Sashe 115
Zaki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ba ni da zabi daya wuce na bin umarninsa, a dole na bi yo bayansa muka fito tare daga dakin Zee muka sauko kasa inda Ammy take zaune, gaba dayansu kallona suke har Ammy irin kallon na kamar mamaki.
“Wani sakamako sai Allah Aliyu, ka auri yarinyar ba dan ka san kowa nata ba, ba dan komai na ta ba, sai ga shi Allah ya maka sakamako da inda baka yi tsammani ba, hakurin da kai da zama da Rahama Allah ya baka wacce ta fita komai”
Kamar yadda suke mana kallon mamaki haka ni da Aliyu muke musu shi jin irin maganar da ke fitowa daga bakin Ammy. Zaunawa Aliyu yai a kujera ni kuma na zauna kasa inda Humaira take zaune kasa.
“Shiyasa ba a son ka wulakanta mutum ba ka san abunda zai zama ba nan gaba, kuma ba kasan da inda zai iya taimakonka ba, ba dole sai babban taimako ma wani ko alfarma yai maka ya baka ruwa ka sha ai ya jidadin a lokacin da kake jin kishi, waya zai tsammanci ke din jikar babban mutum ce, har ki yi aiki a gidan nan? Ni abunda ban gane ba wai kin san cewa Sarki Agadez Kakani kuwa ko kuma sai yau? Abbah ku ma daya fada min wannan maganar shi kanshi mamaki yake domin abun ya dore masa kai sosai”
Ammy ce dai take wannan maganar tana ta kallona. Aliyu ya kalleni sannan ya sake kallonta ya ce.
“Ta sani, amman ta yi shiru saboda mahaifiyarta bata son maganar”
“Mahaifiyarki ta yi dacen ya Ataa, da baki gudu kin koma cikin dadi kin bar a nan ba, da kuma ba ki saka mata ido har ta wulakanta ba Allah yai miki albarka”
Gaba daya suka amsa da amin, ni kuwa tawa amin din a zuciya take, ina jindadin Ammy tun a wacan zaman da nai tana nuna min kauna bata taba nuna min kyama ko kyara ba kamar Mama Fulani, haka ma Muhseen be taba kyamata ba shiyasa na kasa mantawa da shi a zuciyata halinsa kamar na Ammy ne idan ma ba dan fuskarsa da sanin cewar Mama Fulani ce ta haife shi ba idan ka ganshi zaka tsammaci dan Ammy saboda yanayin halinsu na far'a da son mutane ga kuma marhabun da kowa.
Misalin tara da yan mintuna muka fito daga bangaren Ammy muka nufi bangaren Mama Fulani, kamar yadda nai wacan karon wannan karo ma baya baya na tsaya Saboda tunanin irin kallon da zata min ko ta fada min wata maganar marar dadi. Shi ya tura kofar falon ya shiga sannan ni ma na shigo babu kowa falon sai tv da ac da ke ta aikinsa. Kai tsaye ya nufi upstairs hanyar dakinta ni dai ina biye da shi har muka isa cikin dakin da na ke sharewa na yi mopping amman a da. Ba Mama Fulani kadai muka tarar ba har da Rukaiya da Maryam da Baby suna zaune dakin, suna ganinmu sukai tsit da alama wata maganar suke tsaka da tattaunawa, ina daga bayan Aliyu ban karasa shigo sosai cikin dakin ba, sai ya matsa gefe ya matso da ni kusa da shi yadda zan bayyana tsundun a cikin dakin. Aiko a take Mama Fulani ta sako min ido tana min wani irin kallo ba na lafiya ba, ba kuma zan bayyana dalilin kallon ko manufarsa ba.
“Mama za mu wuce gida”
“To Aliyu sai da safe”
Ta fada amman idonta na kai har lokacin, sai Aliyu ya kalleni yai min magana kadankadan kamar mai bawa yaro umarni ko kuma mai koya masa abunda zai ce.
“Ki ce mata sai da safe Mama”
“Mama Fulani sai da safe”
Na fada kamar yadda ya ba ni umarni sai tai saurin kawarda fuskarta daga barin kallon nawa da take na tsawon lokaci, ba kuma kawarwa irin ta tsana ko kyama da tsangwama ba, irin kawar nan ta kamar mai tunani ko kuma wanda ya rude ko yake jin kunyarka. Ni na riga juyawa na fito daga dakin sannan Aliyu ya fito ya tararda ni har kusa sauka downstairs din.
Ya riga ni isa harabar gidan tun kan na karaso ya janyo motarsa ya bude min front na shiga na zauna na ki rufe ganbun motar da gangan na tsaya ina kallonsa murmushi yai ya bude gefensa ya fita ya zagayo inda na ke ya sumbaci goshina.
“Dama ai kin saba bar min mota a bude tun kina budurwa kuma na zo na rufe balle yanzu da kika zama gimbiyata”
Ya fada sannan ya rufe motar ya zagaya gefenta ya shiga motar yai mata keys muka dauki hanyar gida. Sai da ya biya ta wani shago ya siya mana kayan zafi da kaza sannan muka isa gida. Da kansa ya fita ta zagoyo inda na ke ya bude min mota ina saukowa ya saka hannunsa ya ruumgumo ni kamar wata yar baby ko kunyar mai gadinsa da ke hangen baya ji, ni kuwa duk kunyarsa ta rufe ni.
“Wacan Dattijon Baba fa yana hangenmu”
“Sai me dan ya tsinkaye mu? Be san na aure ki ba ni ko kuma be san namiji na taba matarsa ba? Is normal ma ai ba waji abun nai miki ba dafaki kawai nai, kuma shi ai ya saba ganin hakan idan muna tare da Rahma”
Ya fada yana bude gidan vaya ya dauko siyayyar da yai mana da dayan hannunsa yayinda dayan hannun yake makalle da ni kamar zan tsire masa. Da hannu daya ya rufe motar muka nufi cikin gidan ni da shi.
Ice cream kawai na sha daga cikin abubuwan da siyo mana, domin jin nai bana bukatar komai kuma bana jin yunwa, sai da mu kai wanka ni da shi a tare kamar yadda ya saba min sannan muka saka tufafin bachi muka kwanta. Misalin biyu da wani abu na dare yunwa ta tasheni a dole na bar jikinsa na sauka daga kan gadon na nufi wutar dakin na kunna ko da na juyo sai na ga mutun yana kallona.
“Yunwa na ke ji kazar da ka siyo zan ci”
Na fada ina dan wara kamar mai jin kunya.
“Zauna ba ri na dauko miki”
Ya fada yana saukowa daga kan gadon ya fita daga dakin, ni kuma na zauna saman kujerar sai gashi ya dawo da kazar a plate da lemu. Dan karamin tebur ya janyo ya dora plate din sannan ya miko min hannu na taso sai ya nufi bandaki da ni, wani lokacin yadda Aliyu yake min abu kamar wata yar baby abun har mamaki yake ba ni, wata kila saboda baya son yawan magana ne shiyasa ya son ya yi maka abu kawai ba sai ya furta ya ce kai ba wata kila kuma kuanar ce kaiwai yake nuna min. Sai na wanke bakina sannan muka fito na dawo inda na zauna dazun na zauna yawuna har tsinkewa suke kamin na ci kazar. Kusa da ni ya zauna ya saka hannunsa yana bare min yana ba ni a baki ina ci sai da koshi sannan na cige masa hannu da gangan, sai yai saurin cire hannunaa daga baki na dauki nawa yatsan ya kada a bakinsa ya cigeni kamar wani yaro karami, aiko ba shi ri nai ihu saboda zafin da na ji, sai yai saurin rufe min baki.
“Shiiiiiiii dare ne”
Ya fada kadan-kadan, dariya nai kamar yadda yake dariyar, sannan ya dauko lemun ya ba ni na sha sai ya aje ya matsar da teburin can gefe, ya kwanta saman kujera ya janyo ni na kwanta a kirjinsa, a nan muka kwana har safe yana rumgume da ni sosai a kirjinsa. Bayan mun yi sallah Aliyu ya kwantar da kaina jikinsa yana karatun kur'anin daya saba, ba dade yana karatun ba na tashi daga kwancen da na ke a cinyarsa na sauko falo na nufi kitchen domin samun abunda zan sakawa cikina saboda wata azzababbar yunwa da na ke ji. Freezer na fara budewa sai na ga dukan abunda yake ciki yayi kankara sai na bude dayar da bata aiki na ga Apple da sauran fruits a ciki, apple din na dauko na wanke shi a fanfan kitchen din na soma ci kamar wata mayunwaciya. Ina cikin cikin apple na hudu na ga mutum ya shigo kitchen din da tsage tsage a fuskarsa yana sanye da kananan kayan. Ba shiri na fasa ihu ina ra kiran sunana Aliyu shi ko mutunen sai daga min hannu yake alamar ya kwantar da hankali, tun yana magana da turanci har ya dawo yi da hausa sam ban dauka ma ya isa hausa ba. Da gudu Aliyu ya shigo kitchen din hankalinsa a tashe.
“Minenen?”
“Wacan mutumen.”
Na nuna shi.
“Mai mana girki ne”
Mai girki sai na ji abu wani iri, namiji da girki to miyasa wacan zuwan ban ganshi ba? Ko da yake kwana kawai mu kai mu ka wuce Lagos.
“To ta ina ya shigo?”
“Yana da makullin falon ne ko bana nan zai iya zuwa yai girki ya tafi”
Ya fada min sannan ya juya gurinsa..
“Abdulgany daga yau za ka daina shigowa cikin gidana nan, Nasir zai tura maka kudinka na wata ba zaka mana girki ba”
Risinawa nai ya fara bashi hakuri yana ta rokonsa ya yafe masa idan akan ya ba ni tsoro ne, sai ya fada masa ba dan tsoro ba ne wai yana kishin matarsa ne ba shi da bukatar ganinsa a gidan yanzu. Babu irin magiyar da be yi ba amman Aliyu ya ki saurarensa har sai da ya hada masa da fada sannan ya fice daga gidan.
Misalin tara da rabi Aliyu yai mana oder abincin, muna cikin kiran Abbah ya shigo wayrsa sai da suka fara gaisawa sannan ya sanar masa inda yake ya same sa a can.
“Yi sauri ki ci Abbah na nemanmu”
“Har dani?”
“Wani sakamako sai Allah Aliyu, ka auri yarinyar ba dan ka san kowa nata ba, ba dan komai na ta ba, sai ga shi Allah ya maka sakamako da inda baka yi tsammani ba, hakurin da kai da zama da Rahama Allah ya baka wacce ta fita komai”
Kamar yadda suke mana kallon mamaki haka ni da Aliyu muke musu shi jin irin maganar da ke fitowa daga bakin Ammy. Zaunawa Aliyu yai a kujera ni kuma na zauna kasa inda Humaira take zaune kasa.
“Shiyasa ba a son ka wulakanta mutum ba ka san abunda zai zama ba nan gaba, kuma ba kasan da inda zai iya taimakonka ba, ba dole sai babban taimako ma wani ko alfarma yai maka ya baka ruwa ka sha ai ya jidadin a lokacin da kake jin kishi, waya zai tsammanci ke din jikar babban mutum ce, har ki yi aiki a gidan nan? Ni abunda ban gane ba wai kin san cewa Sarki Agadez Kakani kuwa ko kuma sai yau? Abbah ku ma daya fada min wannan maganar shi kanshi mamaki yake domin abun ya dore masa kai sosai”
Ammy ce dai take wannan maganar tana ta kallona. Aliyu ya kalleni sannan ya sake kallonta ya ce.
“Ta sani, amman ta yi shiru saboda mahaifiyarta bata son maganar”
“Mahaifiyarki ta yi dacen ya Ataa, da baki gudu kin koma cikin dadi kin bar a nan ba, da kuma ba ki saka mata ido har ta wulakanta ba Allah yai miki albarka”
Gaba daya suka amsa da amin, ni kuwa tawa amin din a zuciya take, ina jindadin Ammy tun a wacan zaman da nai tana nuna min kauna bata taba nuna min kyama ko kyara ba kamar Mama Fulani, haka ma Muhseen be taba kyamata ba shiyasa na kasa mantawa da shi a zuciyata halinsa kamar na Ammy ne idan ma ba dan fuskarsa da sanin cewar Mama Fulani ce ta haife shi ba idan ka ganshi zaka tsammaci dan Ammy saboda yanayin halinsu na far'a da son mutane ga kuma marhabun da kowa.
Misalin tara da yan mintuna muka fito daga bangaren Ammy muka nufi bangaren Mama Fulani, kamar yadda nai wacan karon wannan karo ma baya baya na tsaya Saboda tunanin irin kallon da zata min ko ta fada min wata maganar marar dadi. Shi ya tura kofar falon ya shiga sannan ni ma na shigo babu kowa falon sai tv da ac da ke ta aikinsa. Kai tsaye ya nufi upstairs hanyar dakinta ni dai ina biye da shi har muka isa cikin dakin da na ke sharewa na yi mopping amman a da. Ba Mama Fulani kadai muka tarar ba har da Rukaiya da Maryam da Baby suna zaune dakin, suna ganinmu sukai tsit da alama wata maganar suke tsaka da tattaunawa, ina daga bayan Aliyu ban karasa shigo sosai cikin dakin ba, sai ya matsa gefe ya matso da ni kusa da shi yadda zan bayyana tsundun a cikin dakin. Aiko a take Mama Fulani ta sako min ido tana min wani irin kallo ba na lafiya ba, ba kuma zan bayyana dalilin kallon ko manufarsa ba.
“Mama za mu wuce gida”
“To Aliyu sai da safe”
Ta fada amman idonta na kai har lokacin, sai Aliyu ya kalleni yai min magana kadankadan kamar mai bawa yaro umarni ko kuma mai koya masa abunda zai ce.
“Ki ce mata sai da safe Mama”
“Mama Fulani sai da safe”
Na fada kamar yadda ya ba ni umarni sai tai saurin kawarda fuskarta daga barin kallon nawa da take na tsawon lokaci, ba kuma kawarwa irin ta tsana ko kyama da tsangwama ba, irin kawar nan ta kamar mai tunani ko kuma wanda ya rude ko yake jin kunyarka. Ni na riga juyawa na fito daga dakin sannan Aliyu ya fito ya tararda ni har kusa sauka downstairs din.
Ya riga ni isa harabar gidan tun kan na karaso ya janyo motarsa ya bude min front na shiga na zauna na ki rufe ganbun motar da gangan na tsaya ina kallonsa murmushi yai ya bude gefensa ya fita ya zagayo inda na ke ya sumbaci goshina.
“Dama ai kin saba bar min mota a bude tun kina budurwa kuma na zo na rufe balle yanzu da kika zama gimbiyata”
Ya fada sannan ya rufe motar ya zagaya gefenta ya shiga motar yai mata keys muka dauki hanyar gida. Sai da ya biya ta wani shago ya siya mana kayan zafi da kaza sannan muka isa gida. Da kansa ya fita ta zagoyo inda na ke ya bude min mota ina saukowa ya saka hannunsa ya ruumgumo ni kamar wata yar baby ko kunyar mai gadinsa da ke hangen baya ji, ni kuwa duk kunyarsa ta rufe ni.
“Wacan Dattijon Baba fa yana hangenmu”
“Sai me dan ya tsinkaye mu? Be san na aure ki ba ni ko kuma be san namiji na taba matarsa ba? Is normal ma ai ba waji abun nai miki ba dafaki kawai nai, kuma shi ai ya saba ganin hakan idan muna tare da Rahma”
Ya fada yana bude gidan vaya ya dauko siyayyar da yai mana da dayan hannunsa yayinda dayan hannun yake makalle da ni kamar zan tsire masa. Da hannu daya ya rufe motar muka nufi cikin gidan ni da shi.
Ice cream kawai na sha daga cikin abubuwan da siyo mana, domin jin nai bana bukatar komai kuma bana jin yunwa, sai da mu kai wanka ni da shi a tare kamar yadda ya saba min sannan muka saka tufafin bachi muka kwanta. Misalin biyu da wani abu na dare yunwa ta tasheni a dole na bar jikinsa na sauka daga kan gadon na nufi wutar dakin na kunna ko da na juyo sai na ga mutun yana kallona.
“Yunwa na ke ji kazar da ka siyo zan ci”
Na fada ina dan wara kamar mai jin kunya.
“Zauna ba ri na dauko miki”
Ya fada yana saukowa daga kan gadon ya fita daga dakin, ni kuma na zauna saman kujerar sai gashi ya dawo da kazar a plate da lemu. Dan karamin tebur ya janyo ya dora plate din sannan ya miko min hannu na taso sai ya nufi bandaki da ni, wani lokacin yadda Aliyu yake min abu kamar wata yar baby abun har mamaki yake ba ni, wata kila saboda baya son yawan magana ne shiyasa ya son ya yi maka abu kawai ba sai ya furta ya ce kai ba wata kila kuma kuanar ce kaiwai yake nuna min. Sai na wanke bakina sannan muka fito na dawo inda na zauna dazun na zauna yawuna har tsinkewa suke kamin na ci kazar. Kusa da ni ya zauna ya saka hannunsa yana bare min yana ba ni a baki ina ci sai da koshi sannan na cige masa hannu da gangan, sai yai saurin cire hannunaa daga baki na dauki nawa yatsan ya kada a bakinsa ya cigeni kamar wani yaro karami, aiko ba shi ri nai ihu saboda zafin da na ji, sai yai saurin rufe min baki.
“Shiiiiiiii dare ne”
Ya fada kadan-kadan, dariya nai kamar yadda yake dariyar, sannan ya dauko lemun ya ba ni na sha sai ya aje ya matsar da teburin can gefe, ya kwanta saman kujera ya janyo ni na kwanta a kirjinsa, a nan muka kwana har safe yana rumgume da ni sosai a kirjinsa. Bayan mun yi sallah Aliyu ya kwantar da kaina jikinsa yana karatun kur'anin daya saba, ba dade yana karatun ba na tashi daga kwancen da na ke a cinyarsa na sauko falo na nufi kitchen domin samun abunda zan sakawa cikina saboda wata azzababbar yunwa da na ke ji. Freezer na fara budewa sai na ga dukan abunda yake ciki yayi kankara sai na bude dayar da bata aiki na ga Apple da sauran fruits a ciki, apple din na dauko na wanke shi a fanfan kitchen din na soma ci kamar wata mayunwaciya. Ina cikin cikin apple na hudu na ga mutum ya shigo kitchen din da tsage tsage a fuskarsa yana sanye da kananan kayan. Ba shiri na fasa ihu ina ra kiran sunana Aliyu shi ko mutunen sai daga min hannu yake alamar ya kwantar da hankali, tun yana magana da turanci har ya dawo yi da hausa sam ban dauka ma ya isa hausa ba. Da gudu Aliyu ya shigo kitchen din hankalinsa a tashe.
“Minenen?”
“Wacan mutumen.”
Na nuna shi.
“Mai mana girki ne”
Mai girki sai na ji abu wani iri, namiji da girki to miyasa wacan zuwan ban ganshi ba? Ko da yake kwana kawai mu kai mu ka wuce Lagos.
“To ta ina ya shigo?”
“Yana da makullin falon ne ko bana nan zai iya zuwa yai girki ya tafi”
Ya fada min sannan ya juya gurinsa..
“Abdulgany daga yau za ka daina shigowa cikin gidana nan, Nasir zai tura maka kudinka na wata ba zaka mana girki ba”
Risinawa nai ya fara bashi hakuri yana ta rokonsa ya yafe masa idan akan ya ba ni tsoro ne, sai ya fada masa ba dan tsoro ba ne wai yana kishin matarsa ne ba shi da bukatar ganinsa a gidan yanzu. Babu irin magiyar da be yi ba amman Aliyu ya ki saurarensa har sai da ya hada masa da fada sannan ya fice daga gidan.
Misalin tara da rabi Aliyu yai mana oder abincin, muna cikin kiran Abbah ya shigo wayrsa sai da suka fara gaisawa sannan ya sanar masa inda yake ya same sa a can.
“Yi sauri ki ci Abbah na nemanmu”
“Har dani?”