Sashe 87
Alkalamin Kaddara ta Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da sauri Shuwwa ta bi bayanta gannin ta sake juyawa zata tafi da sauri ta saka hannunta ta janyota baya ta yada ta juyo a haukace da mamaki tana kallonta
Tun daga kasa har sama Shuwwa ta daukota da kallo kafin ta sauke a saman fuskarta
Yar yatsarta manuniya ta nuna mata zaryan tana kallonta a kausashe ta ce" Ki cewa haukan dake kullawa ko kuncewa a cikin kwakwaluwarki cewar na amshi tayin, ki fadawa rayuwarki cewa da aure ko babu tabas sai na zama Barewar Zakin nan, domin sai ya farauceni ba dare ba rana dan ya ci abinda yake lafiya a gareshi watau ni da nake namana wajenshi!, Ki karra sakawa cikin zuciyarki cewa zaki baya cin zaki bale tsohon nama ai ba na Uban dawa bane!, Ki fadawa kadararki, ko nace gangancinki cewa na siya da farashi mai tsada ba gudu ba ja da baya sai na deba kuma sai na amshi kaya a duk lokacin da hakan ta kama!, Kina iya sakawa a sakeni, aman walahi ki sani sai na haukata duniyar mafarkinki ta yadda zai dawo ya zamto mumunan farkawarki!, Domin ni zahiri ce , kuma na sha iskar duniya sosai ta yadda YAR BARIKI irinki ba zata gigitani ba!, Dama kin kadaice kanki kin sha shinkafar bera an turbune ki da wannan abin kunyar, a gaba ki gani a aikace cewar ya zabeni a kanki!".........
Da mugun mamaki Nahidht ke kallonsu , tunda ta tunkaro take jin maganar Shuwwa a kausashe ya saka ta shigo da sauri
Abinda ta gani ya sakata zubawa Shuwwa ido tanai mata kallon ko ta haukace ne?
Da sauri ta kalli matar da itama mamaki ya nemi halakata ta sake bin yarinyar da ta rainawa ajawali kallo kafin ta fita da sauri tana kai hannunta wajen zuciyarta dake dokawa da gudun balakin tsoron da ya fi na kashedin da MUHAY Ya yi mata karfi
A zabure Nahidt ta juyota tana kallonta kafin ta saketa ta shiga fadin" Shikenan, shikenan, hankalinki ya kwonta, ke wannan fa itace abokiyar tagwaitakar mamansa, me ta maki da zafi da kika nuna mata kalar naki haukan ? Kin san da an sake ki an gama? Mun shiga uku yanzu Shuwwa sai da kika tsinke auren? Tabas Idan mama ta farka sai ta ci uwar ubanmu"
Shuwwa ta kai zaune dabar tana jin wani irin ciwo a zuciyarta wanda bata san dalili ba rai bace ta ce" Walahi, walahi ko ya sake ni sai na bishi irin yadda karya zata bi shi, sai na zamto tamkar bindi a jikinsa, sai ya fuskanceni na gigita rayuwarsa, yadda wannan tsohuwar guzumar take sonsa ba zata taba samunsa ba, ke Nahidt Son Muhay take yi , so irin na soyaya!"
Nahidht ta yi wani irin zabura tana sakin hijab dinta kasa
Jikinta na dan rawa ta dauko Hijab din tana kallon Shuwwa ta girgiza kanta ta ce" Ke kin ji me kika ce?"
Shuwwa ta yi wani murmushi mai ciwo tana gyada kanta
Nahidht ta yi gagawar zuwa wajen salaya ta gyara shi da kyau tana fadin" walahi talahi duniya ta zo karshe, bara na yi sallah kar a tasheta da sallah a kaina, Innalilahi Allah ka sa na auri malan kafin a busa kaho, mun shiga uku Shuwwa na shiga uku wannan matar da tsinaniya ce? Ke gaske na kasa gaisheta ashe uwata ce a bariki Innalilahi wa inna ilaihi raj'une.....Shuwwa mun shiga uku...." Haka ta yi ta sambatu, ita kuma Shuwwa din gaba daya jikinta tamkar wace aka zarewa lakkah
Ya kasance ne ta kurawa waje daya ido ta kasa fahimtar komai
Bata taba jin tsana da kyamatar a rabi abinda take jin a yanzu kamar nata ne irin kar matar nan ta rabe shi domin ai d'an y'ar uwarta ne irin na yau ba
Da wani takaici ta tashi ta fice ta nufi dakin da mahaifiyarta take ta zauna ta zuba mata ido tana kallonta
A yanzu tsafta ingataciya na tare da iyayensu, sai ramar da dan ciwon da ake magani ba dare ba rana
A haka ta tare har yar uwarta ta tardota suka zauna tare ba tare da sun yi tunanin makomarsu a kusa ba, ganni suke koda iyayensu na hali na rashin lafiya a yanzu da suke raye babu mai cin masu, ganni suke dukan wanda zai ki su shikenan ya ki su ai ga mamansu a kwonce ota zata so su! ( Uwa kennan, iyaye kennan, Allah ka gafartawa iyayenmu, ka sa su gama da duniya lafiya,, wa'inda suka rasu Allah ka jikansu, ka basu aljannah ya Allah)
__________________________________________
Bayan sallar magariba
"Ka ga, ai yaren sai ai masu uzuri ko? , Yaren sun cencenci uzuri sosai........, Abinda yake damunahhhhh, abinda na kasa hadiyewa shine zancen gaba dayansa, Meme shin dukkan abinda matanka ke yi mata kafin ka rabu da su gaskiya ne ko kuma ba gaskiya bane?, MUHAY da gaske kaine zaka ce wai saboda matarka nima sai ka bata min?, Ka ga ni fa na haifeka.....gaba daya sai nake kin yarda da maganar ban san ba tsananin sonka ke ya sa haka ko menene?, To aman idan ban yarda da maganar ba da me zan yarda? Kai ka ki zama ka yi maganar da ni..... Sam baka yarda da ni ba, kana boye min damuwarka sosai Muhay....., Shin me yake faruwa tsakaninka da mamanka???? Innalilahi wa inna ilaihi raj'une MUHYIDEEN zuciyata ciwo take yi, shin ka kai shekarun da dole zan yi hakuri da halayanka na rayu da kai a haka ne ko menene ?, Shin ya kai wajen da zan maka biyaya ne ba ka yi min ba?......"
A sanyaye CHIEF OF ARMY dake kallonta cike da tausayawa , sannan ya kalli MUHYIDEEN dake duke kansa a kasa a gabanta yana sauraronta tana kuka , gaba daya ta rikice ta shiga a duhu, so take sai an fahimtar da ita ko menene, bayan bata san rashin sanninta ya fi sanninta kwonciyar hankali ba
A sanyaye ya ce" Wife....."
Kanta take girgizawa ta ki koda kallonsa
A sanyayen ta ce" Dan Allah Abansa kar ka ce komai ka ji?, Na san so kake ka ce min na bar maganar ko? Kar na takura masa ko? Shi ga wanda ya isa ko?, Shikenan ya tashi ya tafi.....ba zan ji haushin matarsa ba domin yarinyar nan tunda na ganta na ji ina kaunarta a raina, na ji ta kwonta min a matsayin matar d'ana, harma na ji tarihinta na karra jin tausayinta da muradin talaf mata, gashinnan har yanzu bata dawo ba, ta yiwu ta tsorata da yannayina ne, bata san a cikin halin kaka naka yi nake ba, abubuwa sun shige min duhu kuma an ki a fitar da ni..........., Ai ni zan yi farin ciki ka so iyalinka fiye da kowa, sannan ka sawakewa yar mutane da baka kulawa ka barta ta tafiyarta ta samu daidai ita, aman ba zan takura maka ba idan ka ga dama ne Muhay......" Ta karashe tana cicibawa da niyar bara masu wajen, stlll kuma tana kukan
Hankalinsa ya karra tashi, sosai hankalinsa ya tashi
A rikice ya rike kafafuwanta yana sada kansa a jikin gwuiwoyinta muryarsa na fita da kyar dan furucin da zai yi bai san me zai haifar ba , ya dago idannuwansa da sukai jajajir daidai hawayenta sun sauka suka sauka a saman fuskarsa , da gagawa ya ringa girgiza Kansa ya ce"
😭😭😭😭😭😭😭 Oh rainarhhhhhhhh😌😌😌😌🥺🥺🥺🥺🥺🥺🥺😍😍😍😍😍😍😍ALK'ALAMIN KADARATAH
Na
*Sajida*
Page
5️⃣0️⃣
Da gagawa ya ringa girgiza kansa ya ce" Mahmahnah......."
Mama ta sake jin wani takaici na sake tukota dan hakaa ta janye kafarta fahimtar da ta yi baa fada mata ba zai yi ta zagaye shi da sauri ta nemi barin dakin
Chief of army ne ya yi gagawar dakatar da ita ta hanyar ambatar sunnanta kai tsaye sanann ya mike shima jikinsa a mace yana kallon bayanta
Muryarsa a sanyaye ya ce" Na so ki kasance mai hakuri da kawar da kai har Allah ya nuna maki alkhairin abin, domin tsananta bincike bashi da wani alkhairi , bashi da kyau, sai dai kashhh, kin kasance mai yawan son bin didigin abubuwa, gashi yau har kuka kike masa dan yana kare ki da bacin rai?, Hasana yaya zaki yi da gabar dake tsakanin Yaronki da yar uwarki?, Ya nisanta kansa da ita , kin matsa kin kisanto shi da ita, subahannalah, Hasana"
A dan tsorace ta juyo tana kallon Chief of army, sannan ta kalli Muhay da ya kifa kansa a jikin kujerar da ta tashi gaba daya jikinsa na jijiga kamarma wanda yake yin kuka ko menene? Tashin hankali mai girma ta ji na karra ziyartarta, sai dai a yanzu babu gudu ba ja da baya ta riga ta kawo wannan gabar bata da halin yin koma baya
Tana kallonsu Mijinta ya dan sake matsota kadan, a sanyaye ya ce" Zan iya kiran hakan da muguwar Kadara, wace ke sake samun waje a wajen wanda ya yi wasa da fadawa Allah, tabas zuciya ce bata da kashi, aman kuma Allah ya bamu hanyar da zamu iya samun kadararmu da sauki idan har muka kai masa kukanmu, kin ga da ace tun da farko da ta faraa jin irin haka ta yi kokari ta nemi shawara sannan ta sake kusanta kanta da ubangijinta , to da tabas ta samu sasaucin koma menene, sai dai kash, kadara, sakaci, muguwar taraya, son zuciya ne suka hadasa haka, kuma sakaci da adu'a ya sa abun ya sake yin tasiri a kanta....."
Sake kure fuskarsa take da kallo tana ji tamkar ta saka haannunta tta bude masa bakinsa ya yi magana ta yadda zata ji takamaiman abinda yake faruwa, domin a yanzu kwata kwata ya durmiyata a cikin wani duhun fiye da farko
Aa sanyaye ya ce" Tana son sa ne......"
Bakinsa da ya yi furucin ta tsatsare da ido kafin a sanyyaye ta dan juyar da hannunta ta ce" Abansa har yanxu baka fadi laifin ba, ka ce tana sonsa ne ka yi shiru, to wanene bai san cewa Useinata na son Son ba? Matar da a kansa sai ta batawa kowa rai? Ai tana son yarontah......"
Tun daga kasa har sama Shuwwa ta daukota da kallo kafin ta sauke a saman fuskarta
Yar yatsarta manuniya ta nuna mata zaryan tana kallonta a kausashe ta ce" Ki cewa haukan dake kullawa ko kuncewa a cikin kwakwaluwarki cewar na amshi tayin, ki fadawa rayuwarki cewa da aure ko babu tabas sai na zama Barewar Zakin nan, domin sai ya farauceni ba dare ba rana dan ya ci abinda yake lafiya a gareshi watau ni da nake namana wajenshi!, Ki karra sakawa cikin zuciyarki cewa zaki baya cin zaki bale tsohon nama ai ba na Uban dawa bane!, Ki fadawa kadararki, ko nace gangancinki cewa na siya da farashi mai tsada ba gudu ba ja da baya sai na deba kuma sai na amshi kaya a duk lokacin da hakan ta kama!, Kina iya sakawa a sakeni, aman walahi ki sani sai na haukata duniyar mafarkinki ta yadda zai dawo ya zamto mumunan farkawarki!, Domin ni zahiri ce , kuma na sha iskar duniya sosai ta yadda YAR BARIKI irinki ba zata gigitani ba!, Dama kin kadaice kanki kin sha shinkafar bera an turbune ki da wannan abin kunyar, a gaba ki gani a aikace cewar ya zabeni a kanki!".........
Da mugun mamaki Nahidht ke kallonsu , tunda ta tunkaro take jin maganar Shuwwa a kausashe ya saka ta shigo da sauri
Abinda ta gani ya sakata zubawa Shuwwa ido tanai mata kallon ko ta haukace ne?
Da sauri ta kalli matar da itama mamaki ya nemi halakata ta sake bin yarinyar da ta rainawa ajawali kallo kafin ta fita da sauri tana kai hannunta wajen zuciyarta dake dokawa da gudun balakin tsoron da ya fi na kashedin da MUHAY Ya yi mata karfi
A zabure Nahidt ta juyota tana kallonta kafin ta saketa ta shiga fadin" Shikenan, shikenan, hankalinki ya kwonta, ke wannan fa itace abokiyar tagwaitakar mamansa, me ta maki da zafi da kika nuna mata kalar naki haukan ? Kin san da an sake ki an gama? Mun shiga uku yanzu Shuwwa sai da kika tsinke auren? Tabas Idan mama ta farka sai ta ci uwar ubanmu"
Shuwwa ta kai zaune dabar tana jin wani irin ciwo a zuciyarta wanda bata san dalili ba rai bace ta ce" Walahi, walahi ko ya sake ni sai na bishi irin yadda karya zata bi shi, sai na zamto tamkar bindi a jikinsa, sai ya fuskanceni na gigita rayuwarsa, yadda wannan tsohuwar guzumar take sonsa ba zata taba samunsa ba, ke Nahidt Son Muhay take yi , so irin na soyaya!"
Nahidht ta yi wani irin zabura tana sakin hijab dinta kasa
Jikinta na dan rawa ta dauko Hijab din tana kallon Shuwwa ta girgiza kanta ta ce" Ke kin ji me kika ce?"
Shuwwa ta yi wani murmushi mai ciwo tana gyada kanta
Nahidht ta yi gagawar zuwa wajen salaya ta gyara shi da kyau tana fadin" walahi talahi duniya ta zo karshe, bara na yi sallah kar a tasheta da sallah a kaina, Innalilahi Allah ka sa na auri malan kafin a busa kaho, mun shiga uku Shuwwa na shiga uku wannan matar da tsinaniya ce? Ke gaske na kasa gaisheta ashe uwata ce a bariki Innalilahi wa inna ilaihi raj'une.....Shuwwa mun shiga uku...." Haka ta yi ta sambatu, ita kuma Shuwwa din gaba daya jikinta tamkar wace aka zarewa lakkah
Ya kasance ne ta kurawa waje daya ido ta kasa fahimtar komai
Bata taba jin tsana da kyamatar a rabi abinda take jin a yanzu kamar nata ne irin kar matar nan ta rabe shi domin ai d'an y'ar uwarta ne irin na yau ba
Da wani takaici ta tashi ta fice ta nufi dakin da mahaifiyarta take ta zauna ta zuba mata ido tana kallonta
A yanzu tsafta ingataciya na tare da iyayensu, sai ramar da dan ciwon da ake magani ba dare ba rana
A haka ta tare har yar uwarta ta tardota suka zauna tare ba tare da sun yi tunanin makomarsu a kusa ba, ganni suke koda iyayensu na hali na rashin lafiya a yanzu da suke raye babu mai cin masu, ganni suke dukan wanda zai ki su shikenan ya ki su ai ga mamansu a kwonce ota zata so su! ( Uwa kennan, iyaye kennan, Allah ka gafartawa iyayenmu, ka sa su gama da duniya lafiya,, wa'inda suka rasu Allah ka jikansu, ka basu aljannah ya Allah)
__________________________________________
Bayan sallar magariba
"Ka ga, ai yaren sai ai masu uzuri ko? , Yaren sun cencenci uzuri sosai........, Abinda yake damunahhhhh, abinda na kasa hadiyewa shine zancen gaba dayansa, Meme shin dukkan abinda matanka ke yi mata kafin ka rabu da su gaskiya ne ko kuma ba gaskiya bane?, MUHAY da gaske kaine zaka ce wai saboda matarka nima sai ka bata min?, Ka ga ni fa na haifeka.....gaba daya sai nake kin yarda da maganar ban san ba tsananin sonka ke ya sa haka ko menene?, To aman idan ban yarda da maganar ba da me zan yarda? Kai ka ki zama ka yi maganar da ni..... Sam baka yarda da ni ba, kana boye min damuwarka sosai Muhay....., Shin me yake faruwa tsakaninka da mamanka???? Innalilahi wa inna ilaihi raj'une MUHYIDEEN zuciyata ciwo take yi, shin ka kai shekarun da dole zan yi hakuri da halayanka na rayu da kai a haka ne ko menene ?, Shin ya kai wajen da zan maka biyaya ne ba ka yi min ba?......"
A sanyaye CHIEF OF ARMY dake kallonta cike da tausayawa , sannan ya kalli MUHYIDEEN dake duke kansa a kasa a gabanta yana sauraronta tana kuka , gaba daya ta rikice ta shiga a duhu, so take sai an fahimtar da ita ko menene, bayan bata san rashin sanninta ya fi sanninta kwonciyar hankali ba
A sanyaye ya ce" Wife....."
Kanta take girgizawa ta ki koda kallonsa
A sanyayen ta ce" Dan Allah Abansa kar ka ce komai ka ji?, Na san so kake ka ce min na bar maganar ko? Kar na takura masa ko? Shi ga wanda ya isa ko?, Shikenan ya tashi ya tafi.....ba zan ji haushin matarsa ba domin yarinyar nan tunda na ganta na ji ina kaunarta a raina, na ji ta kwonta min a matsayin matar d'ana, harma na ji tarihinta na karra jin tausayinta da muradin talaf mata, gashinnan har yanzu bata dawo ba, ta yiwu ta tsorata da yannayina ne, bata san a cikin halin kaka naka yi nake ba, abubuwa sun shige min duhu kuma an ki a fitar da ni..........., Ai ni zan yi farin ciki ka so iyalinka fiye da kowa, sannan ka sawakewa yar mutane da baka kulawa ka barta ta tafiyarta ta samu daidai ita, aman ba zan takura maka ba idan ka ga dama ne Muhay......" Ta karashe tana cicibawa da niyar bara masu wajen, stlll kuma tana kukan
Hankalinsa ya karra tashi, sosai hankalinsa ya tashi
A rikice ya rike kafafuwanta yana sada kansa a jikin gwuiwoyinta muryarsa na fita da kyar dan furucin da zai yi bai san me zai haifar ba , ya dago idannuwansa da sukai jajajir daidai hawayenta sun sauka suka sauka a saman fuskarsa , da gagawa ya ringa girgiza Kansa ya ce"
😭😭😭😭😭😭😭 Oh rainarhhhhhhhh😌😌😌😌🥺🥺🥺🥺🥺🥺🥺😍😍😍😍😍😍😍ALK'ALAMIN KADARATAH
Na
*Sajida*
Page
5️⃣0️⃣
Da gagawa ya ringa girgiza kansa ya ce" Mahmahnah......."
Mama ta sake jin wani takaici na sake tukota dan hakaa ta janye kafarta fahimtar da ta yi baa fada mata ba zai yi ta zagaye shi da sauri ta nemi barin dakin
Chief of army ne ya yi gagawar dakatar da ita ta hanyar ambatar sunnanta kai tsaye sanann ya mike shima jikinsa a mace yana kallon bayanta
Muryarsa a sanyaye ya ce" Na so ki kasance mai hakuri da kawar da kai har Allah ya nuna maki alkhairin abin, domin tsananta bincike bashi da wani alkhairi , bashi da kyau, sai dai kashhh, kin kasance mai yawan son bin didigin abubuwa, gashi yau har kuka kike masa dan yana kare ki da bacin rai?, Hasana yaya zaki yi da gabar dake tsakanin Yaronki da yar uwarki?, Ya nisanta kansa da ita , kin matsa kin kisanto shi da ita, subahannalah, Hasana"
A dan tsorace ta juyo tana kallon Chief of army, sannan ta kalli Muhay da ya kifa kansa a jikin kujerar da ta tashi gaba daya jikinsa na jijiga kamarma wanda yake yin kuka ko menene? Tashin hankali mai girma ta ji na karra ziyartarta, sai dai a yanzu babu gudu ba ja da baya ta riga ta kawo wannan gabar bata da halin yin koma baya
Tana kallonsu Mijinta ya dan sake matsota kadan, a sanyaye ya ce" Zan iya kiran hakan da muguwar Kadara, wace ke sake samun waje a wajen wanda ya yi wasa da fadawa Allah, tabas zuciya ce bata da kashi, aman kuma Allah ya bamu hanyar da zamu iya samun kadararmu da sauki idan har muka kai masa kukanmu, kin ga da ace tun da farko da ta faraa jin irin haka ta yi kokari ta nemi shawara sannan ta sake kusanta kanta da ubangijinta , to da tabas ta samu sasaucin koma menene, sai dai kash, kadara, sakaci, muguwar taraya, son zuciya ne suka hadasa haka, kuma sakaci da adu'a ya sa abun ya sake yin tasiri a kanta....."
Sake kure fuskarsa take da kallo tana ji tamkar ta saka haannunta tta bude masa bakinsa ya yi magana ta yadda zata ji takamaiman abinda yake faruwa, domin a yanzu kwata kwata ya durmiyata a cikin wani duhun fiye da farko
Aa sanyaye ya ce" Tana son sa ne......"
Bakinsa da ya yi furucin ta tsatsare da ido kafin a sanyyaye ta dan juyar da hannunta ta ce" Abansa har yanxu baka fadi laifin ba, ka ce tana sonsa ne ka yi shiru, to wanene bai san cewa Useinata na son Son ba? Matar da a kansa sai ta batawa kowa rai? Ai tana son yarontah......"