Sashe 75
Zaki Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
“Jiki Alhamdulillah, da gaske kai ne?”
“Yes ba gani kina ganina ba, ta ji sauki sosai?”
“Eh bata manta komai ba”
“Ina iya kokari na hada da addu'a a gurin aikin dan an samu na yi aikin cikin nasara, na san yadda uwa take da muhimmanci musamman ke da kike bukatarta, ina son ki rayu da mahaifiyarki duk kuwa da kin nuna min ba kya so na, amman ba son ne a gabana ba samun lafiyar mahaifiyarki ne a gabana”
Ya fada yana murmushi ni kuma na yi kasa da kaina ina taba kwalin dake saman cinyata.
“Ataa.... ”
Na dago na kalleshi.
“Bude kwalin”
Na bude kamar yadda ya bukata wani kyakkyawan zobe na fara cin karo da shi, a kasanshi kuma cake mai zagayen zuciya.
“Ban san size din yatsunki ba amman na san idan be miki yawa ba, ba zai miki kadan ba”“Zoben minene?”
“Na zinari ne”
Wani tsoron na ji na kamani daman tunda naga yanayin zoben ma dauka cewar na zinari ne, sai dai rashin ranin hakikanin zinarin yasa ban yi saurin yake hukunci ba har sai da ya fada min.
“Ni ban taba saka zinari ba”
“Kin fara kenan daga yau, ke din ai matar manya ce Ataa, ba dan ina son ki nake son ki saka zoben ba, sai dai kar ki manta da ni, a duk lokacin da kika tuna da samun lafiyar Nana ki min Addu'a Allah ya bani mata irin ki”
“Amman....”
“Karki ce komai Ataa pls ki saka dan Allah”
Akwa girma da nauyin a hada ka da Allah kuma ka saka yin abun nan, ko be hada ni da Allah ba mutumen da yai ma mahaifiyata tiyata ta samu sauki ya cancanci ya saka wani abun nai masa balle kuma ya hada da mahaliccina. Bude akwatin zoben nai ya fiddo daga ciki, sai da na kalli Muhseen sannan na saka zoben ina hade yawu gabana na bugawa da mugun karfi. Wani irin abu na ji ya ratsa ni, wata irin daraja da daukaka suka cika min ido, saurin cire zoben nai hawaye na sauko min.
“Ba zan iya sakawa ba Muhseen ka yi hakuri”
“Ba zan cilasta ki ba Ataa amman ki aje shi a gurinki”
Na gyada kai kamar yana gabana ina share hawayen.
“Upper week zan zo na yi ma wasu aiki, fada min abunda kike son na zo miki da shi, Mama Fulani ma ta ce na tambaye ki abunda kike so na zo miki da shi”
“Ni”
Na fada ina nuna kaina da tsananin mamaki.
“Yes baki yarda ba? Idan na koma zan fada mata ta kira ki da kanta”
“A a karka ce karka saka ta”
“To fada min abunda kike son na kawo miki”
Na yi shiru ina nazarin ban san mi zan ce masa ba.
“Kina son turare?”
“Eh ina so”Na amsa da sauri domin ya fanshe ni daga dogon tunanin abunda zan fada.
“To zan kawo miki, ki ci cake din kin ji?”
Na sake gyada masa kai ina kallon yadda yake kurba tea da ke gabansa. Murmushi ya sakar min kamin ya kai hannunsa ya taba wani gurin sai hotonsa ya bace bat. Mikewa nai tsaye ina rike da zoben da kuma cake din na fice daga dakin. Kadan kadan nake tafiya ina jim kalamansa kamar yanzu yake fada min su cewar Mama Fulani tace a tambaye ni abunda nake so, yafi komai bani mamaki da al'ajab, anya da gaske ma tace haka ko kuwa cewar Muhseen ne. Da wannan tunanin na shiga dakin da Nana take ina shiga na samu wata mace a tsaye tana sanye da yadi maroon da garin gyale, daga ganin yarinyar ka san budurwa ce ko da ganinta zata yi masifa.
“Ke ce Ataa?”
Ta tambaya tana zare min ido, gabana ne ya fadi har na kasa amsa mata na gyada mata kai kurum.
“To ki fita daga hanyar Aliyu domin ba makaskanci ba ne irinki, Aliyu ya fi karfin ko wace mace balle kuma ballagaza talaka irinki, yar bara a titi marar daraja....”
Yarinyar bata gama fada ba Nana ta daka mata tsawa da yaren buzanci tana zaburowa kamar ba tiyata ce a jikinta ba.
“Ke ya ishe ki”
Saurin karasa nai gurin Nana na dafata ina rufe mata baki. Sai yarinyar ta juyo ta kalli Nana ta ce
“Aniyar da biki idan ma wani abun ne kike karantawa ni na fi karfinki da duk danginki, kuma Wallahi Aliyu ma yafi karfinku duk wani abu yana muku shi a matsayin taimako amman shi kansa baya son kaskantacin mutane irin”
Mikewa nai tsaye ina nuna ta da yatsa na ce.
“Ke ce kaskantacciya domin da kina da wani matsayi a gurin Aliyu da kin hana shi taimakon ku ba sai kin zo kina mana ihu a cikin asibiti ba, jahilar banza wacce bata san darajar dan adam ba.... ”
Matsuwa yarinyar tai ya wanke min fuska da mari ta buge kwalin da ke dayan hannuna da zoben suka watse kasa.
“Lalala wato har da su zobe ya baki eh lallai zaki ci ubanki”
Ta nufi inda zoben yake ta dauka ni kuma na yi kanta na rama marin da ta min ina kuka sai juyo ta rikani ta buga da karfen gadon da Nana take kai a take kaina ya fashe da jini ya fadi zaune a gurin ina kuka, ita kuma tai ficewarta tana kwafa.
ZAKI
By Khadeeja Candy
36...
Ina zaune a gurin ina ta aikin rare kukana a hankali marar sauti sosai Nana na samam gadon ita tana hawaye, jini nata min zuba sosai har jiri na ke gani na kasa tashi a gurin kuma na kasa daga muryata na waje ya ji ya kawo min taimako. Sai bayan sallah la'asar Laraba ta dawo dakin tana ganin halin da nake ciki ta bugawa Momy a waya ta sanar da ita cikin tashin hankali. Ba a dauki lokaci ba Momy ta iso asibitin ina da Amina, tana ganin halin da nake ciki hankalinta ya tashi da sauri ta rikani ta fita da ni zuwa inda za a wanke min ciwon. A gaskiya ta nuna min kulawa sosai bayan sun wanke gurin suka ba ni magani ta biya kudin komai, ba ta dawo da ni dakin da Nana take ba, sai ta nufi motarta da ni, tana rike da ni har muka isa a gidan baya ta saka ni ita kuma ta shiga a front seat Amina ke tukawa, tun kan mu isa ta kira wayar Aliyu ta fada masa tana nemansa cikin fushi.
Da muka isa sai ta wuce ciki Amina ce ta rika ni muka shiga ciki, a saman kujera ta zaunar da ni ta cire min hijab babu nuna kyama ko gazawa a tare da Amina da mahaifiyarta, ruwa Momy ta ba ni mai dan zafi da lemun tsami a ciki a na sha sai ta dauki kofin na kwantar da kaina saman kujerar na lumshe ido ina sauraren yadda take fadawa su Husna da Siyama abunda ya faru cikin fada kamar yarta a aka taba.Mutanen nan biyu sun koya min wani darasi na rayuwa, kyamar talaka da Mama Fulani da 'ya'yanta da suke ra'ayi ne kawai na kansu ba dan talakan ya musu wani abun ba. So da kauna da kulawar da Momy ke nuna min ya karantar da ni wani halin dabam na dan adam. Momy ma masu arziki ne sosai amman bata taba nuna min kyama ba, ta san darajar talaka ba dan zata amfana da ni ba, sai dai tausayi da jin kai da ya cika zuciyarta, halin ne na dan'adam wani da dadin zama wani babu, wani da sanin darajar dan'adam wani babu, haka rayuwar take tafiya kowa da irin ra'ayinsa da halinsa da kuma tarbiyarsa, domin kuwa Husna da Siyama da Amina suna bin tarbiyar da Momy ta dora su akai ne, yayinda Yayan Mama Fulani suke bin tarbiyar da ta dora su akai, ban ce Muhseen da yake da wata rayuwar ta dabam wacce ta fidda shi dabam a cikin yayanta, yatsun hannunmu ma ba daya bane ta ita halin kowa zai zama daya.
Ina kwance na a gurin na ji kamshin turaren Aliyu wani irin turare mai kwnatar da hankali da saka nishadin ruhi, ina jindadin shakar kanshin sosai fiye da komai a yanzu.
Da sallamarsa ya shigo Momy ta ki amsa masa sai Husna ce ta amsa masa wanda hakan ke nuna cewar Momy tana cikin fushi sosai, tashi Husna tai ta nufi kitchen daman ita kadai ta rage a falon Siyama da Amina tuni suna shiga dakinsu dan yim wani sha'anin.
“Aliyu ka fadawa Matarka cewar kana son Ataa ne?”
Kallonta ya tsaya yi kamin ya tantance abunda ke fitowa daga bakinta.
“Son ta kuma? Kamar ya?”
“Wata taje ta taki akanka ta fada mata cewar idan bata fita daga sha'aninka ba sai ta mata illa, ta mareta kuma ta fasa mata kai”
“What”
“Yes ba gani kina ganina ba, ta ji sauki sosai?”
“Eh bata manta komai ba”
“Ina iya kokari na hada da addu'a a gurin aikin dan an samu na yi aikin cikin nasara, na san yadda uwa take da muhimmanci musamman ke da kike bukatarta, ina son ki rayu da mahaifiyarki duk kuwa da kin nuna min ba kya so na, amman ba son ne a gabana ba samun lafiyar mahaifiyarki ne a gabana”
Ya fada yana murmushi ni kuma na yi kasa da kaina ina taba kwalin dake saman cinyata.
“Ataa.... ”
Na dago na kalleshi.
“Bude kwalin”
Na bude kamar yadda ya bukata wani kyakkyawan zobe na fara cin karo da shi, a kasanshi kuma cake mai zagayen zuciya.
“Ban san size din yatsunki ba amman na san idan be miki yawa ba, ba zai miki kadan ba”“Zoben minene?”
“Na zinari ne”
Wani tsoron na ji na kamani daman tunda naga yanayin zoben ma dauka cewar na zinari ne, sai dai rashin ranin hakikanin zinarin yasa ban yi saurin yake hukunci ba har sai da ya fada min.
“Ni ban taba saka zinari ba”
“Kin fara kenan daga yau, ke din ai matar manya ce Ataa, ba dan ina son ki nake son ki saka zoben ba, sai dai kar ki manta da ni, a duk lokacin da kika tuna da samun lafiyar Nana ki min Addu'a Allah ya bani mata irin ki”
“Amman....”
“Karki ce komai Ataa pls ki saka dan Allah”
Akwa girma da nauyin a hada ka da Allah kuma ka saka yin abun nan, ko be hada ni da Allah ba mutumen da yai ma mahaifiyata tiyata ta samu sauki ya cancanci ya saka wani abun nai masa balle kuma ya hada da mahaliccina. Bude akwatin zoben nai ya fiddo daga ciki, sai da na kalli Muhseen sannan na saka zoben ina hade yawu gabana na bugawa da mugun karfi. Wani irin abu na ji ya ratsa ni, wata irin daraja da daukaka suka cika min ido, saurin cire zoben nai hawaye na sauko min.
“Ba zan iya sakawa ba Muhseen ka yi hakuri”
“Ba zan cilasta ki ba Ataa amman ki aje shi a gurinki”
Na gyada kai kamar yana gabana ina share hawayen.
“Upper week zan zo na yi ma wasu aiki, fada min abunda kike son na zo miki da shi, Mama Fulani ma ta ce na tambaye ki abunda kike so na zo miki da shi”
“Ni”
Na fada ina nuna kaina da tsananin mamaki.
“Yes baki yarda ba? Idan na koma zan fada mata ta kira ki da kanta”
“A a karka ce karka saka ta”
“To fada min abunda kike son na kawo miki”
Na yi shiru ina nazarin ban san mi zan ce masa ba.
“Kina son turare?”
“Eh ina so”Na amsa da sauri domin ya fanshe ni daga dogon tunanin abunda zan fada.
“To zan kawo miki, ki ci cake din kin ji?”
Na sake gyada masa kai ina kallon yadda yake kurba tea da ke gabansa. Murmushi ya sakar min kamin ya kai hannunsa ya taba wani gurin sai hotonsa ya bace bat. Mikewa nai tsaye ina rike da zoben da kuma cake din na fice daga dakin. Kadan kadan nake tafiya ina jim kalamansa kamar yanzu yake fada min su cewar Mama Fulani tace a tambaye ni abunda nake so, yafi komai bani mamaki da al'ajab, anya da gaske ma tace haka ko kuwa cewar Muhseen ne. Da wannan tunanin na shiga dakin da Nana take ina shiga na samu wata mace a tsaye tana sanye da yadi maroon da garin gyale, daga ganin yarinyar ka san budurwa ce ko da ganinta zata yi masifa.
“Ke ce Ataa?”
Ta tambaya tana zare min ido, gabana ne ya fadi har na kasa amsa mata na gyada mata kai kurum.
“To ki fita daga hanyar Aliyu domin ba makaskanci ba ne irinki, Aliyu ya fi karfin ko wace mace balle kuma ballagaza talaka irinki, yar bara a titi marar daraja....”
Yarinyar bata gama fada ba Nana ta daka mata tsawa da yaren buzanci tana zaburowa kamar ba tiyata ce a jikinta ba.
“Ke ya ishe ki”
Saurin karasa nai gurin Nana na dafata ina rufe mata baki. Sai yarinyar ta juyo ta kalli Nana ta ce
“Aniyar da biki idan ma wani abun ne kike karantawa ni na fi karfinki da duk danginki, kuma Wallahi Aliyu ma yafi karfinku duk wani abu yana muku shi a matsayin taimako amman shi kansa baya son kaskantacin mutane irin”
Mikewa nai tsaye ina nuna ta da yatsa na ce.
“Ke ce kaskantacciya domin da kina da wani matsayi a gurin Aliyu da kin hana shi taimakon ku ba sai kin zo kina mana ihu a cikin asibiti ba, jahilar banza wacce bata san darajar dan adam ba.... ”
Matsuwa yarinyar tai ya wanke min fuska da mari ta buge kwalin da ke dayan hannuna da zoben suka watse kasa.
“Lalala wato har da su zobe ya baki eh lallai zaki ci ubanki”
Ta nufi inda zoben yake ta dauka ni kuma na yi kanta na rama marin da ta min ina kuka sai juyo ta rikani ta buga da karfen gadon da Nana take kai a take kaina ya fashe da jini ya fadi zaune a gurin ina kuka, ita kuma tai ficewarta tana kwafa.
ZAKI
By Khadeeja Candy
36...
Ina zaune a gurin ina ta aikin rare kukana a hankali marar sauti sosai Nana na samam gadon ita tana hawaye, jini nata min zuba sosai har jiri na ke gani na kasa tashi a gurin kuma na kasa daga muryata na waje ya ji ya kawo min taimako. Sai bayan sallah la'asar Laraba ta dawo dakin tana ganin halin da nake ciki ta bugawa Momy a waya ta sanar da ita cikin tashin hankali. Ba a dauki lokaci ba Momy ta iso asibitin ina da Amina, tana ganin halin da nake ciki hankalinta ya tashi da sauri ta rikani ta fita da ni zuwa inda za a wanke min ciwon. A gaskiya ta nuna min kulawa sosai bayan sun wanke gurin suka ba ni magani ta biya kudin komai, ba ta dawo da ni dakin da Nana take ba, sai ta nufi motarta da ni, tana rike da ni har muka isa a gidan baya ta saka ni ita kuma ta shiga a front seat Amina ke tukawa, tun kan mu isa ta kira wayar Aliyu ta fada masa tana nemansa cikin fushi.
Da muka isa sai ta wuce ciki Amina ce ta rika ni muka shiga ciki, a saman kujera ta zaunar da ni ta cire min hijab babu nuna kyama ko gazawa a tare da Amina da mahaifiyarta, ruwa Momy ta ba ni mai dan zafi da lemun tsami a ciki a na sha sai ta dauki kofin na kwantar da kaina saman kujerar na lumshe ido ina sauraren yadda take fadawa su Husna da Siyama abunda ya faru cikin fada kamar yarta a aka taba.Mutanen nan biyu sun koya min wani darasi na rayuwa, kyamar talaka da Mama Fulani da 'ya'yanta da suke ra'ayi ne kawai na kansu ba dan talakan ya musu wani abun ba. So da kauna da kulawar da Momy ke nuna min ya karantar da ni wani halin dabam na dan adam. Momy ma masu arziki ne sosai amman bata taba nuna min kyama ba, ta san darajar talaka ba dan zata amfana da ni ba, sai dai tausayi da jin kai da ya cika zuciyarta, halin ne na dan'adam wani da dadin zama wani babu, wani da sanin darajar dan'adam wani babu, haka rayuwar take tafiya kowa da irin ra'ayinsa da halinsa da kuma tarbiyarsa, domin kuwa Husna da Siyama da Amina suna bin tarbiyar da Momy ta dora su akai ne, yayinda Yayan Mama Fulani suke bin tarbiyar da ta dora su akai, ban ce Muhseen da yake da wata rayuwar ta dabam wacce ta fidda shi dabam a cikin yayanta, yatsun hannunmu ma ba daya bane ta ita halin kowa zai zama daya.
Ina kwance na a gurin na ji kamshin turaren Aliyu wani irin turare mai kwnatar da hankali da saka nishadin ruhi, ina jindadin shakar kanshin sosai fiye da komai a yanzu.
Da sallamarsa ya shigo Momy ta ki amsa masa sai Husna ce ta amsa masa wanda hakan ke nuna cewar Momy tana cikin fushi sosai, tashi Husna tai ta nufi kitchen daman ita kadai ta rage a falon Siyama da Amina tuni suna shiga dakinsu dan yim wani sha'anin.
“Aliyu ka fadawa Matarka cewar kana son Ataa ne?”
Kallonta ya tsaya yi kamin ya tantance abunda ke fitowa daga bakinta.
“Son ta kuma? Kamar ya?”
“Wata taje ta taki akanka ta fada mata cewar idan bata fita daga sha'aninka ba sai ta mata illa, ta mareta kuma ta fasa mata kai”
“What”