Sashe 68
Zaki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Be iya labartawa Momy abunda ya faru ba, domin yasan ita ma ba fahimta za tai ba, wata kila ma shi zata dorawa laifi sabanin Muhseen. Yanayinsa kawai ta gani tasan yana cikin bacinrai, Momy tana ganewa idan Aliyu yana cikin damuwa da bacinrai. Karya yai mata dan kar ta tambaye shi ya ce mata kansa ke ciwo. A gidan ya wuni har yamma sallama masallacin unguwar yai.
Bayan la'asar Momy ta shirya ita da Laraba wacce ta iso suka kama hanyar Asibitin, Momy na fita Husna da Siyama suka tashi suke shige daki gudun kar su yi wani abun yace am masa ba daidai ba, daman Amina tun da ya shigo gidan ta tare a daki tana kallonta. Bayan fitar Momy da mintuna kadan motar Muhseen ta shigo cikin gidan, a kusa da motar Aliyu ya fakata ya fito ya nufo kofar falon. Knocked ya fara yi kamin ya tura kofar falon ya shiga. Aliyu na zauna saman cushion yana kallon Muhseen har ya karaso cikin falon, be ce da Aliyu komai ba ya nufi kitchen a zatonsa Momy na can.
“Kana aiki kamar baka san aikin ka ba Muhseen, taya zaka fadawa karamar yarinya kai tsaye cewar mahaifiyarta za manta da komai?”
Muhseen ya juyo ya kalleshi.
“Wani likitan ne zai fada min idan na yi kuskure amman ba mai kula da Sky Global Resources ba, aikin kamfani kake Aliyu baka san komai akan aikina ba”
“Yes aikin kamfani nake, shiyasa na iya sarrafa halshe na san irin maganar da zan fadawa kowa, ba kamar kai ba da zaka tashi hankali yarinya karama kana fada mata maganar da bata kamata ba”
“Miyasa tashin hankalinka zai tashi hankakinka Aliyu? Saboda kar cutar da kai mata ta fito fili ko kuma saboda akwai abunda kake boye?”
Aliyu ya masa banza yana ciro wayarsa ya danna.
“Son ta kake yi ko Aliyu?”
“Son ta nake yi ko akwai abunda zaka yi? Yanzu ma kaje ka fada mata cewar ina son ta shikenan”
“Very funny”
Muhseen ya fada yana dariya sannan ya nufi kitchen din. Aliyu ya bishi da wani kallon banza.
“Zan yi kokarin hana duk wani kusanci na ku ko kebawa ka fada mata magana son ranka, ba zan kyaleka ka rika shigar mata jiki ba kana son cutar da zuciyarta da ita sakare kawai”
Shine abunda Aliyu ya fada a ransa sannan ya tashi ya fice daga gidan gaba daya zuwa gidansa.Be samu Rahma a idan ba, hakan kuma be bashi mamaki ba domin ya saba mata da fita ba tare da ta nemi izininsa ba. Sai dai a tsakanin yau da ta fita da kuma wacan zuwan daga Abuja zuwa nan ya bata masa rai matuka. Yana zaune a gidan har magariba babu abunda yake tunani sai Ataa, ta masa maganganu masu zafi amman yai mata uzuri saboda tana cikin damuwa da bacin rai, zancen zata manta kowa ya fi komai tsaya masa a rai shi yana mamakin yadda ciwon kodarta zai taba kanta har ta manta da kowa.
“All this saboda ni oh Ya rabbi ashe haka jarrabawar nan take? Ni kuma tawa kenan?”
Ya furta yana tsaye jikin karfen stairs yana sauraren kiran sallah isha'i da ake. Komawa yai ciki yai alwala ya fito ya shiga masallacin unguwar yai sallah daya dawo be ma shiga falon ba ya shiga motarsa zuwa gidan Momy. Ko da ya shiga Momy ta shirya abincin dare na su Ataa tuwo da miya.
“Ga abincin ta nan ka je ka kai mata”
Ko zama be yi ma Momy tai masa wannan maganar. Kai tsaye ya nufi dinning ya dauki miyar Siyama ta saka masa tuwo da plates Momy tana ce masa idan ya kai ya dauko na can a wanke. Tare da Siyama ya tafi asibitin saboda ta rika masa kulolin, bayan yayi fakin ya fito tana gaba yana baya har suka shiga ciki. Wannan karon ma be shi sallama ba sai dai Siyama ta fanshe shi tun da ita ta yi sallamar. Bayan sun gaisa da Laraba yai ta rabon ido ko zai ga Ataa be ganta ba.
“Ina Ataa?”
Ya tambaya yana kallon Nana.
“Ta fita tun dazun”
“Ina taje?”
“Bata fada min inda zata je ba”
Fitowa yai sai Siyama tai saurin daukar kayan ta biyo bayansa ta saka su a mota ya kama hanyar gida.A bakin gate ya gaje ta ragowar kulolin ma sai da mai gadin ya rika mata ta shiga da su, sai ya koma cikin asibitin. Harabar ya tsaya yana ta kallon mutane kamin ya sake komawa ciki a zaton mai gadin ward din Aliyu likita me dan haka ya bude masa kofa da kansa ya shiga duk kuwa da kasancewar dazun ya ganshi da wata yarinya tana dauke da kuloli.
“Bata dawo ba?”
Ya tambaya daga shigarsa dakin.
“Eh har yanzu”
Juyowa yai ya fito ya dawo cikin motar ya zauna yana ta tunanin inda zata je cikin daren nan, wata kila Doc Bukar ya fita da ita ko kuma Muhseen daman be ganshi cikin gidan ba lokacin daya shiga, fargabarsa daya baya son ta kebe da wani gudun faruwar wani domin shi yana ganin ba ko wane namiji ne zai iya kallonta ya kawarda ido ya hade yawunsa ba, musamman ganin bata da kowa. Key yai ma motarsa yana rage ac cikin ya fito daga cikin asibitin ya nufi Clapperto road domin ya duba can, idan kuma har bada can gida zai koma ya saka Momy ta kira Muhseen shi kuma ya kira Doc Bukar. Slowly ya shiga cikin unguwar ya kashe hasken motarsa yana tukawa a hankali har ya isa gidansu Farida.
Karasowa yai da motar har dakin kwanon ya matsa ta can inda kofar dakin take ya sauke gilashin motarsa yana hango dakin mai duhu da farin wata ke haskawa, fitowa yai cikin motar a hankali ya nufo dakin ya haska screen din wayarsa daga nisa ya hango Ataa a kwance ta takure guri daya tana bachi kanta na gurin kofa. Wani dogon numfashi yaja ya sauke sannan ya koma cikin motar ya zauna ya bar kofar motar a bude. Idan ya tafi ya barta be san abunda zai iya samunta ba, idan kuma ya tashe ta wata kila wata bakar maganar zata fada masa ko kuma tai masa ihu. Sosai ya so ya tafi sai kuma ya ji ba zai iya kyaleta wani ya zo ya yaga mutuncin ta ba, idan ta kara shiga wani halin a yanzu yana jin kamar shine sanadi, kwantar da kujerar motar yai ya jingina yana ta kallonta tana bachi sai sauke ajiyar zuciya take har shi ma bachin yai gaba da shi.
*Khadeeja Candy ce*
ZAKI
By Khadeeja Candy
33...
Ban kwanta da niyar bachi ba na kwanta ne kawai na wani lokaci da zimmar idan na dan hutu tunanin ya fita a raina na koma asibitin, daga nan bachi yai gaba da ni ban sake sanin inda nake ba sai da sanyin azuba ya soma saukowa kiran sallah ya karade ko'ina sannan na bude idona mika nai ina jin yadda jikina yake ciwo saboda kwantarwa da nai a takure ga kuma dadewar da nai a kwancen. Hango mota na facing din inda na ke yasa ni saurin tashi zaune kamin na mike tsaye ina kallon kotar duk da kasancewar akwai hudun asuba sai dai a akwai wutar nepar gidansu Farida da ta hasko inda muke ba kamar Jiya dana kwanta babu nepar ba.
Gabana ne ya soma faduwa ina ta tunanin inda babbar mota zata fito irin wannan, sai kuma nake ganin kamar na taba ganin kalarta sai dai ba zan iya shaidar ta waye ba, wani karin abun tsoro kofar motar a bude take kuma babu kowa a ciki. Na hade yawu ya fi sau a kirga saboda tsoro gabana sai faduwa yake. Koma nai can kuryar dakin ina ta kallon ko zan samu wani abu na boya, tsoro duk ya kamani sai a yanzu nake ganin wautata na kwantawa ni kadai a gurin yanzu idan sace ni aka zo yi fa ya zanyi? Idan kuma wani abun za a mim babu mai cetona. Hawaye na fara yi a take na dan tako zuwa gurin kofar ya leko kaina, ina lekowa Aliyu na dago kansa ya kalleni yana zaune a gurin ya jingina da kwanon dakinmu wani abun mamaki a kasa ba tare da ya shimfida komai ba. Saurin komawa nai cikin zuciyata na raya min cewar ba shi ne ba, domin shi mai girman kan tsiya da kankantar da mutane ba zai zauna a nan ba, idan ma ya zauna mi zaiyi? Amman idan ba shi ba ne waye? Aljani? Domin kamaninsa da na wacan Aliyu bil'adam daya ne. Sake kai kaina nai zan leka sai shi ma ya leko cikin dakin.
“Ataa kin tashi?”
Jin muryarsa yasa na tabbatar da cewar shi din ne, amman kuma me yake yi a nan?
“Aliyu ne?”
Banza yai min kamar ba zai amsa min ba.
“Fito muje gida gurin Momy kamin mutane su taru”
Ya fada yana kabe kasar dake wandonsa.
“Kai din ne?”
Na tambaya dan tabbatar, nan ma be amsa ni ba ya nufi motarsa ya shiga, wannan miskilancin nasa kadai ya isa ya tabbatar min da cewar shi din ne dai ba wani ba.Fitowa nai ba dan na daina jin tsoron ba sai dai wannan karon ba zan iya musa masa ba. Takawa na fara yi ina kallon fuskarsa da wayar hannunsa ke haskawa sakamakon danna ta da yake. Zagayawa nai dayan side din idonsa n kan wayarsa amman hakan be hana shi sanin na karaso kusa da motar ba sai hannunsa ya mika ya bude min motar ni kuma na shiga ina kallonsa har ya janyo murfin motar ya rufe be dauke idonsa daga kan wayar ba. Nima na rufe gefena sai yai motar key ya kunna fitilar motar a sannan ya daga kansa ya kalli gabansa yana ribas kamin ya dawo kan hanya mu fito daga cikin kwanar mu hau titin Clapperto road. Kallonsa nake ina ta mamakin yadda mutum kamar Aliyu mai taka ma da kudi da ji da kai ga isa zai zauna a gurin kamar wannan.
“Miyasa ka zauna a nan gurin?”
Bayan la'asar Momy ta shirya ita da Laraba wacce ta iso suka kama hanyar Asibitin, Momy na fita Husna da Siyama suka tashi suke shige daki gudun kar su yi wani abun yace am masa ba daidai ba, daman Amina tun da ya shigo gidan ta tare a daki tana kallonta. Bayan fitar Momy da mintuna kadan motar Muhseen ta shigo cikin gidan, a kusa da motar Aliyu ya fakata ya fito ya nufo kofar falon. Knocked ya fara yi kamin ya tura kofar falon ya shiga. Aliyu na zauna saman cushion yana kallon Muhseen har ya karaso cikin falon, be ce da Aliyu komai ba ya nufi kitchen a zatonsa Momy na can.
“Kana aiki kamar baka san aikin ka ba Muhseen, taya zaka fadawa karamar yarinya kai tsaye cewar mahaifiyarta za manta da komai?”
Muhseen ya juyo ya kalleshi.
“Wani likitan ne zai fada min idan na yi kuskure amman ba mai kula da Sky Global Resources ba, aikin kamfani kake Aliyu baka san komai akan aikina ba”
“Yes aikin kamfani nake, shiyasa na iya sarrafa halshe na san irin maganar da zan fadawa kowa, ba kamar kai ba da zaka tashi hankali yarinya karama kana fada mata maganar da bata kamata ba”
“Miyasa tashin hankalinka zai tashi hankakinka Aliyu? Saboda kar cutar da kai mata ta fito fili ko kuma saboda akwai abunda kake boye?”
Aliyu ya masa banza yana ciro wayarsa ya danna.
“Son ta kake yi ko Aliyu?”
“Son ta nake yi ko akwai abunda zaka yi? Yanzu ma kaje ka fada mata cewar ina son ta shikenan”
“Very funny”
Muhseen ya fada yana dariya sannan ya nufi kitchen din. Aliyu ya bishi da wani kallon banza.
“Zan yi kokarin hana duk wani kusanci na ku ko kebawa ka fada mata magana son ranka, ba zan kyaleka ka rika shigar mata jiki ba kana son cutar da zuciyarta da ita sakare kawai”
Shine abunda Aliyu ya fada a ransa sannan ya tashi ya fice daga gidan gaba daya zuwa gidansa.Be samu Rahma a idan ba, hakan kuma be bashi mamaki ba domin ya saba mata da fita ba tare da ta nemi izininsa ba. Sai dai a tsakanin yau da ta fita da kuma wacan zuwan daga Abuja zuwa nan ya bata masa rai matuka. Yana zaune a gidan har magariba babu abunda yake tunani sai Ataa, ta masa maganganu masu zafi amman yai mata uzuri saboda tana cikin damuwa da bacin rai, zancen zata manta kowa ya fi komai tsaya masa a rai shi yana mamakin yadda ciwon kodarta zai taba kanta har ta manta da kowa.
“All this saboda ni oh Ya rabbi ashe haka jarrabawar nan take? Ni kuma tawa kenan?”
Ya furta yana tsaye jikin karfen stairs yana sauraren kiran sallah isha'i da ake. Komawa yai ciki yai alwala ya fito ya shiga masallacin unguwar yai sallah daya dawo be ma shiga falon ba ya shiga motarsa zuwa gidan Momy. Ko da ya shiga Momy ta shirya abincin dare na su Ataa tuwo da miya.
“Ga abincin ta nan ka je ka kai mata”
Ko zama be yi ma Momy tai masa wannan maganar. Kai tsaye ya nufi dinning ya dauki miyar Siyama ta saka masa tuwo da plates Momy tana ce masa idan ya kai ya dauko na can a wanke. Tare da Siyama ya tafi asibitin saboda ta rika masa kulolin, bayan yayi fakin ya fito tana gaba yana baya har suka shiga ciki. Wannan karon ma be shi sallama ba sai dai Siyama ta fanshe shi tun da ita ta yi sallamar. Bayan sun gaisa da Laraba yai ta rabon ido ko zai ga Ataa be ganta ba.
“Ina Ataa?”
Ya tambaya yana kallon Nana.
“Ta fita tun dazun”
“Ina taje?”
“Bata fada min inda zata je ba”
Fitowa yai sai Siyama tai saurin daukar kayan ta biyo bayansa ta saka su a mota ya kama hanyar gida.A bakin gate ya gaje ta ragowar kulolin ma sai da mai gadin ya rika mata ta shiga da su, sai ya koma cikin asibitin. Harabar ya tsaya yana ta kallon mutane kamin ya sake komawa ciki a zaton mai gadin ward din Aliyu likita me dan haka ya bude masa kofa da kansa ya shiga duk kuwa da kasancewar dazun ya ganshi da wata yarinya tana dauke da kuloli.
“Bata dawo ba?”
Ya tambaya daga shigarsa dakin.
“Eh har yanzu”
Juyowa yai ya fito ya dawo cikin motar ya zauna yana ta tunanin inda zata je cikin daren nan, wata kila Doc Bukar ya fita da ita ko kuma Muhseen daman be ganshi cikin gidan ba lokacin daya shiga, fargabarsa daya baya son ta kebe da wani gudun faruwar wani domin shi yana ganin ba ko wane namiji ne zai iya kallonta ya kawarda ido ya hade yawunsa ba, musamman ganin bata da kowa. Key yai ma motarsa yana rage ac cikin ya fito daga cikin asibitin ya nufi Clapperto road domin ya duba can, idan kuma har bada can gida zai koma ya saka Momy ta kira Muhseen shi kuma ya kira Doc Bukar. Slowly ya shiga cikin unguwar ya kashe hasken motarsa yana tukawa a hankali har ya isa gidansu Farida.
Karasowa yai da motar har dakin kwanon ya matsa ta can inda kofar dakin take ya sauke gilashin motarsa yana hango dakin mai duhu da farin wata ke haskawa, fitowa yai cikin motar a hankali ya nufo dakin ya haska screen din wayarsa daga nisa ya hango Ataa a kwance ta takure guri daya tana bachi kanta na gurin kofa. Wani dogon numfashi yaja ya sauke sannan ya koma cikin motar ya zauna ya bar kofar motar a bude. Idan ya tafi ya barta be san abunda zai iya samunta ba, idan kuma ya tashe ta wata kila wata bakar maganar zata fada masa ko kuma tai masa ihu. Sosai ya so ya tafi sai kuma ya ji ba zai iya kyaleta wani ya zo ya yaga mutuncin ta ba, idan ta kara shiga wani halin a yanzu yana jin kamar shine sanadi, kwantar da kujerar motar yai ya jingina yana ta kallonta tana bachi sai sauke ajiyar zuciya take har shi ma bachin yai gaba da shi.
*Khadeeja Candy ce*
ZAKI
By Khadeeja Candy
33...
Ban kwanta da niyar bachi ba na kwanta ne kawai na wani lokaci da zimmar idan na dan hutu tunanin ya fita a raina na koma asibitin, daga nan bachi yai gaba da ni ban sake sanin inda nake ba sai da sanyin azuba ya soma saukowa kiran sallah ya karade ko'ina sannan na bude idona mika nai ina jin yadda jikina yake ciwo saboda kwantarwa da nai a takure ga kuma dadewar da nai a kwancen. Hango mota na facing din inda na ke yasa ni saurin tashi zaune kamin na mike tsaye ina kallon kotar duk da kasancewar akwai hudun asuba sai dai a akwai wutar nepar gidansu Farida da ta hasko inda muke ba kamar Jiya dana kwanta babu nepar ba.
Gabana ne ya soma faduwa ina ta tunanin inda babbar mota zata fito irin wannan, sai kuma nake ganin kamar na taba ganin kalarta sai dai ba zan iya shaidar ta waye ba, wani karin abun tsoro kofar motar a bude take kuma babu kowa a ciki. Na hade yawu ya fi sau a kirga saboda tsoro gabana sai faduwa yake. Koma nai can kuryar dakin ina ta kallon ko zan samu wani abu na boya, tsoro duk ya kamani sai a yanzu nake ganin wautata na kwantawa ni kadai a gurin yanzu idan sace ni aka zo yi fa ya zanyi? Idan kuma wani abun za a mim babu mai cetona. Hawaye na fara yi a take na dan tako zuwa gurin kofar ya leko kaina, ina lekowa Aliyu na dago kansa ya kalleni yana zaune a gurin ya jingina da kwanon dakinmu wani abun mamaki a kasa ba tare da ya shimfida komai ba. Saurin komawa nai cikin zuciyata na raya min cewar ba shi ne ba, domin shi mai girman kan tsiya da kankantar da mutane ba zai zauna a nan ba, idan ma ya zauna mi zaiyi? Amman idan ba shi ba ne waye? Aljani? Domin kamaninsa da na wacan Aliyu bil'adam daya ne. Sake kai kaina nai zan leka sai shi ma ya leko cikin dakin.
“Ataa kin tashi?”
Jin muryarsa yasa na tabbatar da cewar shi din ne, amman kuma me yake yi a nan?
“Aliyu ne?”
Banza yai min kamar ba zai amsa min ba.
“Fito muje gida gurin Momy kamin mutane su taru”
Ya fada yana kabe kasar dake wandonsa.
“Kai din ne?”
Na tambaya dan tabbatar, nan ma be amsa ni ba ya nufi motarsa ya shiga, wannan miskilancin nasa kadai ya isa ya tabbatar min da cewar shi din ne dai ba wani ba.Fitowa nai ba dan na daina jin tsoron ba sai dai wannan karon ba zan iya musa masa ba. Takawa na fara yi ina kallon fuskarsa da wayar hannunsa ke haskawa sakamakon danna ta da yake. Zagayawa nai dayan side din idonsa n kan wayarsa amman hakan be hana shi sanin na karaso kusa da motar ba sai hannunsa ya mika ya bude min motar ni kuma na shiga ina kallonsa har ya janyo murfin motar ya rufe be dauke idonsa daga kan wayar ba. Nima na rufe gefena sai yai motar key ya kunna fitilar motar a sannan ya daga kansa ya kalli gabansa yana ribas kamin ya dawo kan hanya mu fito daga cikin kwanar mu hau titin Clapperto road. Kallonsa nake ina ta mamakin yadda mutum kamar Aliyu mai taka ma da kudi da ji da kai ga isa zai zauna a gurin kamar wannan.
“Miyasa ka zauna a nan gurin?”