Sashe 57
Alkalamin Kaddara ta Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ga ƴan Niger zaku biya kuɗin ku ta wannan layin +22793811618 katin sahelcom ko AIRTEL ta dala DARI ne ( 500 francs cefa) sai ku tura shaidar ta layin nawa sannan na saka ku a grup din
Sai kun zo🥰🥰🥰🥰🥰
A sanyaye ta budi bakinta ta ce" Amen wa alaikumus salaam warahamatulah wa barakatuhu........"
Sai kuma ta samu kanta da sake sada kanta a hankali taa furta" Barka da safiya "
Kasa kasa Nahidt ta ce" Ke wuni ne"
Muryarta ta shiga dan rawa ta samu kanta da fadin" Wuni, wuni ne, Barka da wuni"
Mama ta ringa sakin murmushi a nutse ta ce" Barka da warhaka y'ata, fatan kina cikin koshin lafia, yaya bakunta?"
SHUWWA ta samu kanta da jin nauyin matar da kuma son ta yi mata biyaya, ji take kamar muryar matar ne ke sakata yin biyaya koda bata shiryawa hakan ba
A sanyaye tamkar ba ita ba ta budi bakinta muryarta kasa kasa sosai bayan zakinta ta karra mata biyaya wanda koda mutun ya ki fadin ne ba zai ce muryar nan bata saja masa jin wani iri har cikin zuciyarsa ba, da dan inda inda ta furta" Alhamdulilah"
Daga tsayen da yake a kansu yana kallon gefe ya samu kansa da juyowa yana kallonta, ba dan wani abu ba sai dan ya gaskata kunnayensa da tunanin ko yayar tata ce ta amshi wayar ne ta yi magana a hankali irin na masu hankali? Domin shi dai tunfa ya santa da biyaya ya santa, kanwar ce bata da hankali
Da fara'a Mama ta ce" Masha Allah, Allah ya miki albarka, in sha Allah sai kin zo kin ji? Ina nan ina jiranki da izinin Ubangiji"
SHUWWA ta dan kalli fuskar Nahidt dake rike mata da wayar a hankali ta ce" To Mama, a gaida Aba da mutanen gidan in sha Allah"
Mama kam da farin cikinta ta ce" Amen zasu ji yarinyata, na gode sai an jima"
Kai ta gyada ta kasa fadin wata maganar har wayar ta bada hasken dake nuna ta mutu
Tana kula da kiran ya mutu ta dora mata wayar a saman cinyarta
Hamza da ya mike tsaye yana fadin tafi ne suka kalla su dukansu
Hannunta ta saka ta kamo nasa tana kallonsa aa sanyaye ta ce" Haba yayanmu, tafia zaka yi min da ita? Dan Allah ka barta tare da ni"
Hannun nasu ya bi da kallo, ya sake kallon wayarsa dake saman cinyarta
Baki ya sake tabewa ya juya ya nufi sama ba tare da ya furta masu ci kanku ba,
Da kyar suka iya daidaita tsakaninsu bayan Hamza ya fahimta sannan ya yarda cewa daga an kwana biyu zata koma wajensa ne ya iya tabo mahaifinsa cewar zai koma ya gama , a nan mahaifinsa ya tabo Number Muhyideen dake saman cinyar SHUWWAR, a kan dole ta mike ta nufi sama tana ta gungunnin barin wayar da ya yi ta nufi dakinsa dan ta kai masa wayar su kuma sunna jira ya amsa dan ya bada damar zai fita a barikin a wannan lokacin a raka shi har cikin gari saboda tsaro
Bugawa ta fara yi kamar sau hudu, kafin ya saka hannunta ta murda ta shiga gaba dayanta tana mai yin salama a dan dage
Ido cikin ido sukai da junna domin tunda ta fara buga masan ya tabata cewar sabuwar tsagerar dake kawowa nutsuwa da kwonciyar hankalinsa farmaki ce, dan kaf cikin barikin nan ko mashaya giya ba zasu sha su nufo nan su aikata mumunan aikin nan ba gaskiya, wannan aiki na bakon gari ne mai son halaka kansa ido rufe
A hankali ta janye idannuwanta a cikin nasa tana sauke ajiyar zuciya hadi da rike gefen rigarta da karfi tana son controlling din abunda take tunanin ko tsoro ne ta ji sanadiyar ido hudun da sukai da wannan mutumen domin gabanta ne ya yanke ya fadi a lokacin da ta kalli fuskarsa wace take cikin yannayi na ba yabo ba falasa
Dan murmushi ta yi tana sake aro jarumta ta shiga fadin" Dama, Dama, Dama kira ne yake shigowa, shine na ce bara na kawo maka wayar ka mantata a cen kasa ne"
Hannun nata dake miko masa wayar ya kurawa ido kafin ya maida dubansa saman fuskarta
Gefe take kallo, ko yace kirjinsa take kallo
A dan nutse ya ce" Waye shi?"
A hankali ta dan dago tana kallon fuskarsa ta ce" Ban sani ba na dai ga an rubuta Father"
Idannuwansa ya maida gefe ya sake maidowa kanta yana girgiza kai da tunanin ta yiwu jaka ce bata da ilimi sam, ta yaya zata yi tunanin zai mata tambayar waye mutumen dake kira a wayarsa bale ta ga sarai me aka rubuta, ko bata iya karantawa ba sai a magana ne ta dan koyi kadan kadan?
"Look, Allah ya sa tare kuka fito duniya kar na kuma gannin kin zaune gabansa ba hijabin dake kare mutuninki na mace, sannan kar na kuma gannin kina magana kina shafarsa ki yi hakurin aikata hakan daga nan har zuwa lokacin da zamu saki hannun junna dan bama so sanadiyar kina karkashin ikona a matsayin wanda ya aureki na fada wutar jahanama dan Annabi ya fada duk mutumen da baya kishin iyalinsa dan wuta ne, bai bambance iyalin naka wanda kake so, ko wanda baka so ba, dan bariki ko tsaftatace ba, cewa dai ya yi duk mutumen da baya kishin iyalinsa dan wuta........bana tunanin kin kai matsayin da zan yi sake na fada wuta saboda ke, game din ba riba......ki kama mutuncin kanki ki iya bambance bariki da gidan aurena!".................................... A kausashe ya yi furucinsa, a hade ya fadi abinda ke cikin tunaninsa, a zafafe ya isar da sakonsa, sannan sai da ya damki damtsen hannunta ya dago da dan karfin da ya saka ta bashi dukan hankalinta harma ta gane cewar furucinsa ba karya yake nufi ba, gaskiyarsa yake nufi yanai mata kashedi ne a kan ta kiyaye kar ta aikata zina da yayanta a cikin gidansa
A hankali ta raka bayansa da kallo, har bayan ya rufo kofar da karfin da ya saka Idannuwanta kirftawa a sekwond daya suka kuma budewa a yan sekwani,
A hankali ta shiga taka kafafuwanta tana nufar Wajen da ya bi ya fita har ta fice a dakin itama ta tsaya daga sama tana kallon lokacin da suka yi gaba da shi da yayunta sukaiwa Hamza rakiya ya fice tana kallon kofar har ta ga an bude an shigi, Nahidt ta nufi dakinta tana yar dariya, cen kuma sai ta ga an bude ya bayana ya shigo kamar yadda ya saba shigowa, wannan karron direct ya nufi wajen kayan abincin nan ya hau ya zauna ga dukan alamu abincin ne zai ci
A hankali ta lumshe idannuwanta da dan karfin da ya sakata jin dumi dumi , danshi danshi na bin kumatunta hakan ya sa a hankali ta saka hannunta na dama ta shafa abin a hannunta ta dauko yatsarta tana kallo
Juyawa ta yi jikinta tamkar babu laka ta nufi dakinta ta murda ta shige a hankali ta nufi bakin bed ta zauna tana kallon kasa
Mayafin abayarta ta saka hannunta tana shafawa wajen goshinta dan ta ji shin rufarta ta yaye a jikinta ne?
Sai dai ta ji a rufe gashinta yake ruffffffffff tun daurin da ta yi a dakin NAHIDT
A hankali ta dora hannunta saman kirjinta tana rintse idannuwanta a sanyaye ta ce" Ban yi tunanin mutun mai ilimi, da girma, da hankali, wanda ke gwagwarmaya da kalolin mararsa jin magana, wanda ya shanye su a cikin kwakwaluwarsa da rashin jinsu da komai zai iya aikata aiki irin wannan ba...................., Kana nufin ka ce min kana hanna ni kokarin kusantar zina da yayana a cikin gidanka???????"
Idannuwanta ta sake rintsewa hakan ya sa wasu zazafan hawaye suka shiga silalo mata a saman kumatunta ta sake cewa" Duka lalacewar tamu ce ta kai haka ko kuma rashin gata ne ya sa ake jifanmu da kazamin tunanin irin haka?, MUHAY me na aikata da zafi haka da har zaka kwatanta irin wannan a kaina?, Me ya saka ka a cikin duhun da har kake neman saka zuciyata mai rauni da sanyi a saman wannan sha'ani, mai saurin kawar da damuwa dan kar tai min ila, mai matukar yin takatsantsan da aikin nan na zina, na rufe ido nake warto aure ido rufe, ba ruwana da yaro ko tsoro ni dai na raya sunnar ma'aiki, na shigo nima a gidanka ba da rokona ko son raina ba, asalima kai din nan ka saka kaki bayan haka kawai masu kaki basu yi min ba a rayuwata, a haka ne ka dangantani da mumunan aiki haka Why?"............................................. Ta idasa maganar ta fitowa da gursheken kukan da ya saka ta dora kanta saman filonta tana yi har kasan zuciyarta kafin ta sake lumshe idannuwanta tana dannar kirjinta a kasan zuciyarta ta ci gaba da maganarta kamar haka' Na san ni ba kowa bace, aman mutun ce ni da ya dace idan za'ai min magana a kiyaye yi min wace zata tarwatsa min farin cikina harma ta sakani zubar da hawaye.....shin kai baka san ba magana mai dadima sadaka ce in ji ma'aikin Allah? Ko kuma a cikin kokarin kaucewa fadawa wutar jahanamar da kake son yi a kan mutun marar mahinmanci irina a rayuwarka kana da zabe ne? Ko ka manta a cikin hakokin da aka wajabta maka wa'inda suke iya kaika wutar idan baka kiyaye ba akoy masu tsaurin da kake takewa hankali kwonce, kai ko dai kai ana baka zabi ne na rayuwa da yadda zaka tafiyar da ita ko dan kana wani kana da damar wulakantani hankali kwonce? Ko so kake ka nuna min dan ina mace an rigaya an yini a cikin wadda maza ke takawa a lokacin da sukai ra'ayi su wulakanta idan hakan ta raya masu?.............'
Sake rukunkume jikinta ta yi tana mamakin irina yadda maganar nan ke neman kasara dukan wani farin cikinta da kwonciyar hankalinta har idannuwanta suka sauka a kan boyayen abin da bata taba ankara cewar akoyshi a dakin barcinta ba
Sai kun zo🥰🥰🥰🥰🥰
A sanyaye ta budi bakinta ta ce" Amen wa alaikumus salaam warahamatulah wa barakatuhu........"
Sai kuma ta samu kanta da sake sada kanta a hankali taa furta" Barka da safiya "
Kasa kasa Nahidt ta ce" Ke wuni ne"
Muryarta ta shiga dan rawa ta samu kanta da fadin" Wuni, wuni ne, Barka da wuni"
Mama ta ringa sakin murmushi a nutse ta ce" Barka da warhaka y'ata, fatan kina cikin koshin lafia, yaya bakunta?"
SHUWWA ta samu kanta da jin nauyin matar da kuma son ta yi mata biyaya, ji take kamar muryar matar ne ke sakata yin biyaya koda bata shiryawa hakan ba
A sanyaye tamkar ba ita ba ta budi bakinta muryarta kasa kasa sosai bayan zakinta ta karra mata biyaya wanda koda mutun ya ki fadin ne ba zai ce muryar nan bata saja masa jin wani iri har cikin zuciyarsa ba, da dan inda inda ta furta" Alhamdulilah"
Daga tsayen da yake a kansu yana kallon gefe ya samu kansa da juyowa yana kallonta, ba dan wani abu ba sai dan ya gaskata kunnayensa da tunanin ko yayar tata ce ta amshi wayar ne ta yi magana a hankali irin na masu hankali? Domin shi dai tunfa ya santa da biyaya ya santa, kanwar ce bata da hankali
Da fara'a Mama ta ce" Masha Allah, Allah ya miki albarka, in sha Allah sai kin zo kin ji? Ina nan ina jiranki da izinin Ubangiji"
SHUWWA ta dan kalli fuskar Nahidt dake rike mata da wayar a hankali ta ce" To Mama, a gaida Aba da mutanen gidan in sha Allah"
Mama kam da farin cikinta ta ce" Amen zasu ji yarinyata, na gode sai an jima"
Kai ta gyada ta kasa fadin wata maganar har wayar ta bada hasken dake nuna ta mutu
Tana kula da kiran ya mutu ta dora mata wayar a saman cinyarta
Hamza da ya mike tsaye yana fadin tafi ne suka kalla su dukansu
Hannunta ta saka ta kamo nasa tana kallonsa aa sanyaye ta ce" Haba yayanmu, tafia zaka yi min da ita? Dan Allah ka barta tare da ni"
Hannun nasu ya bi da kallo, ya sake kallon wayarsa dake saman cinyarta
Baki ya sake tabewa ya juya ya nufi sama ba tare da ya furta masu ci kanku ba,
Da kyar suka iya daidaita tsakaninsu bayan Hamza ya fahimta sannan ya yarda cewa daga an kwana biyu zata koma wajensa ne ya iya tabo mahaifinsa cewar zai koma ya gama , a nan mahaifinsa ya tabo Number Muhyideen dake saman cinyar SHUWWAR, a kan dole ta mike ta nufi sama tana ta gungunnin barin wayar da ya yi ta nufi dakinsa dan ta kai masa wayar su kuma sunna jira ya amsa dan ya bada damar zai fita a barikin a wannan lokacin a raka shi har cikin gari saboda tsaro
Bugawa ta fara yi kamar sau hudu, kafin ya saka hannunta ta murda ta shiga gaba dayanta tana mai yin salama a dan dage
Ido cikin ido sukai da junna domin tunda ta fara buga masan ya tabata cewar sabuwar tsagerar dake kawowa nutsuwa da kwonciyar hankalinsa farmaki ce, dan kaf cikin barikin nan ko mashaya giya ba zasu sha su nufo nan su aikata mumunan aikin nan ba gaskiya, wannan aiki na bakon gari ne mai son halaka kansa ido rufe
A hankali ta janye idannuwanta a cikin nasa tana sauke ajiyar zuciya hadi da rike gefen rigarta da karfi tana son controlling din abunda take tunanin ko tsoro ne ta ji sanadiyar ido hudun da sukai da wannan mutumen domin gabanta ne ya yanke ya fadi a lokacin da ta kalli fuskarsa wace take cikin yannayi na ba yabo ba falasa
Dan murmushi ta yi tana sake aro jarumta ta shiga fadin" Dama, Dama, Dama kira ne yake shigowa, shine na ce bara na kawo maka wayar ka mantata a cen kasa ne"
Hannun nata dake miko masa wayar ya kurawa ido kafin ya maida dubansa saman fuskarta
Gefe take kallo, ko yace kirjinsa take kallo
A dan nutse ya ce" Waye shi?"
A hankali ta dan dago tana kallon fuskarsa ta ce" Ban sani ba na dai ga an rubuta Father"
Idannuwansa ya maida gefe ya sake maidowa kanta yana girgiza kai da tunanin ta yiwu jaka ce bata da ilimi sam, ta yaya zata yi tunanin zai mata tambayar waye mutumen dake kira a wayarsa bale ta ga sarai me aka rubuta, ko bata iya karantawa ba sai a magana ne ta dan koyi kadan kadan?
"Look, Allah ya sa tare kuka fito duniya kar na kuma gannin kin zaune gabansa ba hijabin dake kare mutuninki na mace, sannan kar na kuma gannin kina magana kina shafarsa ki yi hakurin aikata hakan daga nan har zuwa lokacin da zamu saki hannun junna dan bama so sanadiyar kina karkashin ikona a matsayin wanda ya aureki na fada wutar jahanama dan Annabi ya fada duk mutumen da baya kishin iyalinsa dan wuta ne, bai bambance iyalin naka wanda kake so, ko wanda baka so ba, dan bariki ko tsaftatace ba, cewa dai ya yi duk mutumen da baya kishin iyalinsa dan wuta........bana tunanin kin kai matsayin da zan yi sake na fada wuta saboda ke, game din ba riba......ki kama mutuncin kanki ki iya bambance bariki da gidan aurena!".................................... A kausashe ya yi furucinsa, a hade ya fadi abinda ke cikin tunaninsa, a zafafe ya isar da sakonsa, sannan sai da ya damki damtsen hannunta ya dago da dan karfin da ya saka ta bashi dukan hankalinta harma ta gane cewar furucinsa ba karya yake nufi ba, gaskiyarsa yake nufi yanai mata kashedi ne a kan ta kiyaye kar ta aikata zina da yayanta a cikin gidansa
A hankali ta raka bayansa da kallo, har bayan ya rufo kofar da karfin da ya saka Idannuwanta kirftawa a sekwond daya suka kuma budewa a yan sekwani,
A hankali ta shiga taka kafafuwanta tana nufar Wajen da ya bi ya fita har ta fice a dakin itama ta tsaya daga sama tana kallon lokacin da suka yi gaba da shi da yayunta sukaiwa Hamza rakiya ya fice tana kallon kofar har ta ga an bude an shigi, Nahidt ta nufi dakinta tana yar dariya, cen kuma sai ta ga an bude ya bayana ya shigo kamar yadda ya saba shigowa, wannan karron direct ya nufi wajen kayan abincin nan ya hau ya zauna ga dukan alamu abincin ne zai ci
A hankali ta lumshe idannuwanta da dan karfin da ya sakata jin dumi dumi , danshi danshi na bin kumatunta hakan ya sa a hankali ta saka hannunta na dama ta shafa abin a hannunta ta dauko yatsarta tana kallo
Juyawa ta yi jikinta tamkar babu laka ta nufi dakinta ta murda ta shige a hankali ta nufi bakin bed ta zauna tana kallon kasa
Mayafin abayarta ta saka hannunta tana shafawa wajen goshinta dan ta ji shin rufarta ta yaye a jikinta ne?
Sai dai ta ji a rufe gashinta yake ruffffffffff tun daurin da ta yi a dakin NAHIDT
A hankali ta dora hannunta saman kirjinta tana rintse idannuwanta a sanyaye ta ce" Ban yi tunanin mutun mai ilimi, da girma, da hankali, wanda ke gwagwarmaya da kalolin mararsa jin magana, wanda ya shanye su a cikin kwakwaluwarsa da rashin jinsu da komai zai iya aikata aiki irin wannan ba...................., Kana nufin ka ce min kana hanna ni kokarin kusantar zina da yayana a cikin gidanka???????"
Idannuwanta ta sake rintsewa hakan ya sa wasu zazafan hawaye suka shiga silalo mata a saman kumatunta ta sake cewa" Duka lalacewar tamu ce ta kai haka ko kuma rashin gata ne ya sa ake jifanmu da kazamin tunanin irin haka?, MUHAY me na aikata da zafi haka da har zaka kwatanta irin wannan a kaina?, Me ya saka ka a cikin duhun da har kake neman saka zuciyata mai rauni da sanyi a saman wannan sha'ani, mai saurin kawar da damuwa dan kar tai min ila, mai matukar yin takatsantsan da aikin nan na zina, na rufe ido nake warto aure ido rufe, ba ruwana da yaro ko tsoro ni dai na raya sunnar ma'aiki, na shigo nima a gidanka ba da rokona ko son raina ba, asalima kai din nan ka saka kaki bayan haka kawai masu kaki basu yi min ba a rayuwata, a haka ne ka dangantani da mumunan aiki haka Why?"............................................. Ta idasa maganar ta fitowa da gursheken kukan da ya saka ta dora kanta saman filonta tana yi har kasan zuciyarta kafin ta sake lumshe idannuwanta tana dannar kirjinta a kasan zuciyarta ta ci gaba da maganarta kamar haka' Na san ni ba kowa bace, aman mutun ce ni da ya dace idan za'ai min magana a kiyaye yi min wace zata tarwatsa min farin cikina harma ta sakani zubar da hawaye.....shin kai baka san ba magana mai dadima sadaka ce in ji ma'aikin Allah? Ko kuma a cikin kokarin kaucewa fadawa wutar jahanamar da kake son yi a kan mutun marar mahinmanci irina a rayuwarka kana da zabe ne? Ko ka manta a cikin hakokin da aka wajabta maka wa'inda suke iya kaika wutar idan baka kiyaye ba akoy masu tsaurin da kake takewa hankali kwonce, kai ko dai kai ana baka zabi ne na rayuwa da yadda zaka tafiyar da ita ko dan kana wani kana da damar wulakantani hankali kwonce? Ko so kake ka nuna min dan ina mace an rigaya an yini a cikin wadda maza ke takawa a lokacin da sukai ra'ayi su wulakanta idan hakan ta raya masu?.............'
Sake rukunkume jikinta ta yi tana mamakin irina yadda maganar nan ke neman kasara dukan wani farin cikinta da kwonciyar hankalinta har idannuwanta suka sauka a kan boyayen abin da bata taba ankara cewar akoyshi a dakin barcinta ba