Sashe 131
Zaki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
*Ina mata son rage kiba? Ina mazan da kiba ta hana su sukuni? Ina masu jikin yai kyau kamar na yarinya? Ina masu fama da kujera ko wani ta bo a fuska? Ina masu fama da hawan jini? Masu diabetic? Ag cera an gwada yayi an tantance ingancin babu shakku ko kadan. AG cera ya zo domin ya temaki garkuwan jiki da kuma lafiyar jiki. Sinadari ne wanda ze magance matsaloli da dama wadanda suke hana garkuwan jiki aiki yadda ya kamata ko kuma yake rusa garkuwan jikin ita kanta.*
*Cututtukan zamani daban daban sun sa mutane gaba kuma magance su yana da wahala; irin ciwon Sugar, hawan jini, ciwon sanyin kashi, ciwon gabobi da sauran su. Haka ma cutukka irin wadanda suka shafi fatar jikin wadanda sun hada da kyasfi, pimples, takurewar fata, rakainuwar fata da kuma haske da kyallin fata duka ana shan AG cera kuma yana temakawa wajen magance illolin nan. Mutane masu fama da rashin karfin jiki wajen kwanciya da iyali da kuma mata masu fama da yawan ciwon mara lokacin al'ada ta karshen wata suma baa bar su a baya ba. A takaice dai AG Cera yana temakawa wajen magance cuttukka daban daban wadan ke damun mutum. Domin karin bayani ku tuntuni mu a wannan number +60167474649 ko kuma ku ziyarci shafin mu http://agnutritioninternational.com.*
Da sauri Muhseen ya nufi inda Rahma take ya shiga dubata. Fita yai da sauri ya kira wasu likitocin suka shigo, sai ya ja hannun Aliyu ya fitar da shi waje, ya koma ciki shi da sauran likitocin biyu suka shiga bata taimakon gaggawa, amman ina rai yai halinsa mai abu ya karbi abarsa a lokacin da yake so kuma ya ga dama.
Aliyu na tsaye wajen kofar dakin ya kasa zaune ya kasa tsaye, sai safa da marwa yake jikinsa na zafi, gumi sai karyo masa yake zuciyarsa na bugawa da mugun karfi har ya kasa daidai ta numfashinta. Yana ganin Muhseen ya fito ya nufo shi da sauri ya tsaya a gabansa sai kuma ya kasa tambayarsa tana raye ko a mace, saboda yana tsoron irin amsar da Muhseen zai ba shi, shi ma Muhseen din sai ya kasa ce masa komai, be taba jin tausayin dan'uwansa kamar yau ba, be taba fargabar fada masa wata magana kai tsaye ba sai yau, be taba jin cewar idan yana da ikon da zai ma Aliyu wani abu da zai saka farinciki ba irin yau, ji yake kamar ace ikon dawo da rai a hannunsa yake da ya dawo da ran Rahma saboda Aliyu.
“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u”
Shine abunda Aliyu ya furta ya risina a gurin ya dafe kansa, ya san Rahmarsa ta tafi kenan, domin da ace tana da rai Muhseen ba zai yi fargabar fada masa ba. Muhseen ma risinawa yai ya dafa shi
“Aliyu”
Sai kuma ya kasa cewa komai, a lokacin da Aliyu ya dago ya kalli shi sai hawaye Muhseen ya gani a fuskar Aliyu ga wani kadewa da idonsa sukai su kai ja sosai.
“Allah be halicce kan Rahma ba, kuma be halicce Rahma dan kai ba, ba za a kara maka wa'adin mutuwarka ba idan lokaci yayi balle kuma a karawa Rahma dan ta rayu da kai, ka yi hakuri kuma kai hamdala ga wanda ya baka ita kuma a yanzu ya karbe ta”
Aliyu ya gyada kai tare da hade wani abu daya tsaya masa a makoshi ya mike tsaye yana share hawayensa, yana kallon Muhseen sai ga fuskar Rahma a fuskarsa, a take rayuwar da kai a da ta fara dawo masa, iyakar kokarin da yai na kawar da kansa daga barin kallon Muhseen ya fara takawa yana jin kamar ba tafiya yake ba saboda nauyin da kafafuwansa sukai masa, hannunsa ya kai ya rika ginin gurin yana maida numfashi a hankali wani abun ya tsaya masa a zuciya ya tokare masa. Da sauri Muhseen ya rika shi ya bude wani dakin da ke kusa da su ya shiga dashi ya zaunar da shi saman kujera. A take Aliyu ya lumshe ido ya bude bakinsa saboda samun taimakon numfashi, know one can express yadda Aliyu yake ji saboda be taba losing wani important person a rayuwarsa ba kamar yau, mamanshi tana raye, Mama Fulani na raye Daddy da Abbah duka suna raye, yana rayuwa da Rahma and he pray for Ataa Allah ya ba shi, bayan tarin dukiya da lafiya da Allah ya bashi, ga kuma samun cikin Ataa Allah ya bashi Allah ya hada masa goma da ashiri na farinciki duk shi kadai, be taba jin yadda ake jin zafin rasa wani ba, be taba sanin haka zafin rashi yake ba, be taba jin zafin rasa wani abu ba sai yau.
Muhseen ya fito da wayarsa ya kira Momy da Mama Fulani ya fada musu halin da ake ciki.
Cikin firgici da rudewa mahaifiyar Rahma ta shiga dakin da Rahma take ciki, ba kuka take ba domin ihun da take ya wuce a kira shi da kuka sai dai hargagi da kuwa.
“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u, na shiga uku na lalace Rahma ta tafi ta bar ni, La'ilaha illallahu”
Ikram da wata gwaggonsu na rikonta amman ta kasa yin shiru sai ihu take, har da tsalle tana direwa kasa, kaico mai rai bakon duniya, yau Rahma ta tafi kamar bata taba wanzuwa a duniya ba. Babu mai iya bayyana yadda Aliyu da mahaifiyar Rahma suke ji sai wanda ya taba rasa uwa ko uba miji ko mata, saboda sune the most important abu a rayuwar ko wane dan'adam. Cikin wani irin karfi Mahaifiyar Rahma take wai ko zata tashi, amman ina mai rai ya aiko an tafi da abunsa, daman can aro aka ba kowa, kuma ranar tafiyar tana nan zuwa komai daren dadewa. Ji take kamar ace tana da ikon dawo mata da rai da ta dawo mata da shi, da ace kudi suna maganin mutuwa a yau da ta cire ko nawa ne an bawa Rahma ranta ta dawo su yi rayuwa kamar da, ina ma tana da yadda za tai Rahma ta sake rayuwa. Fitowa akai da ita daga cikin dakin Ikram da Gwaggonsu suna ta kuka, ga Rahma kwance kamar tai magana amman babu numfashi ta zama gawa.
Kan kace kwabo kofar emergency ta cika da sisters din Rahma kowa sai kuka yake, ciki har da Momy da wasu yan'uwanta da ta dauko su rakota, ba mahaifiyar Rahma ce kadai abar tausayi ba har da yan'uwanta da Aliyu, domin kana kallonsu kasan suna cikin damuwa marar misaltuwa. Momy kan ciki ta wuce gurin Aliyu har lokacin yana nan zaune a dakin da Muhseen ya shiga da shi yana zaune baya kuka kuma ba hawaye idonsa sun yi ja sosai ga wani gumi da har yanzu be daina zubo masa ba.
Momy na shigo Aliyu ya kalleta da sauri kuma ya mike tsaye kamar zai yi magana da ita sai kuma ya kasa cewa komai. Karaso tai kusa da shi tana hawaye tana kallonsa. Sai ya rikata ya zaunar da ita ya zauna kasa ya dora kansa a kan cinyarta, auna rashin Rahma yake a ma'auni mai nauyi amman idan ya hada da Momy sai yaji nauyinta ya koma kamar bashi, da Momy ce ta mutu a yau da be san iya halin da zai shiga ba.
“Ka yi hakuri haka Allah ya so, haka yake a sadda ya so ga wanda ya zo babu wanda ya isa ya hana shi balle har ya tambaye shi dalilin yin haka, kai ma zaka mutu balle abunda ka mallaka ko ka aje”
Be ce komai ba bayan Lumshe ido da yai yana ta hade yawu ko abunda yake jin ya tsaya masa zai tafi. Sai kusan sha daya na safe suka bar asibitin tare da gawar Rahma suka nufi gidan iyayenta da ita. Babu wanda zai ga gawar Rahma ya ayyana cewar ta mutu har sai idan an fada masa ko kuma ta taba ya tabbatar, mai rai bawan Allah iyakar iskancin dan'adam idan yana da rai ne daga lokacin da aka zare rai daga jikinsa ya zama gawa yan'uwan ne za su saffara shi har a kai shi masaukinsa na gaskiya. Kowa ya yaba karfin halin Aliyu na yi ma matarsa wanka kuma yai mata surura kamar yadda addini.
“Allah ga Rahma nan, baiwar ka ce Allah yau ta dawo gareka aron ran da ka bata yau ka karbe abun ka ya Allah, Allah ina son matata ka sani, ita kuma tana so na, mun yi zaman aure da ita na shekaru tsabanin da muka samu atsakanina da ita na rashin jutuwa ko fada ko bacin rai da gangan ko cikin rashin sani Allah ka shaida na yafe mata, Allah kai ma ina rokon ka yafe mata, Allah jinyar da tai kasa ta zama sanadin tsira, Allah ka sadata mala'ikunka na Rahma ka sadata da Annabin Rahma, Allah ka hada ni da matata Aljanna”
Wannan karon be iya rike kansa ba ya fashe da kuka sosai kamar mace, har sai da aka shigo aka fita da shi, hankalin kowa be kara tashi ba sai da aka fito da ita akai mata sallah aka dauki gawarta zuwa makabarta inda gidanta na gaskiya yake kuma gidan kowa. Muhseen ne rike da Aliyu har aka kai makabarta aka saka ta cikin kabarinta, wa zai iya fadar yadda cikin kabari yake? Babu iyakar abunda ido ya gani ko ya ji a duniya ne kawai, the first thing da aka saka bayan gawar Rahma itace sannan aka saka tukane sai haki da ciyayi ya biyo baya, haka aka lullube kabarinta da kasa sai aka tabbatar babu wata kusurwa da wani abun zai iya shiga sannan aka kewaye kabarin ana mata addu'ar neman Rahma. Sannan aka taso aka baro ta can ita kadai daga ita sai aikinta. Gida aka kawo ana karbar gaisuwar, Momy kuma ta bukaci Aliyu ya koma gida su a can su yi na su karbar gaisuwar. Har lokacin Mama Fulani da Nasir ba su iso ba saboda mota suka biyo ba su samu jirgin da zai taso yau.
Aliyu na kusan shiga motarsa Ikram ta zo ta miko masa wata wasika, idonta yayi ja sosai.
“Minene?”
*Cututtukan zamani daban daban sun sa mutane gaba kuma magance su yana da wahala; irin ciwon Sugar, hawan jini, ciwon sanyin kashi, ciwon gabobi da sauran su. Haka ma cutukka irin wadanda suka shafi fatar jikin wadanda sun hada da kyasfi, pimples, takurewar fata, rakainuwar fata da kuma haske da kyallin fata duka ana shan AG cera kuma yana temakawa wajen magance illolin nan. Mutane masu fama da rashin karfin jiki wajen kwanciya da iyali da kuma mata masu fama da yawan ciwon mara lokacin al'ada ta karshen wata suma baa bar su a baya ba. A takaice dai AG Cera yana temakawa wajen magance cuttukka daban daban wadan ke damun mutum. Domin karin bayani ku tuntuni mu a wannan number +60167474649 ko kuma ku ziyarci shafin mu http://agnutritioninternational.com.*
Da sauri Muhseen ya nufi inda Rahma take ya shiga dubata. Fita yai da sauri ya kira wasu likitocin suka shigo, sai ya ja hannun Aliyu ya fitar da shi waje, ya koma ciki shi da sauran likitocin biyu suka shiga bata taimakon gaggawa, amman ina rai yai halinsa mai abu ya karbi abarsa a lokacin da yake so kuma ya ga dama.
Aliyu na tsaye wajen kofar dakin ya kasa zaune ya kasa tsaye, sai safa da marwa yake jikinsa na zafi, gumi sai karyo masa yake zuciyarsa na bugawa da mugun karfi har ya kasa daidai ta numfashinta. Yana ganin Muhseen ya fito ya nufo shi da sauri ya tsaya a gabansa sai kuma ya kasa tambayarsa tana raye ko a mace, saboda yana tsoron irin amsar da Muhseen zai ba shi, shi ma Muhseen din sai ya kasa ce masa komai, be taba jin tausayin dan'uwansa kamar yau ba, be taba fargabar fada masa wata magana kai tsaye ba sai yau, be taba jin cewar idan yana da ikon da zai ma Aliyu wani abu da zai saka farinciki ba irin yau, ji yake kamar ace ikon dawo da rai a hannunsa yake da ya dawo da ran Rahma saboda Aliyu.
“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u”
Shine abunda Aliyu ya furta ya risina a gurin ya dafe kansa, ya san Rahmarsa ta tafi kenan, domin da ace tana da rai Muhseen ba zai yi fargabar fada masa ba. Muhseen ma risinawa yai ya dafa shi
“Aliyu”
Sai kuma ya kasa cewa komai, a lokacin da Aliyu ya dago ya kalli shi sai hawaye Muhseen ya gani a fuskar Aliyu ga wani kadewa da idonsa sukai su kai ja sosai.
“Allah be halicce kan Rahma ba, kuma be halicce Rahma dan kai ba, ba za a kara maka wa'adin mutuwarka ba idan lokaci yayi balle kuma a karawa Rahma dan ta rayu da kai, ka yi hakuri kuma kai hamdala ga wanda ya baka ita kuma a yanzu ya karbe ta”
Aliyu ya gyada kai tare da hade wani abu daya tsaya masa a makoshi ya mike tsaye yana share hawayensa, yana kallon Muhseen sai ga fuskar Rahma a fuskarsa, a take rayuwar da kai a da ta fara dawo masa, iyakar kokarin da yai na kawar da kansa daga barin kallon Muhseen ya fara takawa yana jin kamar ba tafiya yake ba saboda nauyin da kafafuwansa sukai masa, hannunsa ya kai ya rika ginin gurin yana maida numfashi a hankali wani abun ya tsaya masa a zuciya ya tokare masa. Da sauri Muhseen ya rika shi ya bude wani dakin da ke kusa da su ya shiga dashi ya zaunar da shi saman kujera. A take Aliyu ya lumshe ido ya bude bakinsa saboda samun taimakon numfashi, know one can express yadda Aliyu yake ji saboda be taba losing wani important person a rayuwarsa ba kamar yau, mamanshi tana raye, Mama Fulani na raye Daddy da Abbah duka suna raye, yana rayuwa da Rahma and he pray for Ataa Allah ya ba shi, bayan tarin dukiya da lafiya da Allah ya bashi, ga kuma samun cikin Ataa Allah ya bashi Allah ya hada masa goma da ashiri na farinciki duk shi kadai, be taba jin yadda ake jin zafin rasa wani ba, be taba sanin haka zafin rashi yake ba, be taba jin zafin rasa wani abu ba sai yau.
Muhseen ya fito da wayarsa ya kira Momy da Mama Fulani ya fada musu halin da ake ciki.
Cikin firgici da rudewa mahaifiyar Rahma ta shiga dakin da Rahma take ciki, ba kuka take ba domin ihun da take ya wuce a kira shi da kuka sai dai hargagi da kuwa.
“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u, na shiga uku na lalace Rahma ta tafi ta bar ni, La'ilaha illallahu”
Ikram da wata gwaggonsu na rikonta amman ta kasa yin shiru sai ihu take, har da tsalle tana direwa kasa, kaico mai rai bakon duniya, yau Rahma ta tafi kamar bata taba wanzuwa a duniya ba. Babu mai iya bayyana yadda Aliyu da mahaifiyar Rahma suke ji sai wanda ya taba rasa uwa ko uba miji ko mata, saboda sune the most important abu a rayuwar ko wane dan'adam. Cikin wani irin karfi Mahaifiyar Rahma take wai ko zata tashi, amman ina mai rai ya aiko an tafi da abunsa, daman can aro aka ba kowa, kuma ranar tafiyar tana nan zuwa komai daren dadewa. Ji take kamar ace tana da ikon dawo mata da rai da ta dawo mata da shi, da ace kudi suna maganin mutuwa a yau da ta cire ko nawa ne an bawa Rahma ranta ta dawo su yi rayuwa kamar da, ina ma tana da yadda za tai Rahma ta sake rayuwa. Fitowa akai da ita daga cikin dakin Ikram da Gwaggonsu suna ta kuka, ga Rahma kwance kamar tai magana amman babu numfashi ta zama gawa.
Kan kace kwabo kofar emergency ta cika da sisters din Rahma kowa sai kuka yake, ciki har da Momy da wasu yan'uwanta da ta dauko su rakota, ba mahaifiyar Rahma ce kadai abar tausayi ba har da yan'uwanta da Aliyu, domin kana kallonsu kasan suna cikin damuwa marar misaltuwa. Momy kan ciki ta wuce gurin Aliyu har lokacin yana nan zaune a dakin da Muhseen ya shiga da shi yana zaune baya kuka kuma ba hawaye idonsa sun yi ja sosai ga wani gumi da har yanzu be daina zubo masa ba.
Momy na shigo Aliyu ya kalleta da sauri kuma ya mike tsaye kamar zai yi magana da ita sai kuma ya kasa cewa komai. Karaso tai kusa da shi tana hawaye tana kallonsa. Sai ya rikata ya zaunar da ita ya zauna kasa ya dora kansa a kan cinyarta, auna rashin Rahma yake a ma'auni mai nauyi amman idan ya hada da Momy sai yaji nauyinta ya koma kamar bashi, da Momy ce ta mutu a yau da be san iya halin da zai shiga ba.
“Ka yi hakuri haka Allah ya so, haka yake a sadda ya so ga wanda ya zo babu wanda ya isa ya hana shi balle har ya tambaye shi dalilin yin haka, kai ma zaka mutu balle abunda ka mallaka ko ka aje”
Be ce komai ba bayan Lumshe ido da yai yana ta hade yawu ko abunda yake jin ya tsaya masa zai tafi. Sai kusan sha daya na safe suka bar asibitin tare da gawar Rahma suka nufi gidan iyayenta da ita. Babu wanda zai ga gawar Rahma ya ayyana cewar ta mutu har sai idan an fada masa ko kuma ta taba ya tabbatar, mai rai bawan Allah iyakar iskancin dan'adam idan yana da rai ne daga lokacin da aka zare rai daga jikinsa ya zama gawa yan'uwan ne za su saffara shi har a kai shi masaukinsa na gaskiya. Kowa ya yaba karfin halin Aliyu na yi ma matarsa wanka kuma yai mata surura kamar yadda addini.
“Allah ga Rahma nan, baiwar ka ce Allah yau ta dawo gareka aron ran da ka bata yau ka karbe abun ka ya Allah, Allah ina son matata ka sani, ita kuma tana so na, mun yi zaman aure da ita na shekaru tsabanin da muka samu atsakanina da ita na rashin jutuwa ko fada ko bacin rai da gangan ko cikin rashin sani Allah ka shaida na yafe mata, Allah kai ma ina rokon ka yafe mata, Allah jinyar da tai kasa ta zama sanadin tsira, Allah ka sadata mala'ikunka na Rahma ka sadata da Annabin Rahma, Allah ka hada ni da matata Aljanna”
Wannan karon be iya rike kansa ba ya fashe da kuka sosai kamar mace, har sai da aka shigo aka fita da shi, hankalin kowa be kara tashi ba sai da aka fito da ita akai mata sallah aka dauki gawarta zuwa makabarta inda gidanta na gaskiya yake kuma gidan kowa. Muhseen ne rike da Aliyu har aka kai makabarta aka saka ta cikin kabarinta, wa zai iya fadar yadda cikin kabari yake? Babu iyakar abunda ido ya gani ko ya ji a duniya ne kawai, the first thing da aka saka bayan gawar Rahma itace sannan aka saka tukane sai haki da ciyayi ya biyo baya, haka aka lullube kabarinta da kasa sai aka tabbatar babu wata kusurwa da wani abun zai iya shiga sannan aka kewaye kabarin ana mata addu'ar neman Rahma. Sannan aka taso aka baro ta can ita kadai daga ita sai aikinta. Gida aka kawo ana karbar gaisuwar, Momy kuma ta bukaci Aliyu ya koma gida su a can su yi na su karbar gaisuwar. Har lokacin Mama Fulani da Nasir ba su iso ba saboda mota suka biyo ba su samu jirgin da zai taso yau.
Aliyu na kusan shiga motarsa Ikram ta zo ta miko masa wata wasika, idonta yayi ja sosai.
“Minene?”