Sashe 96
Alkalamin Kaddara ta Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
*WANNAN BOOK NA KUDI NE BA FREE BANE, IDAN KINA DA RA'AYIN KARANTASHI KI GARZAYO KI BIYA KUDINKI YAR UWA ZAKI SAMU BONUS NA DUKAN LITATAFAINA CIKI HARDA NA KUDIN DA NA GAMA KWANAN NAN, KI GANE................ALKALAMI NA DORA, NA ZUBA RUBUTU......IN SHA ALLAH ZAKI NISHADANTU SANNAN KI KARU💓💓💓*
Zaku biya kuɗin ku ta wannan account numbern 0225962748
Amina Maikudi Abdullahi
GTBank Naira 300 ne kacal zaku biya anyi araha an hana bashi.
Ko ku turo Recharge card ta wannan numbern wayar
08038856944 banda vtu hoton katin zaki ɗauka ki turo.
Sannan Sai ku tura shaidar biya ta wannan no din +22793811618
Ga ƴan Niger zaku biya kuɗin ku ta wannan layin +22793811618 katin sahelcom ko AIRTEL ta dala DARI ne ( 500 francs cefa) sai ku tura shaidar ta layin nawa sannan na saka ku a grup din
Sai kun zo🥰🥰🥰🥰🥰
A guje ta diba ta nufi bangarensu gannin itace za'a bugawa ludayin ko me?
Ai kam mamanta bata yi kasa da gwuiwa ba ta rufa mata baya har suka idasa shiga kafin ta ja ta tsaya gannin ta je da gudu bayan mahaifinta ta tsaya tana kallon Maman
Dan murmushi ya yi da alkur'anin dake hannunsa ya dan rufe yana kallonta ya ce" Malama wani abu muka yi ne?"
Ludayin dake hannunta ta nuna ta ce" Aban IBTISAM ka bani yarinyar nan na maka mata wannan ludayin ko zata nutsu"
Kai ya girgiza da dan sauri yana mai jin wani farin ciki da annashuwa da tuna rayuwarsu ta da ya sake fadin" Me zai hanna a gyara matsalar ta fatar baki ne ba sai an taba lafiyar jikinmu ba?"
Mamanta ta sauke yar ajiyar zuciya tana kallonsa ta ce" Mijinta fa zai dawo yau, shin a shiriricewar da suka yi harda ta rashin sannin ciwon kai?, Rashin sannin ciwon kai ne mana Abansu macen da zata yi zaune kamar jaka mijinta na hanya daga tafia? Allah na tuba ko a cikin gari ne ya yi tafiyar awa hudu wajen aiki ko zaman majalisa ai kya kokarta da abinda Allah ya malaka maki ki dan daidaita ta yadda gobe idan ya tashi yi maki gori ba dai na tsaftar jikinki, ko muhalinki, ko girkinki ba, Malama wuce ki je ki gyara masa bangarensa, ki maida hankali ki zo ki kawo kayan abincinsa daban a zuba ki kai ki kilace, ki kula da turaren wuta da na bayi da na gadonsa, sannan ki tabata kin kula da jikinki yadda ya dace .......ko shima sai na koya maki ne?" Ta karashe da dan daga muryarta kadan tana zazaro mata ido
Da sauri Shuwwa ta girgiza kanta ta fito daga bayan mahaifinta ta zagaya da gudu ta wuce a dakin gaba daya ta tafi wajen Maman Muhay dan tambayarta ky din bangarensa cike da tunani kala daban daban
Tunda take fadan, mahaifin Shuwwa ke kallonta
Zai iya cewa rabonsa da irin wannan tunanin a zuciyarsa har ya manta,
Hijabin dake jikinta kiwa sosai yake boye yar ramar da bata idasa cikewa a jikinta ba, fadan da take yi kuwa sai yar duma dumar budurwar da ta sace zuciyarsa dare daya ta dawo masa a cikin tunaninsa
Tabas zai iya cewa bai taba gannin mace mai tsaftarta ba, watau idanma tana da dati to fa idannuwansa basu gani ba, gata da kamshi, gata da dumi.............
A hankali ya samu kansa da dan hadiye yawu kadan a makoshinsa da ya dan bushe a lokacin da ta juya ta fice a dakin bayan an ja masa nasa kashedin shima ta hanyar turo bakinta kadan ta auno shagwabar dake tata ce wace ake yi masa ne ta dan dira kafarta ta ce" Ka ga dai Abanta walahi karma ka ce zaka hannani shakarta, gaba daya yaren nan na kula sun dauki marar kirkin hali da yawa sun zubar da na kirkin, ka ga NAHIDTma jira take na ce ta je ta gyara jikinta dan bakon da za'a zo da shi, aman ba komai daidai nake da y'ayanka ni kam!" Ta idasa ta juya ta bar masa wajen
Dan murmushi ya yi yana girgiza kansa ya sake bude Alkur'aninsa a kasan zuciyarsa yana ayanna abubuwa kamar haka' Wannan rayuwar ita nake so ta co gaba da wakana a tare da ni, na so na yi ta yinta har zuwa cikin kabarina......, Sai dai gashi ga dukkan alamu kwana kusa zata gagareni, domin nadin dake kaina mai rikicin da ban san ko zan iya kallonta a haka tana min girgiza ba......?' (Mamana, auntyna, dan Allah ku duba, ku bude idannuwanku ku duba, koda kune kushewa a tsufa, koda kune magarya a y'aya ya dace ku gane cewar ibada ne, haihuwar y'aya ba shine zai sa ki watsar da komai ki zubar da komai ba, tabas akoy kunya irin tamu ta hausa fulani wace ke hanna mana aikata wasu abubuwan a gaban y'ayanmu ko bakin fuska, aman na tambayeku su y'ayan har cikin dakinmu suke kwana da mu ne?, Ki iya rigima mama koda baki iya ba, ki dan ringa dan jefo shagwaba lokaci zuwa lokaci koda baba bai san me hakan yake nufi ba, ki gane mama nishadinki ne koda baba a yanzun baya andanuwa ta hanyar bed, ki gane ki dan zuba abu irin na yarintama zai saka baba kallonki da murmushi a fuskarsa ya dan dungure maki kai ya ce yau kuma shagwaba ake ji maman walida?, Yau kuma rigima ake ji uman Fatima?, Yau yan rikicin a kusa suke da alama uwar gidan Malan, ba maganar mijinki bashi da kudi a wajenki sarki ne, ba maganar mijinki babu abinda ya sani sai fushi cen dam baki koya masa walwala ba a yanzu ba zai iya koya ba, walahi ko dutse ne shi dabi'a zata shige shi, domin yau da gobe sai Allah , ke dai ki yi kokari idan kin zubar da komai ki dawo da daurin nan naki ture ka ga tsiy a gabansa, ki dan shafa jan baki ki kanne ido, idan yace to yau kuma? Ko dai a kaiki a maki rukiya ne? Rukunkume baba ki jefa shi a gado zai gane aljanu sun shigeki😌, aman fisabililahi dan kawai kin samu jika kamarni shikenan sai ki wani kashe kanki inadarma ba'a habakata?, Lada ne fa, 😌 gaskiya a daina wasa da lada gaskiya, a gyara Mama babama yana son jin dadi gaskiya, kuma tsufanki a wajenmu y'ayanki kika dan kwana biyu walahi a wajensa in kin so kika tsufa, domin kinga damar da furfurarki da yabarki ki ce sai ya maki Ampa😌, ba nufina da shekarunki ki ringa fama da kannanun kaya ba, ko daya, ko daya walahi, wani sa'in da kannanun shekarunma sai ka ga idan yannayin jikin mutun sai a hankali kannanun kayan basa yi masa kyau, ba dole bane saka su, ke dai kawai ki iya dauri 😂babu abinda bama gani ehe, a dai kula😍😍😍)
Gyaran take yi cike da takaici a kasan zuciyarta
Ba komaine ya sakata a cikin takaicin ba sai tunawa da ta yi ko a safiyar yau ta yi masa mesage kamar haka *Barka da safiya yalabai, fatan ka tashi cikin koshin lafiya? Yaya aiki? Allah ya tsare* aman ko nataciyar mayya bai turo mata da reply ba bale ta yi tunanin ya gani, to wai ko bai gannin bane? Ko kuma da wani tunani na daban ne a cikin kwakwaluwar wannan bawan Allahn ne? Koda yake idan ta ce babu ta yi karya, ta san da décision dinsa na rabuwa da ita kwana kusa, to aman ita tana gannin mutuncinsa da kimarsa a yanzu ne dan ya kwatanta kamar shi din ai dan mutunci ne ta hanyar taimakon iyayenta kau?, Aman a yanzu abinda Mamansa ta ce ya matukar bata mamaki, shin ta yaya suke so ta dauko suturarta ta kawo dakin nan ne? Wai me suke so da ita ne haka kai tsaye?
Maida hankaki ta yi ta gama gyaran sannan ta koma bangaren Mama ta shiga wanka
Kukawa da jikinta da mahaifiyarta ta ce ta kwatanta gwargwadon sanninta ta hanyar cire dukkan datin da ta san yana iya zama a jikinta sannan ta saka turare a dukan wani lungu da ta san tana da shi a jikinta komai kankantarsa
A saman kujera ta zauna ta shiga tsara sasaukar Mak'up a fuskarta, wace haka kawia ta ji tana ra'ayin a saman farin fatarta ta dan karra hoda ko yayane sannan ta gyara girarta harma ta saka kajal, ta dora da jan baki mai hawa da rantsatsan dinkin atamparta da ta ciro cikin dinkunnan da akai masu ita da yar uwarta
Sosai ta bata lokaci tana gyara har akai kiraye kirayen sallar magariba
Nan ta gabatar da sallarta, sannan ta saka kayanta ta kashe dauri irin mai tsokale idon ogan nan
Bata dauki mayafi ba, bale hijab, takalminta ta saka plate sai dai mai gashi a jikinsa sosai bayan ta saka safar da ta zame mata jiki
A tausashe take tafiya a tsakar gidan tana hankalce da yannayin gidan nasu na yau, taron sojoji ya fi na da yawa sosai, sannan du idan aka ji motsi sai an duba dan gannin ko wanene, da zarar an ga itace kuwa sai ta ga ana yi mata gaisuwa irin ta mutuntawar nan sannan a bata hanya ta wuce
Ita dai bata damu ba har ta karasa ta kama kofar ta bude da salama a bakinta ta shiga
Sansanyan kanshin turaren wuta garwaye da turarrukan jikin mutanen dake falon, da sasanyan sanyin Ac din da ya gama game dakin ya fara buso mata kafin idannuwanta su fara sauka a kan jama'ar dake falon wa'inda yawancinsu tunda suka dago suka ganta basu cire dubansu a kanta ba Idan ka cire Abanta watau Malan, da daidaikun ciki da suka yi mata kallo daya suka dauke idannuwansu sai wanda shi baima dago idannuwan nasa ba sakamakon muryarta da ta yi masa kuwa a kunne
A hankali ta karasa shigowa da murnar dake shinfide saman fuskarta na yin ido hudu da Fauzy da kuma Hamza dake gefe zaune kusa da mamansu kadan
Da dan farin ciki ta rungume Fauzy tana dan kakane mata ido ta ce" Hei malama kece da wannan hijab din? Irin za'a zo gaishe da sarakuwa ko?"
Zaku biya kuɗin ku ta wannan account numbern 0225962748
Amina Maikudi Abdullahi
GTBank Naira 300 ne kacal zaku biya anyi araha an hana bashi.
Ko ku turo Recharge card ta wannan numbern wayar
08038856944 banda vtu hoton katin zaki ɗauka ki turo.
Sannan Sai ku tura shaidar biya ta wannan no din +22793811618
Ga ƴan Niger zaku biya kuɗin ku ta wannan layin +22793811618 katin sahelcom ko AIRTEL ta dala DARI ne ( 500 francs cefa) sai ku tura shaidar ta layin nawa sannan na saka ku a grup din
Sai kun zo🥰🥰🥰🥰🥰
A guje ta diba ta nufi bangarensu gannin itace za'a bugawa ludayin ko me?
Ai kam mamanta bata yi kasa da gwuiwa ba ta rufa mata baya har suka idasa shiga kafin ta ja ta tsaya gannin ta je da gudu bayan mahaifinta ta tsaya tana kallon Maman
Dan murmushi ya yi da alkur'anin dake hannunsa ya dan rufe yana kallonta ya ce" Malama wani abu muka yi ne?"
Ludayin dake hannunta ta nuna ta ce" Aban IBTISAM ka bani yarinyar nan na maka mata wannan ludayin ko zata nutsu"
Kai ya girgiza da dan sauri yana mai jin wani farin ciki da annashuwa da tuna rayuwarsu ta da ya sake fadin" Me zai hanna a gyara matsalar ta fatar baki ne ba sai an taba lafiyar jikinmu ba?"
Mamanta ta sauke yar ajiyar zuciya tana kallonsa ta ce" Mijinta fa zai dawo yau, shin a shiriricewar da suka yi harda ta rashin sannin ciwon kai?, Rashin sannin ciwon kai ne mana Abansu macen da zata yi zaune kamar jaka mijinta na hanya daga tafia? Allah na tuba ko a cikin gari ne ya yi tafiyar awa hudu wajen aiki ko zaman majalisa ai kya kokarta da abinda Allah ya malaka maki ki dan daidaita ta yadda gobe idan ya tashi yi maki gori ba dai na tsaftar jikinki, ko muhalinki, ko girkinki ba, Malama wuce ki je ki gyara masa bangarensa, ki maida hankali ki zo ki kawo kayan abincinsa daban a zuba ki kai ki kilace, ki kula da turaren wuta da na bayi da na gadonsa, sannan ki tabata kin kula da jikinki yadda ya dace .......ko shima sai na koya maki ne?" Ta karashe da dan daga muryarta kadan tana zazaro mata ido
Da sauri Shuwwa ta girgiza kanta ta fito daga bayan mahaifinta ta zagaya da gudu ta wuce a dakin gaba daya ta tafi wajen Maman Muhay dan tambayarta ky din bangarensa cike da tunani kala daban daban
Tunda take fadan, mahaifin Shuwwa ke kallonta
Zai iya cewa rabonsa da irin wannan tunanin a zuciyarsa har ya manta,
Hijabin dake jikinta kiwa sosai yake boye yar ramar da bata idasa cikewa a jikinta ba, fadan da take yi kuwa sai yar duma dumar budurwar da ta sace zuciyarsa dare daya ta dawo masa a cikin tunaninsa
Tabas zai iya cewa bai taba gannin mace mai tsaftarta ba, watau idanma tana da dati to fa idannuwansa basu gani ba, gata da kamshi, gata da dumi.............
A hankali ya samu kansa da dan hadiye yawu kadan a makoshinsa da ya dan bushe a lokacin da ta juya ta fice a dakin bayan an ja masa nasa kashedin shima ta hanyar turo bakinta kadan ta auno shagwabar dake tata ce wace ake yi masa ne ta dan dira kafarta ta ce" Ka ga dai Abanta walahi karma ka ce zaka hannani shakarta, gaba daya yaren nan na kula sun dauki marar kirkin hali da yawa sun zubar da na kirkin, ka ga NAHIDTma jira take na ce ta je ta gyara jikinta dan bakon da za'a zo da shi, aman ba komai daidai nake da y'ayanka ni kam!" Ta idasa ta juya ta bar masa wajen
Dan murmushi ya yi yana girgiza kansa ya sake bude Alkur'aninsa a kasan zuciyarsa yana ayanna abubuwa kamar haka' Wannan rayuwar ita nake so ta co gaba da wakana a tare da ni, na so na yi ta yinta har zuwa cikin kabarina......, Sai dai gashi ga dukkan alamu kwana kusa zata gagareni, domin nadin dake kaina mai rikicin da ban san ko zan iya kallonta a haka tana min girgiza ba......?' (Mamana, auntyna, dan Allah ku duba, ku bude idannuwanku ku duba, koda kune kushewa a tsufa, koda kune magarya a y'aya ya dace ku gane cewar ibada ne, haihuwar y'aya ba shine zai sa ki watsar da komai ki zubar da komai ba, tabas akoy kunya irin tamu ta hausa fulani wace ke hanna mana aikata wasu abubuwan a gaban y'ayanmu ko bakin fuska, aman na tambayeku su y'ayan har cikin dakinmu suke kwana da mu ne?, Ki iya rigima mama koda baki iya ba, ki dan ringa dan jefo shagwaba lokaci zuwa lokaci koda baba bai san me hakan yake nufi ba, ki gane mama nishadinki ne koda baba a yanzun baya andanuwa ta hanyar bed, ki gane ki dan zuba abu irin na yarintama zai saka baba kallonki da murmushi a fuskarsa ya dan dungure maki kai ya ce yau kuma shagwaba ake ji maman walida?, Yau kuma rigima ake ji uman Fatima?, Yau yan rikicin a kusa suke da alama uwar gidan Malan, ba maganar mijinki bashi da kudi a wajenki sarki ne, ba maganar mijinki babu abinda ya sani sai fushi cen dam baki koya masa walwala ba a yanzu ba zai iya koya ba, walahi ko dutse ne shi dabi'a zata shige shi, domin yau da gobe sai Allah , ke dai ki yi kokari idan kin zubar da komai ki dawo da daurin nan naki ture ka ga tsiy a gabansa, ki dan shafa jan baki ki kanne ido, idan yace to yau kuma? Ko dai a kaiki a maki rukiya ne? Rukunkume baba ki jefa shi a gado zai gane aljanu sun shigeki😌, aman fisabililahi dan kawai kin samu jika kamarni shikenan sai ki wani kashe kanki inadarma ba'a habakata?, Lada ne fa, 😌 gaskiya a daina wasa da lada gaskiya, a gyara Mama babama yana son jin dadi gaskiya, kuma tsufanki a wajenmu y'ayanki kika dan kwana biyu walahi a wajensa in kin so kika tsufa, domin kinga damar da furfurarki da yabarki ki ce sai ya maki Ampa😌, ba nufina da shekarunki ki ringa fama da kannanun kaya ba, ko daya, ko daya walahi, wani sa'in da kannanun shekarunma sai ka ga idan yannayin jikin mutun sai a hankali kannanun kayan basa yi masa kyau, ba dole bane saka su, ke dai kawai ki iya dauri 😂babu abinda bama gani ehe, a dai kula😍😍😍)
Gyaran take yi cike da takaici a kasan zuciyarta
Ba komaine ya sakata a cikin takaicin ba sai tunawa da ta yi ko a safiyar yau ta yi masa mesage kamar haka *Barka da safiya yalabai, fatan ka tashi cikin koshin lafiya? Yaya aiki? Allah ya tsare* aman ko nataciyar mayya bai turo mata da reply ba bale ta yi tunanin ya gani, to wai ko bai gannin bane? Ko kuma da wani tunani na daban ne a cikin kwakwaluwar wannan bawan Allahn ne? Koda yake idan ta ce babu ta yi karya, ta san da décision dinsa na rabuwa da ita kwana kusa, to aman ita tana gannin mutuncinsa da kimarsa a yanzu ne dan ya kwatanta kamar shi din ai dan mutunci ne ta hanyar taimakon iyayenta kau?, Aman a yanzu abinda Mamansa ta ce ya matukar bata mamaki, shin ta yaya suke so ta dauko suturarta ta kawo dakin nan ne? Wai me suke so da ita ne haka kai tsaye?
Maida hankaki ta yi ta gama gyaran sannan ta koma bangaren Mama ta shiga wanka
Kukawa da jikinta da mahaifiyarta ta ce ta kwatanta gwargwadon sanninta ta hanyar cire dukkan datin da ta san yana iya zama a jikinta sannan ta saka turare a dukan wani lungu da ta san tana da shi a jikinta komai kankantarsa
A saman kujera ta zauna ta shiga tsara sasaukar Mak'up a fuskarta, wace haka kawia ta ji tana ra'ayin a saman farin fatarta ta dan karra hoda ko yayane sannan ta gyara girarta harma ta saka kajal, ta dora da jan baki mai hawa da rantsatsan dinkin atamparta da ta ciro cikin dinkunnan da akai masu ita da yar uwarta
Sosai ta bata lokaci tana gyara har akai kiraye kirayen sallar magariba
Nan ta gabatar da sallarta, sannan ta saka kayanta ta kashe dauri irin mai tsokale idon ogan nan
Bata dauki mayafi ba, bale hijab, takalminta ta saka plate sai dai mai gashi a jikinsa sosai bayan ta saka safar da ta zame mata jiki
A tausashe take tafiya a tsakar gidan tana hankalce da yannayin gidan nasu na yau, taron sojoji ya fi na da yawa sosai, sannan du idan aka ji motsi sai an duba dan gannin ko wanene, da zarar an ga itace kuwa sai ta ga ana yi mata gaisuwa irin ta mutuntawar nan sannan a bata hanya ta wuce
Ita dai bata damu ba har ta karasa ta kama kofar ta bude da salama a bakinta ta shiga
Sansanyan kanshin turaren wuta garwaye da turarrukan jikin mutanen dake falon, da sasanyan sanyin Ac din da ya gama game dakin ya fara buso mata kafin idannuwanta su fara sauka a kan jama'ar dake falon wa'inda yawancinsu tunda suka dago suka ganta basu cire dubansu a kanta ba Idan ka cire Abanta watau Malan, da daidaikun ciki da suka yi mata kallo daya suka dauke idannuwansu sai wanda shi baima dago idannuwan nasa ba sakamakon muryarta da ta yi masa kuwa a kunne
A hankali ta karasa shigowa da murnar dake shinfide saman fuskarta na yin ido hudu da Fauzy da kuma Hamza dake gefe zaune kusa da mamansu kadan
Da dan farin ciki ta rungume Fauzy tana dan kakane mata ido ta ce" Hei malama kece da wannan hijab din? Irin za'a zo gaishe da sarakuwa ko?"