilin daya saka ta kirashi.
“Adamu mai gadi ya fada min wata ta zo zata siyar da kodarta kuma ka yi magana da ita ina take?”
“Ataa ce yarinyar da kike fada akanta, ta zo ta siyarda kodar dan kawai ta nema mahaifiyarta magani irin wannan yarinyar ce kike cewa kar a taimakawa? Haba Rahma”
Kashe wayar tai bata sake cewa komai ba, shi kuma ya sauke yana mai jin haushin abunda tai masa dan shi ba a kashe nasa waya sai dai shi ya kashe maka indai ba Momy ba ko Mama Fulani ko Abbah Daddy, sai ko Nasir shi ma kuma ba kullum ba. Sai ya tuka motar ya dauki hanyar gidansu Rahma dan zuwa ganinta and yana son yin wasu maganganun da ita, a dayan bangaren kuma yana jin kamar ya kira Muhseen yai masa magana, duk da yasan ba abune mai sauki a gareshi ba kiran Muhseen har yai requesting wani abu a gurinsa, he can't remember when last yai waya da shi, wani bangaren na zuciyarsa yana fada masa ya hakura kawai har sai next week idan Muhseen din ya zo, sai kuma yaji kamar ba zai iya kyale Nana a cikin wannan halin ba bayan sune silar shigarta halin kuma yana da yadda zai yi. Cikin wayarsa ya shiga ya nemo number Muhseen yana ta kallonta kamar ba zai kira ba, sai kuma sata zuciyar tace masa ya aika masa kawai da sako, wata kila kuma kiran ya fi dan zai fi daukar abun da muhimmanci, ba shi da wani zabi daya wuce kiran idan ma ya koma gida be san ta yadda Ataa zata dauki abun ba idan ya fada mata likitan da zai mata aiki sai next week zai zo wata kila ba zata yarda da shi ba. Ringing tai har ta katse Muhseen be dauka ba, bs karamin jihadi yai na sake kiransa tare da alkwarin idan har be daga ba ba zai sake kiransa ba, tana yin ringing daya Muhseen ya daga.
“Ya akai?”
Aliyu yai shiru na wani lokaci ba tare da yace komai ba tana jin zafin tambayar da Muhseen yai masa. Har Muhseen zai kashe wayar sai Aliyu ya ce.
“Akwai wata patient mai matsalar koda, ina son ka duba ta gobe”
“Yaushe ka zama ogana ne da har zaka ba ni umarni?”
Aliyu yai shiru be ce komai ba sai dantsar hakora yake gumi na karyo masa a take. Can Muhseen ya ce
“Idan ma wani abun ne ai ba kai zaka fada ba, daga can asibitin za a turo min mail, sai idan alfarma kake nema then say it”
A fusace Aliyu ya katse kiran ya gwammace yai hakan da ya furta neman alfarma a gurin kowa balle kuma Muhseen da furta hakan zai ba shi damar ganin ramarsa. Bacin ransa ne ya saka yaji ba zai iya zuwa gurin Rahma a haka ba, can din ma yasan ba bacin rai zai kwaso domin ba fahimtarsa zata yi ba. Canja hanya yai ya dauki hanyar da zata sadashi da Arkilla phone dinsa a dayan hannunsa yana driving da dayan, sako ya shigo wayarsa ta saman screen din ya karanta abunda Muhseen ya turo masa.
_Ka fara bawa Ataa wayar zan yi magana da ita then zan zo gobe_
Wani murmushin haushi Aliyu ya buga wayar a front seat yana wani irin huce how on earth Muhseen zai saka masa doka wai sai ya bawa Ataa ya yi waya da ita sannan zai zo, har ya isa gida be daina jin zuciyarsa na tafasa ba. A harabar gidan ya samu Momy zaune tana gyara giďa daman ta kan zauna wani lokacin har ita da Daddy ko da yara, tana ganin yadda Aliyu ya fito mota tasan akwai bacin rai a tare da shi, kai tsaye inda take zaune ya nufo ya zauna kusa da ita.
“Wai ni Muhseen zai sakawa doka?”
“Miya faru?”
A nan ya labarta mata abunda ya faru sai Momy tai murmushi.
“To yanzu kiran waya ka bata su yi magana shine wani abu?”
Yayi shiru be ce komai ba. Momy ta dauki wayarta ta kira Siyama tace ta fito tare da Ataa su same ta harabar gidan, a tare suka fito Siyama da Ataa sai dai Ataa ta fi sauri gurin karasowa gurin domin a tunaninta wani abun ne.
“Miya faru? Ina Nana”
“Waya za ki yi da Muhseen yanzu, shi zai zo ya duba Maman ki gobe”
Momy ta fada tana kiran Muhseen din waya. Sai da suka gaisa sannan ta ce masa.
“Ga Ataa din”
“Momy ba a wayarki na ke son magana da ita ba, a wayar Aliyu”
“Naga kamar duka daya ne ai”
“Na sani Momy amman wayarsa na ke so please”
Katse kiran Momy tai ta kalli Aliyu.
“Da wayarka yake son magana da ita, ka kira shi yanzu nan ka bata”
Har ya bude baki zai yi magana sai Momy ta tari numfashinsa.
“Umarni ne ka kira shi ka bata wayar ta ce”
Ta fada da kamar fada tana kallonsa fuskarta babu alamun wasa.
“Wayar tana mota”
“Je ka dauko”
Tashi yai ya nufi motar ya bude ya dauko wayar ya dawo ya zauna sannan ya kira Muhseen ya mikawa Ataa wayar. Bata karba ba ta tsaya kallonsa sai ya daka mata tsawa.
“Ki karba mana...!”
A razane ta mika hannu biyu ta karba idonta na kokarin cika da hawaye ta kara wayar a kunne.
“Karka sake daka mata tsawa balle kuma ka ce zaka nuna nata dan yatsa, bata jidadi a wani gurin ba ba zaka zo nan ka hana ta ba, abunda kake yi ma kannenka da kowa ita ba zan daukar maka ba”
Momy ta fada tana nuna shi da yatsa cike da jin haushin yadda ya razana ta sannan ta mike tsaye ta dauki gyaďarta ta bar masa gurin, dafe kansa yai a gurin har yanzu gumin bacin rai ne yake sauko masa.
Gaisawa Ataa ta fara yi da Muhseen cikin sautin kuka sai ya ce.
“Mi aka miki kike kuka?”
“Ba a min komai ba”
“Zan zo na duba Mamanki gobe kina so?”
“Eh”
“To zan zo, ki kula da kan ki kinji? Idan na zo za mu yi magana da ke”
“To”
Daga haka ya kashe wayar, sai ta mikawa Aliyu wayarsa.
“Gashi”
“Aliyu ya akai aka bar matar nan haka? Ciwon nan yana kokarin cinye ta?”
Lokacin da suka jero suka fito daga emergency ne Bukar ke masa wannan tambayar.
“I can't tell yanzu fada min ba zata samu sauki ba?”
“Zata samu mana, amman dole sai mun jira Doc Muhseen ya zo shi kadai zai mata aikin nan tun da Doc Mustapha yana waje, daman sune likitocin da suka fi kwarewa wannan fannin”
“Ka kira shi?”
“No na yi request a kira shi dai, ai ba mu muke kira ba, kuma ko bayan nata ai zai zo ya duba wasu patients daman amman sai next week”
“Kana tunanin zata kai gobe?”
“Yes zata iya kaiwa next year ma a haka, daman yanzu jini da ruwa ne abunda ta fi bukata, to mun saka mata ruwa jinin kuma na saka a bincika idan kawai wanda yai daidai da nata ko kuma zai iya zama a jikinta”
“Ka gwada nawa mana idan zai yi”
Doc Bukar ya kalleshi.
“Seriously?”
“Yes ina son rayuwar matar nan Bukar, ko me za ayi dai i need her alive”
“Then ka kira dan uwanka ka fada masa idan zai iya ya zo ya duba ta yau ma, idan yai mata aiki ina da tabbacin nan da two weeks zata koma normal”
Wani guntun numfashi Aliyu yaja ya sauke sannan ya kalli Doc Bukar din ya ce.
“Muje a gwada jinin”
Tare suka juya suka zuwa lap a can aka gwada jininsa da na Nana aka ga zai shiga sai ya kwanta aka cire gora uku a jikinsa aka sannan ya taso ya fito Doc Bukar ma bashi gangon madara.
“Ya jikin Rahma tana ta samun sauki dai ko?”
“Ka ji bata da lafiya ne?”
“Yes ba mahaifinta ya saka cigiya gurin likitoci cewar yana bukatar kodar siyarwa ba, sai dai samun koda yanzu ba abu ne mai sauki ba ba kowa ke iya siyarda wani bangare na jikinsa ba, kamar wannan maybe ita ta siyar muku da na farkon gashi yanzu sai an sake mata aiki”
Sai da Aliyu ya shaye madarar sannan ya jefar da gongon ya kalli Doc Bukar kamar zai yi magana sai kuma yai shiru dan yasan daya fadi gaskiya kara ma kawai yai shiru dan babu wanda zai yarda cewar ba da amincewar Doc Asim ya cire kodar ba.
“What is better now is ka kira Muhseen ka fada masa cewar kana da patient ya zo ya duba maka ita, na san zai yi ai”
“Zan kira”
Ya bashi amsa sannan ya rako shi har gurin motarsa ya shiga ya sannan Doc Bukar ya juya ya koma cikin asibiti Aliyu kuma ya amsa wayar da Rahma take masa.
“Aliyu ka shigo garin nan?”
“Eh”
“Amman ban sani ba”
“Shigowar dare nai, ya jikinki?”
“Aliyu yarinyar nan ka biyo ko?”
Yayi shiru be ce mata komai ba.
“Aliyu wai ba zaka fita harkar yarinyar nan ba? Shikenan daga yarinya ta zo tayi karya kai kuma ka zauna akai ka yarda cewar hakan din ne?”
“Babu ruwanki a cikin lamarin nan, ban nemi shawararki ba akaran kaina nake komai, and bana son yadda kike min magana kamar kina saka ni nai dole”
Ajiyar zuciya ta sauke daga can cikin wayar sannan ta dora da dalilin daya saka ta kirashi.
“Adamu mai gadi ya fada min wata ta zo zata siyar da kodarta kuma ka yi magana da ita ina take?”
“Ataa ce yarinyar da kike fada akanta, ta zo ta siyarda kodar dan kawai ta nema mahaifiyarta magani irin wannan yarinyar ce kike cewa kar a taimakawa? Haba Rahma”
Kashe wayar tai bata sake cewa komai ba, shi kuma ya sauke yana mai jin haushin abunda tai masa dan shi ba a kashe nasa waya sai dai shi ya kashe maka indai ba Momy ba ko Mama Fulani ko Abbah Daddy, sai ko Nasir shi ma kuma ba kullum ba. Sai ya tuka motar ya dauki hanyar gidansu Rahma dan zuwa ganinta and yana son yin wasu maganganun da ita, a dayan bangaren kuma yana jin kamar ya kira Muhseen yai masa magana, duk da yasan ba abune mai sauki a gareshi ba kiran Muhseen har yai requesting wani abu a gurinsa, he can't remember when last yai waya da shi, wani bangaren na zuciyarsa yana fada masa ya hakura kawai har sai next week idan Muhseen din ya zo, sai kuma yaji kamar ba zai iya kyale Nana a cikin wannan halin ba bayan sune silar shigarta halin kuma yana da yadda zai yi. Cikin wayarsa ya shiga ya nemo number Muhseen yana ta kallonta kamar ba zai kira ba, sai kuma sata zuciyar tace masa ya aika masa kawai da sako, wata kila kuma kiran ya fi dan zai fi daukar abun da muhimmanci, ba shi da wani zabi daya wuce kiran idan ma ya koma gida be san ta yadda Ataa zata dauki abun ba idan ya fada mata likitan da zai mata aiki sai next week zai zo wata kila ba zata yarda da shi ba. Ringing tai har ta katse Muhseen be dauka ba, bs karamin jihadi yai na sake kiransa tare da alkwarin idan har be daga ba ba zai sake kiransa ba, tana yin ringing daya Muhseen ya daga.
“Ya akai?”
Aliyu yai shiru na wani lokaci ba tare da yace komai ba tana jin zafin tambayar da Muhseen yai masa. Har Muhseen zai kashe wayar sai Aliyu ya ce.
“Akwai wata patient mai matsalar koda, ina son ka duba ta gobe”
“Yaushe ka zama ogana ne da har zaka ba ni umarni?”
Aliyu yai shiru be ce komai ba sai dantsar hakora yake gumi na karyo masa a take. Can Muhseen ya ce
“Idan ma wani abun ne ai ba kai zaka fada ba, daga can asibitin za a turo min mail, sai idan alfarma kake nema then say it”
A fusace Aliyu ya katse kiran ya gwammace yai hakan da ya furta neman alfarma a gurin kowa balle kuma Muhseen da furta hakan zai ba shi damar ganin ramarsa. Bacin ransa ne ya saka yaji ba zai iya zuwa gurin Rahma a haka ba, can din ma yasan ba bacin rai zai kwaso domin ba fahimtarsa zata yi ba. Canja hanya yai ya dauki hanyar da zata sadashi da Arkilla phone dinsa a dayan hannunsa yana driving da dayan, sako ya shigo wayarsa ta saman screen din ya karanta abunda Muhseen ya turo masa.
_Ka fara bawa Ataa wayar zan yi magana da ita then zan zo gobe_
Wani murmushin haushi Aliyu ya buga wayar a front seat yana wani irin huce how on earth Muhseen zai saka masa doka wai sai ya bawa Ataa ya yi waya da ita sannan zai zo, har ya isa gida be daina jin zuciyarsa na tafasa ba. A harabar gidan ya samu Momy zaune tana gyara giďa daman ta kan zauna wani lokacin har ita da Daddy ko da yara, tana ganin yadda Aliyu ya fito mota tasan akwai bacin rai a tare da shi, kai tsaye inda take zaune ya nufo ya zauna kusa da ita.
“Wai ni Muhseen zai sakawa doka?”
“Miya faru?”
A nan ya labarta mata abunda ya faru sai Momy tai murmushi.
“To yanzu kiran waya ka bata su yi magana shine wani abu?”
Yayi shiru be ce komai ba. Momy ta dauki wayarta ta kira Siyama tace ta fito tare da Ataa su same ta harabar gidan, a tare suka fito Siyama da Ataa sai dai Ataa ta fi sauri gurin karasowa gurin domin a tunaninta wani abun ne.
“Miya faru? Ina Nana”
“Waya za ki yi da Muhseen yanzu, shi zai zo ya duba Maman ki gobe”
Momy ta fada tana kiran Muhseen din waya. Sai da suka gaisa sannan ta ce masa.
“Ga Ataa din”
“Momy ba a wayarki na ke son magana da ita ba, a wayar Aliyu”
“Naga kamar duka daya ne ai”
“Na sani Momy amman wayarsa na ke so please”
Katse kiran Momy tai ta kalli Aliyu.
“Da wayarka yake son magana da ita, ka kira shi yanzu nan ka bata”
Har ya bude baki zai yi magana sai Momy ta tari numfashinsa.
“Umarni ne ka kira shi ka bata wayar ta ce”
Ta fada da kamar fada tana kallonsa fuskarta babu alamun wasa.
“Wayar tana mota”
“Je ka dauko”
Tashi yai ya nufi motar ya bude ya dauko wayar ya dawo ya zauna sannan ya kira Muhseen ya mikawa Ataa wayar. Bata karba ba ta tsaya kallonsa sai ya daka mata tsawa.
“Ki karba mana...!”
A razane ta mika hannu biyu ta karba idonta na kokarin cika da hawaye ta kara wayar a kunne.
“Karka sake daka mata tsawa balle kuma ka ce zaka nuna nata dan yatsa, bata jidadi a wani gurin ba ba zaka zo nan ka hana ta ba, abunda kake yi ma kannenka da kowa ita ba zan daukar maka ba”
Momy ta fada tana nuna shi da yatsa cike da jin haushin yadda ya razana ta sannan ta mike tsaye ta dauki gyaďarta ta bar masa gurin, dafe kansa yai a gurin har yanzu gumin bacin rai ne yake sauko masa.
Gaisawa Ataa ta fara yi da Muhseen cikin sautin kuka sai ya ce.
“Mi aka miki kike kuka?”
“Ba a min komai ba”
“Zan zo na duba Mamanki gobe kina so?”
“Eh”
“To zan zo, ki kula da kan ki kinji? Idan na zo za mu yi magana da ke”
“To”
Daga haka ya kashe wayar, sai ta mikawa Aliyu wayarsa.
“Gashi”