Sashe 126
Zaki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da zahar muka isa lagos, wani kyakkyawan gida aka kai sauke mu, gida ne nadaidaicin mai kyau wanda aka kawata da shuke shuke gwanin sha'awa. A nan muka gaisa da Mai Martaba muka ci abinci muka huta sannan aka zo aka dauki mu aka tafi da mu wani gurin aka dauki hoton mu da tambarin yatsun mu akai wasu abubuwan da ban san ma'anarsu ba sannan aka dawo da mu. Bayan mun dawo Aliyu ya kira Momy ya ba ni muka gaisa har ta ke ce min na kula da kaina kuma na gaishe da kowa da yake can, ya bawa Mama ita ma ta gaisa da ita sannan ya kira Daddynsa shi ma muka gaisa kamar yadda ya fara gaisawa da shi, Abbah ya biyo baya shi da Mama Fulani sai a lokacin ya sanar musu mun iso lagos lafiya kalau.
Ba mu bar lagos ba sai da la'asar sannan muka shiga jirgin Mai martaba zuwa nijar, ni da Aliyu muna zaune a kujera daya daga can baya, Mama da Mai Martana kuma suna zaune a wata kujera mai kamar dinning wacce kowa ke iya kallon kowa ga wani dan karamin tebur a tsakani, bayan wadancan jikokin da ya zo da su wato Yusuf da kuma dayan da na ji Nana ta kira sunansa da Abdallah na ga su ma da ban san fuskarsu ba sai yau. Ban san awa nawa ne daga nigeria to Nijar ba, mota balle kuma a jirgin sama, sai dai na yi bachi a cikin jirgin a kafadar Aliyu sau biyu ina farkawa sai kuma nai bachin, abincin da aka ba mu a jirgin kin ci nai duk kuwa da kasancewar na mu ne irin wanda na saba ci yau da kullum amman sai naji bana ma kaunar warin abinci. Aliyu ma Ginger tea kawai ya sha sai wani biscuit na alkama, ni dai ko ruwa da ban sakawa cikina ba har muka sauka. A nan ma akwai banbancin lokaci da can kamar dai yadda mukai wacan tafiyar zuwa Las Vegas sai dai wannan ba tai nisa wacan ba ko kadar nisanta bata kamo ba, wata kila kuma saboda mun sauka da dare ne na ke ganin kamar lokacin da banbanci. Mama da Mai Martaba su suka fara fita daga jirgin tare da masu take masa baya wato fadawansa, sannan ni da Aliyu muka fito sai kuma sauran suka fito. Tun daga yanayin filin jirgin zaka fahimci ba a Nigeria kake ba, domin yawacan mutunen da suk can shigarsu daban ce da wadanda suke airport din Nigeria.
Motar biyar aka jera a filin jirgin ban yi zaton na Mai marta ne ba har da na ga ya doshi can wasu fadawan sun fito daga motar da sauri suna tarbarsa, motar da ya shiga dabam da wacce mu muka shiga. Duka motocin bakake ne masu bakim gilashi a hankali suke tuka motar har muka hau babbar hanyar garin. Yawacan mutanen da na ke kallo a titi da inda muke wucewa mafi yawansu suna sanye da rawani da ginuka su sum sha banban da na Nigeria domin su zaka ga wasu ginin na su tun na al'ada ne ba su zamanantar da shi ba, wasu kuma an kawata su kamar garin sokoto.
Tun daga unguwar da muka shiga na gane cewar ana yin sarkin a unguwar yadda na ga mutane suna tsayawa kallonsa da daga masa hannu da masa kirari a cikin yaren buzanci. Wata irin katuwar masarauta muka shiga mai haske kamar rana sakamakon kwan lantarki da aka saka ta ko'ina, ga kuma ginin da zanen masarautar irin an al'adar masarautar mai hawa biyu ce, wani bangaren kuma hawa daya ne, ga fadi kamar wata unguwa dukam wadanda suke cikin masarautar daga mai rawani sai mai hula manya da yara, mutane da dama suka fito daga cikon gidan zuwa inda aka faka motarmu suna mana lalle marhabun a cikin kuwa har da manyan mazan da nake saka ran yayun Mama ne, ganinta ya bawa kowa, sai Mai Martaba ya fito sannan ta fito, muma muka fito ni dai sai wara ido na ke abun ka da bakauyen mutum kuma mai son ganin masarauta. Kowa mamakin ganin Mama yake wasu kuma kallonta kawai suke wanda hakan ke nuna cewar ma su kallon nata ba su santa ba ne ko kuma sun manta, domin matasa me ko da yake a akwai manya a ciki, sauran kan mamaki ya hana su magana, ta yadda na ga suna mamakin ne ya fahimtar da ni cewar Mai marta be fada musu cewar ya hadu da Mama ba sai dai zuwan da yai da ita na ba zata. Tare da Aliyu muka karasa gurin da Mama take tsaye shi kan Mai martaba tuni yayi cikin fadarsa tare da manyan amsu take masa baya, Mama kuma ta fashe da kuka har sai da aka rakata a ka shiga da ita ciki.
Nima hawayen na ke har muka shiga cikin katuwar fadar wacce akaiwa ado da kwalliya irin ta mutanen da sai dai an zamanantar da adon ta yadda zai burge kowa gwanin sha'awa. Kwatatan fadin fadar da girma ta abu ne mai wahala ga mutum irina ne, domin kallon kwaliyar fadar ya hana ni tsayawa na lura da wadanda suke cikin fadar ma. Ban an kara da hakan ba har sai da masu yi ma Mai martaba kirarin cikin yalshen buzanci suka hankato da ni na dawo daga duniyar kallon fadar. Ashe tuni Mai Martaba yai gaba ni da Aliyu da wasu masu take mana baya tafiya muke zuwa wani bangare na fadar ban sani ba. Duk inda muka bi indai da mutane wasu kallon tausayi suke mana wasu kuma kallo ne akwai ma Mamaki, Mama kan sai aikin kuka take ni kuma ina taya ta da hawaye har muak shiga cikin gidan ni da ita da kuma Aliyu. Shi ka Mai Martana tuni ya kama wata hanyar dabam, Yusuf ne yake mana ja gaba har muka shiga inda Mata da yaya da yawa suke. A tsakar gidan Mama ta gurfana ta fashe da wani sabon kuka mai taba zuciya, matan gaba daya suka zagaye ta suna kallonta kamin wasu su kama ta su shiga da ita ciki ciki. A bangaren da ke farko aka shiga da ita wanda na ke kyautata zaton na mahaifiyarta ne ganin hoton Mai Martaba da wasu da ga kuma wati dattijiwa wacce tuni ta kawo bakin kofar falon tana kuka sosai har da saka hannunta ta dafe zuciyarta, Mama ta fadi a bakin kofar tana rike da hannun matar matar ma ta rike hannun Mama gam tana kuka sosai, ba ni kadai ba kowa da ke gurin sai da ya tausawa Mama da matar saboda kukan da suke da kuma wasu ma har da kukan sai da sukai.
“Nana ce ta dawo, Nana ce, Nana, Nana”
Shine abunda yawancin matan da ke gurin suke fadi tare da wasu dattijan mazan, wadanda suka tsaya rumgume da hannunsu suna kallon Mama. Sai da akai ta ba su hakuri sannan Mama ta tsagaita kukan da take ta shiga cikin katon falon wanda sanyin ac da kamshin turare ke maka lale marhabun. Muma shiga cikin falon ni da Aliyu sai aka dawo kan mu ana ta kallon mu wasu har da bude baki, ina jin lokacin da wasu ke fadar ni da Aliyu duka yayanta ne wai Aliyu ne yaya ni kanwa, wasu kuma su ce rakota mu kai. A lokacin da Dattijiwar ta zauna a falon sai ta daga kanta sama hawaye nata mata zuba sai girgiza kai take.
“Mama ki yafe min, Mama ban kyauta miki ba aikata daidai ba, kuma ban kyautawa kaina ba na sani, kuma na cancanci ko wane irin hukunci ko fushi daga gareki”
Mama ce take fadin haka tana daga kasa zaune rike da hannun matar tana kuka, matar ma kukan take irin na tsofi gwanin ban tausayi da taba zuciya, ta hanyar kalaman da Mama take na fahimci cewar dattijiwar Mahaifiyarta ce duk kuwa da kasancewar ba a su yi kama sosai ba domin Mama ta fi kama da Mai Martaba.
RAHMA POV.
daga idonta har makoshinta da fatar jikinta abushe suke kamar wacce. Ta shekara ashirin a gadon asibiti, kallo daya zaka mata ka fahimce akwai damuwa sosai a cikin zuciyarta, tun daga lokacin da aka kawo ta asibiti ta farka bata ce da kowa komai ba, ciki kuwa har da mahaifiyarta da ke kai da kawo tana yawan tambayarta idan tana bukatar wani abun, sai dai ta gyada kai ko ta girgiza, likitan da ya zo dubata ma sai dai ta girgiza masa kai ko ta gyada kai, rashin maganar ya damu kowa domin an kasa gano matsalar rashin maganar tunda tana ji maganar ce kawai bata furtawa, wata kila damuwarta da ke ranta ce ta hana ta magana da kowa ko kuma wani ciwon ne, na daban ya same ra a yanzu.
“Ya kamata a sanar da mijinta Mommyn wannan abun, tun da ta tashi ba tai magana ba, idan kuma aka takura da magana ta fara hawaye wannan abun yayi yawa”
“Ya san da ita ai, tun da yai aure be waiwaye ba, idan ma ya zo ba wani maganin zai mata ba, koda ce take bukata kuma ta mu In-Sha-Allah”
Mahaifiyarta ta mayarwa da Ikram amsa cikin hawaye, kallonsu kawai Rahma ke yi ba tare da tace komai ba.
“Ko jiya ya kirata amman ban daga ba saboda ban san mi zan fada masa ba, amman kyaleta a haka ba shine mafita ba, ya kamata ace ya san matarsa tana asibiti ko da ba zai mata komai ba”
“Idan ya kira ki daga ki fada masa cewar matarsa bata da lafiya tana asibiti”
“To Mommy”
Ba mu bar lagos ba sai da la'asar sannan muka shiga jirgin Mai martaba zuwa nijar, ni da Aliyu muna zaune a kujera daya daga can baya, Mama da Mai Martana kuma suna zaune a wata kujera mai kamar dinning wacce kowa ke iya kallon kowa ga wani dan karamin tebur a tsakani, bayan wadancan jikokin da ya zo da su wato Yusuf da kuma dayan da na ji Nana ta kira sunansa da Abdallah na ga su ma da ban san fuskarsu ba sai yau. Ban san awa nawa ne daga nigeria to Nijar ba, mota balle kuma a jirgin sama, sai dai na yi bachi a cikin jirgin a kafadar Aliyu sau biyu ina farkawa sai kuma nai bachin, abincin da aka ba mu a jirgin kin ci nai duk kuwa da kasancewar na mu ne irin wanda na saba ci yau da kullum amman sai naji bana ma kaunar warin abinci. Aliyu ma Ginger tea kawai ya sha sai wani biscuit na alkama, ni dai ko ruwa da ban sakawa cikina ba har muka sauka. A nan ma akwai banbancin lokaci da can kamar dai yadda mukai wacan tafiyar zuwa Las Vegas sai dai wannan ba tai nisa wacan ba ko kadar nisanta bata kamo ba, wata kila kuma saboda mun sauka da dare ne na ke ganin kamar lokacin da banbanci. Mama da Mai Martaba su suka fara fita daga jirgin tare da masu take masa baya wato fadawansa, sannan ni da Aliyu muka fito sai kuma sauran suka fito. Tun daga yanayin filin jirgin zaka fahimci ba a Nigeria kake ba, domin yawacan mutunen da suk can shigarsu daban ce da wadanda suke airport din Nigeria.
Motar biyar aka jera a filin jirgin ban yi zaton na Mai marta ne ba har da na ga ya doshi can wasu fadawan sun fito daga motar da sauri suna tarbarsa, motar da ya shiga dabam da wacce mu muka shiga. Duka motocin bakake ne masu bakim gilashi a hankali suke tuka motar har muka hau babbar hanyar garin. Yawacan mutanen da na ke kallo a titi da inda muke wucewa mafi yawansu suna sanye da rawani da ginuka su sum sha banban da na Nigeria domin su zaka ga wasu ginin na su tun na al'ada ne ba su zamanantar da shi ba, wasu kuma an kawata su kamar garin sokoto.
Tun daga unguwar da muka shiga na gane cewar ana yin sarkin a unguwar yadda na ga mutane suna tsayawa kallonsa da daga masa hannu da masa kirari a cikin yaren buzanci. Wata irin katuwar masarauta muka shiga mai haske kamar rana sakamakon kwan lantarki da aka saka ta ko'ina, ga kuma ginin da zanen masarautar irin an al'adar masarautar mai hawa biyu ce, wani bangaren kuma hawa daya ne, ga fadi kamar wata unguwa dukam wadanda suke cikin masarautar daga mai rawani sai mai hula manya da yara, mutane da dama suka fito daga cikon gidan zuwa inda aka faka motarmu suna mana lalle marhabun a cikin kuwa har da manyan mazan da nake saka ran yayun Mama ne, ganinta ya bawa kowa, sai Mai Martaba ya fito sannan ta fito, muma muka fito ni dai sai wara ido na ke abun ka da bakauyen mutum kuma mai son ganin masarauta. Kowa mamakin ganin Mama yake wasu kuma kallonta kawai suke wanda hakan ke nuna cewar ma su kallon nata ba su santa ba ne ko kuma sun manta, domin matasa me ko da yake a akwai manya a ciki, sauran kan mamaki ya hana su magana, ta yadda na ga suna mamakin ne ya fahimtar da ni cewar Mai marta be fada musu cewar ya hadu da Mama ba sai dai zuwan da yai da ita na ba zata. Tare da Aliyu muka karasa gurin da Mama take tsaye shi kan Mai martaba tuni yayi cikin fadarsa tare da manyan amsu take masa baya, Mama kuma ta fashe da kuka har sai da aka rakata a ka shiga da ita ciki.
Nima hawayen na ke har muka shiga cikin katuwar fadar wacce akaiwa ado da kwalliya irin ta mutanen da sai dai an zamanantar da adon ta yadda zai burge kowa gwanin sha'awa. Kwatatan fadin fadar da girma ta abu ne mai wahala ga mutum irina ne, domin kallon kwaliyar fadar ya hana ni tsayawa na lura da wadanda suke cikin fadar ma. Ban an kara da hakan ba har sai da masu yi ma Mai martaba kirarin cikin yalshen buzanci suka hankato da ni na dawo daga duniyar kallon fadar. Ashe tuni Mai Martaba yai gaba ni da Aliyu da wasu masu take mana baya tafiya muke zuwa wani bangare na fadar ban sani ba. Duk inda muka bi indai da mutane wasu kallon tausayi suke mana wasu kuma kallo ne akwai ma Mamaki, Mama kan sai aikin kuka take ni kuma ina taya ta da hawaye har muak shiga cikin gidan ni da ita da kuma Aliyu. Shi ka Mai Martana tuni ya kama wata hanyar dabam, Yusuf ne yake mana ja gaba har muka shiga inda Mata da yaya da yawa suke. A tsakar gidan Mama ta gurfana ta fashe da wani sabon kuka mai taba zuciya, matan gaba daya suka zagaye ta suna kallonta kamin wasu su kama ta su shiga da ita ciki ciki. A bangaren da ke farko aka shiga da ita wanda na ke kyautata zaton na mahaifiyarta ne ganin hoton Mai Martaba da wasu da ga kuma wati dattijiwa wacce tuni ta kawo bakin kofar falon tana kuka sosai har da saka hannunta ta dafe zuciyarta, Mama ta fadi a bakin kofar tana rike da hannun matar matar ma ta rike hannun Mama gam tana kuka sosai, ba ni kadai ba kowa da ke gurin sai da ya tausawa Mama da matar saboda kukan da suke da kuma wasu ma har da kukan sai da sukai.
“Nana ce ta dawo, Nana ce, Nana, Nana”
Shine abunda yawancin matan da ke gurin suke fadi tare da wasu dattijan mazan, wadanda suka tsaya rumgume da hannunsu suna kallon Mama. Sai da akai ta ba su hakuri sannan Mama ta tsagaita kukan da take ta shiga cikin katon falon wanda sanyin ac da kamshin turare ke maka lale marhabun. Muma shiga cikin falon ni da Aliyu sai aka dawo kan mu ana ta kallon mu wasu har da bude baki, ina jin lokacin da wasu ke fadar ni da Aliyu duka yayanta ne wai Aliyu ne yaya ni kanwa, wasu kuma su ce rakota mu kai. A lokacin da Dattijiwar ta zauna a falon sai ta daga kanta sama hawaye nata mata zuba sai girgiza kai take.
“Mama ki yafe min, Mama ban kyauta miki ba aikata daidai ba, kuma ban kyautawa kaina ba na sani, kuma na cancanci ko wane irin hukunci ko fushi daga gareki”
Mama ce take fadin haka tana daga kasa zaune rike da hannun matar tana kuka, matar ma kukan take irin na tsofi gwanin ban tausayi da taba zuciya, ta hanyar kalaman da Mama take na fahimci cewar dattijiwar Mahaifiyarta ce duk kuwa da kasancewar ba a su yi kama sosai ba domin Mama ta fi kama da Mai Martaba.
RAHMA POV.
daga idonta har makoshinta da fatar jikinta abushe suke kamar wacce. Ta shekara ashirin a gadon asibiti, kallo daya zaka mata ka fahimce akwai damuwa sosai a cikin zuciyarta, tun daga lokacin da aka kawo ta asibiti ta farka bata ce da kowa komai ba, ciki kuwa har da mahaifiyarta da ke kai da kawo tana yawan tambayarta idan tana bukatar wani abun, sai dai ta gyada kai ko ta girgiza, likitan da ya zo dubata ma sai dai ta girgiza masa kai ko ta gyada kai, rashin maganar ya damu kowa domin an kasa gano matsalar rashin maganar tunda tana ji maganar ce kawai bata furtawa, wata kila damuwarta da ke ranta ce ta hana ta magana da kowa ko kuma wani ciwon ne, na daban ya same ra a yanzu.
“Ya kamata a sanar da mijinta Mommyn wannan abun, tun da ta tashi ba tai magana ba, idan kuma aka takura da magana ta fara hawaye wannan abun yayi yawa”
“Ya san da ita ai, tun da yai aure be waiwaye ba, idan ma ya zo ba wani maganin zai mata ba, koda ce take bukata kuma ta mu In-Sha-Allah”
Mahaifiyarta ta mayarwa da Ikram amsa cikin hawaye, kallonsu kawai Rahma ke yi ba tare da tace komai ba.
“Ko jiya ya kirata amman ban daga ba saboda ban san mi zan fada masa ba, amman kyaleta a haka ba shine mafita ba, ya kamata ace ya san matarsa tana asibiti ko da ba zai mata komai ba”
“Idan ya kira ki daga ki fada masa cewar matarsa bata da lafiya tana asibiti”
“To Mommy”