← Book details Alkalamin Kaddara ta Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 41 OF 138

Sashe 41

Alkalamin Kaddara ta Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Sannan Sai ku tura shaidar biya ta wannan no din +22793811618

Ga ƴan Niger zaku biya kuɗin ku ta wannan layin +22793811618 katin sahelcom ko AIRTEL ta dala DARI ne ( 500 francs cefa) sai ku tura shaidar ta layin nawa sannan na saka ku a grup din

Sai kun zo🥰🥰🥰🥰🥰

Bata taba tunanin hankalinta zai tashi da tashin hankalin wani dan adam a duniya dan kawai ya shiga hali na tashin hankali irin haka ba sai yau

Da rarafe ta karasa gabansa tana karra dukawa ta hade hannayenta tana girgiza kanta tana fadin" Walahi ka isa da ni, kuma kai, kai Abana ne, dan Allah ka yi hakuri, ban yi haka dan na saka ka kuka ba ko kadan, walahi nima a Abana na daukeka kaf duniya bani da wani uban da ya daraka, Abahna me ka rage min na uba da dansa? Kana tare da ni dukan abinda na kwaso ina zubewa a kanka kai kuma kana amsa kana kuma tarairayata da zuciya daya, Aba ban ce bana sonsa dan na saka ka kuka ba, iya gaskiyata ce na fada, aman ka yi hakuri walahi zan je, zan tafi bana so ka yi kukan". Gaba daya rikicewar da ta yi ya sake saka masa farin ciki da godiya ga ubangijinsa
Walahi ba dan ya sakata ta amince da auren nan ya saka shi kuka ba, har zuciyarsa ya ji ba dadi da take son bijire masa a yau da ya yi bugun kirji ba tare da ya nemi shawararta ba ya daura mata auren nan, aman a yanzu da ta nuna cewar eh shima uba ne sai ya ji farin ciki da sanyi a cikin zuciyarsa
Yana godewa Allah har wani takama yake idan ta ce da shi ABAHNA din nan, shi dai ya san yana iya haihuwarta da cikinsa idan ya yi auren shekara ashirin da uku, dan ya amsa idan ta kireshi da Aba ai ba laifi ya aikata ba ba kuma abin kunya bane, SHUWWA y'arsa ce , yana farin ciki da haka, ba sai ya nakuda ya haifa ba zai ce ga d'ansa tunda Allah ya bashi mai yi masa biyaya ya rasa mikin dake damunsa na rashin d'a a duniya

A sanyaye yana murmushi ya furta" Allah ya yi miki albarka SHUWWA, Allah ya faranta maki yadda kika faranta min, Allah ya sa alkalamin kadararki daga yanzu ya tashi daga rayuwa mai gigitarwa ya mayar da ke rayuwa mai saka shauki da farin ciki da kwonciyar hankalin zuciya, ki gane sai ka zauna fa mutun kake iya gane wanenen shi, ni gani nake shi din zai so iyalinsa sosai , kingama abokiyar zamankima a cen babar kasa take zaune, a nan ke kadai ce kuma in sha Allah ba zaki samu bacin ran zama da su baki daya ba"

'kuturu, harda mata gareshi? Koda yake ai da ganninsa zai yi hali na mai maimaita Ubaiiii yana barbara da zarar ya ga mace, hm, zama da shi? Abah zan dai je na dawo ka sama min miji , zan tafi ne dan na ga ka fara kuka, aman zan dawo maka ne da shokiiiina na mika maka takardar sakina ka sama min miji, kai auren kansa sai na hakura da shi dan na kula gigitani yake yi, rayuwa ai yar sanyi ce sosai' wannan abubuwa shine Shuwwa ke ayanawa a cen kasan zuciyarta

"Shuwwa?" Ya fada a sanyaye yana kallonta dan ta afka tunanin da har bata ji salamar gwogonsu dake fada masa cewa yan daukan amarya ne suka karaso ba

A nutse ya ce" Ki ji tsoron Allah a zamanki da shi, ki yi masa biyaya da dukan karfin iyawarki, ki sani aljanarki ce zaki je nema Shuwwa sannan ki dauka zabinki ne shi din ba hadaki akai da makiyinki ba, zaki kwatanta haka?" Malan ya fada yana sake kallonta hakan ya sa ta sake jin zuciyarta ta karye sosai, ta kalle shi, ta juya ta kalli gogonsu ta kasa furta koda A ne

Gogonsu ta yi murmushi tana zama a kusa da ita sosai ta kamo hannunta na dama tana kallonta ta ce" IBTISAM, gashi na sanki a kuraran lokaci, duda ba mutuwa mukai ni ko ke ba aman zaman aure zama ne na tafia aa rayu da miji ba shirme ba, ki sani ni mamanki ce, Allah ya jikan mahaifiyarki ba zaki kuma yin kukan maraicin rashin uwa ba, kar cenjin da kika samu ya rude ki SHUWWA jinnin dake gudu a cikin jikinki ba na ja da baya a gaban gwagwarmaya bane ko wace iri ce, uwa uba babar kokowar duniya itace ta mace da mijinta, da yardar Allah furucinsa zai dawo bege a gareki, maza yiwa Abanki salama mu tafi ba'ai masu dare a wajensu duda matar uban gidansu za'a kawo ta yiwu mu ko karfe nawa muke son shiga ko fita muna iya yi kanmu tsaye" ta karashe da dan barkwonci bata kula da kallon kun shiga uku da Shuwwar din ke binta da shi ba
Wannan jawabi da gogonsu ya saka bata daukarwa Abanta alkawarin zama lafiya da abokin gaba ba, da wannan aka luluba mata abin rufa abinda ba'a taba yi mata ba, a yau kuma uwa uba rakiyarta harda NAHIDT wace sai da aka zo shiga dankareriyar ferarin da za'a kaita a ciki Malan ya sake jadada maganar cewa daga cen a sada NAHIDT da gidan Hamza bisa umarnin manyansu
Ita dai a yau bata da ja in ja da KOWA, kai bama zasu gane bane aminiyarta da kanwarta ta aurar fa? Ai yau ita shagali takeda a gabanta mai zafin gaske, a dai kai rigimatu kurjin gwuiwar nan a dawo a ga bidi'a ta arziki, yau Malan zai gane itace Nahidht (🥺 Hum)

Lafaya ce aka nada mata a saman wando da rigarta masu santsi farare kal , hakama lafayar fara ce kall
Sun tanaji kayan nan ne saboda irin wannan lokacin da sukai tunanin zasu sadata da dakin Hamza ne
A tanadin nasu harda makup suka so cencada mata sai dai a yanzu ta tsaya a kan kafafuwanta ta nuna cewar bata cikin yaren makup, su je kawai su sadata da dakinta kowa ya kama gabansa, a cikin zuciyarta kuwa kudirinta shine abinda sunna zuwa zata biyo bayansu? Shirme suke yi da batawa kansu lokaci

Matar tsohon ganaral, watau maman Hamza da gogonsu ne rike da ita a tsakiyarsu

A hankali bayan sojojin dake tsaitsaye sun bada damar ana iya fitowa da ita Matar tsohon ganaral kasa kasa sosai ta furta" Ki karra sada kanki My daughter ta yadda yarensa ba zasu ga fuskarki cikin sauki ba, domin matar uban gidansu kike, zasu ganki ne bayan ya ganki"

Jajayen lebunnanta ta dan dantse a hankali, domin tunda aka ringa ambatar masha Allah tap wannan tsaro haka? Gabanta ya farra faduwa, saima da aka ringa fadar to wai dama haka gidan baban yake kamar a turai? Ta ji zuciyarta na yi mata mugun bugu na zartacen ka'ida

Bindigogin dake hannayensu wa'inda suka ririke su biyar a laye a bakin hanyar shiga bayan sun gama yin jawabai na oyoyo da maraba da zuwa wa madame din oga ne suka daga sama suka harba wanda hakan ya saki gigitacen karan da ya firgita dukkan wani bakon al'amarin, ya saka shauki ga wa'inda suka san ana haka kuma sai mai matsayi ake yiwa hakan watau sai matan manyan ake tarba da hakan
Cikin wa'inda karar bindigar ya zowa a ba zata harda SHUWWA , hakan ya sa ta damki hannun gogonsu muryarta cen ciki ta furta" GoGo bindiga"

Tsinkayo muryar NAHIDT cikin murna tana fadin" Kai soja duniya ne, tarbar oyoyo da kukan abin kisa ake yi, mtssss tsakani da Allah soja zan tafi" ya sakata sauke nanauyar ajiyar zuciya tana sasautawa Gogonsu rikon kasa kasa ta sake fadin" Mahaukata, komai nasu a haukace ba irin na mutane ba, komai basu kya yinsa a nutse ba sai a gigice, cen ku da bindigarku!"
Ita dai goginsu yar daria abin ya bata domin rabin jikin Shuwwa din a jikinta yake dan ta dan rankwasa jikinta sakamakon jin da ta yi santsin wajen na son dagata da dogon takalminta ya maka kasa bayan bata ra'ayin hakan, bata gannin gabanta ga jaraba sun tanaji acokal dan su cocoka gaban Hamza, asge Hamza yayansu ne? Kai jamai

Dukan yan rakiyar amaryar da suka zo sanadiyar Tsohon ganaral da mutanen Matar Malan uwar gida da matar Malan din kanta a bayansu suke, a lokacin da suka ja suka tsaya sunna shirin shiga Nahidt a sanyaye kamar ba ita ba dan Shuwwa din ta ji maganarta ta ce" Gogonmu, dan Allah ku dan tsaya Shuwwana ta yi adu'a kafin ku sadata da cikin gidanta"

Dan matsawa ta yi kusa da Shuwwar din a nutse ta shiga furta" Shuwwan Mamah, shuwwan Abanta, Shuwwan yayarta? Dan Allah ki yi adu'ar neman alkhairin auren nan kin ji? Kin ga kamar da ran iyayenmu, kina gannin wata daraja da ta lulubeki kuwa ? Gaba daya sai na yarda mai daraja kika aura, dan Allah Ibtina ki yi adu'ar shiga cikin gidan nan da fatan zaman lafia da mijinki kin ji? Ba dan ni ba"

A hankali IBTISAM ta lumshe idannuwanta sannan ta bude ta shiga dan kokarin bude gaban furkarta dan ta kalli yar uwarta da muryarta kadai take ji
Tana budewa sukai ido hudu da junna ashema a gabanta take kadan sannan ta hade hannayenta waje daya tana kallonta

Tunda aka fara lamarin daurin auren nan sai yanzu murmushi ya subuce mata a saman fuskarta da ta ga irin abinda yayarta ke yi mata idan tana so tai mata biyaya
A hankali ta saki hannyensu ta damko na yayarta sannan ta dan matsa jikinta ta rungume ta a jikinta sosai
Chapter 41 · 0% Book details