Sashe 105
Alkalamin Kaddara ta Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Dad ya sauke wata irin ajiyar zuciya yana fadin" Ban san yaya zan kwatanta maka abinda yake faruwa ba, an yi faduwa daidai da rashin lafiyarta, wai tana fama da zazafar zazabin nan mai saka surutu, ka ga dai yanzu likita ya jona mata magani jikinta ne ya dauki wani irin zafi sosai Son, na rasa gane menene rashin lafiyar nan kuma......."
Zai yi magana ya ringa jiyo salalamin mutanen dake zagaye da matar Father, sannan ya ringa jin hatsaniya irin sosai din nan, kai harma da furuci kamar haka"Hajia me kike yi haka kar ki cire suturarki mana hajia Innalilahi wa inna ilaihi raj'une menene wannan?"
Da sauri ya kalli wayar domin ba'a yanke kiran ba saima muryar Fathern da ya ji yana fadin" Menene wannan kamar kamun aljannu?, Ke? Ke? Hajia meye wannan kuma?"
Hakan ya sa da dan sauri ya sake kafe fuskarta da kallo yana datse kiran da tunanin abinda ya dace ya yi , ga barcinsa ba wai barinsa ya yi domin maganin yana saka barci sosai, ko yanzu da kyar ya iya mikewa sallar nan
Juyawa ya yi da nufin tafia, sai dai muryarta ta dakatar da shi a lokacin da ta hadasa masa da bugawar zuciya da ta furta" Ina zaka je kuma? Ya ja yaa tsaya yana rike da labulen kofar fitar sannan ya juyo yana kallonta hakan ya sa ta dan daburce kadan tana sosa gaban goshinta ta ce" Gani na yi dare ya yi fa, kuma baka cikin shirin fita aikin dare ko?"
Har ta dire maganar lebenta yake kallo da tuna moment dinsa na dazu da ita
A hankali ya saki kofar ya nufota, hakan ya saka gabanta faduwa, sai dai bata gudu ba ta dake tana kuma kallon fuskarsa
Yana zuwa ya tsaya yana kallon fuskarta ya ce" Kar na fita ne?"
Dan tsuru ta yi tana tambayar kanta tambayar tasa kamar wace take son gane yaren, sai kuma ta dan gumtse bakinta ta bude ta ce" Gani na yi baka ci abincin da kuma ruwan ba gayacen a rufe yadda na barshi"
Wajen abincin ya kai dubansa wanda sai yanzuma shi ya kula da shi har ga Allah, to in ba ita ba ai wata yinwar ta kori wata gaskiya
Bakinsa ya tabr ya juya yana fadin" Cinye abinki na koshi!"
Da ido ta raka shi har ya bacewa ganninta kafin ta sake sauke ajiyar zuciya tana shafa dogon karan hancinta hadi da lumshe idannuwanta ta nufi dakin barcinsa dan gyara masa bed dinsa da tatare gajeran wandonsa dan ta tabata ba zai taba shiryuwa da yarda gajeran wando ba a inda ya cire shi!
______________________________________
Da Mugun sauri ya idasa shiga wajen da likitar sojan ta kawo shi ta nuna masa cewar matar Dad na ciki da likitoci a tare da ita da su Dad din
Hankalinsa tashe ya shiga yana kallon yadda likitan nan ke magana su Dad gaba daya hankalinsu a kansa ga kuma gefe daya likitoci mata biyu da su Mama na ririke da ita tana ta fuzga tana dumumuwa mararsa dadin sauraro masu kamanceceniya da tonon silili da bugun kirji da fitsarar harshe da komai , sannan sai ihun a barta mutuwa zata yi ta yi gunduwa gunduwa take yi, abu shi ba na mai iska ba, shi ba na mai fitar rai ba, shi ba na mahaukaci ba, abu dai abun mamaki da tsoro , abun rikita zuciya tashi daya abun haukata bawa
Likitan ya sake fadin" CHIEF, abinda ke hadasa irin wannan crise din ba komai bane sai rashin lafiya fa muke kira da NERO PALU, shi Nero palu zan iya kwatanta maka shi a matsayin muguwar masasara, watau zazabin dake kama jiki ya cinye karfin jiki har ya haye ya nemi taba kwakwaluwa, tabas wannan zazabi yana da hadari sosai domin bama fatan rashin lafiya ta yiwa mutun yawa har ta kaishi da haka, wannam zazabin idan ya rike mutun mukan hada dukan kokarinmu bayan mun fara rike Allah, domin yana saka mutun ya yi har fiye da haka, ciki harda dabi'u irin na mahaukaci, tube suturar jiki, zage zage, kokowa, neman fita da gudu, sakin kashi a jiki, yakushi ne, dukka ne, magangannu ne masu muni sosai, domin akan shafe dukan wani hankaki na bawa ne a zuba masa rashin hankalin, daidaiku ke yin irin rashin lafiyar nan a cikin hali na summa, dayawansu kuwa idan suka tafi duniyar summan basa dawowa shikenan, wannan zazabi yana da hadarin gaske domin wasun idan suka dawo hayacinsu kwakwaluwarsu na tabuwa, wasu zasu jima sunna yin jinya, wasun kuma sai ka ga Allah ya taimaka sun tashi garas abinsu............ Ba maganar aljannu bane wannan kar ku ce zaku tafi da ita , ku yi hakuri mu daureta haka dan kar ta lahanta jikinta sannan ta lahanta na kusa da ita, in sha Allah zamu bi crise din nan sau da kafa har ta dakatar sai mu saka mata magungunnan fa zasu karra talafa mata wajen sake dawowa hayacinta da samun lafiyar zazabin"
Gaba daya abin wani iri ya zo masu duba da su basu karanta ba, bayan hakan take, Nero palu gaskiya ne, ba cutar iskokai bane cuta ce da zafin zazabi ke hadasa shi har ya haye ya taba kwakwaluwa, daga nan sai abinda Allah ya yi, wasun daga nan ake kwasarsu a kaisu gidan mai rukiya, kana ja da karfi kana kokowa da zazabin da kake fama da shi, malamin na daneka yana tofa maka abubuwan alkhairi yana so ya kwontar da iskokan, wani sa'in akan yi dace Allah ya yiwa abin tsawa, wani sa'in kuma dacen kan hadewa da ALK'ALAMIN kadararka wanda ya riga ya zanna tun kafin a haliceka cewa ta wannan dalili zaka dawo mahaukaci ko ka rasa rayuwarka, ko kuma ka ga baban tashin hankalin da baka taba tunanin akoyshi a cikin duniya ba......kadan daga aikin zafin zazabin nan, baban matsalarsa shine yawanci idan hankalinka ya dauke din nan dukkan wani abu na sirrin ratuwarka ke dagowa ya bayana da bakinka, alkhairi ne ko shari ne, ko menene da bakinka ne zaka fadi cewa ni da nake yin kaza da kaza? ......... Ku tambayi likitoci zasu baku bayani dala dala cewar tabas haka ne kuma hakan ke faruwa
Da wannan lamari aka taki rashin sa'a ya fado a kanta, a daidai wannan gaba, a irin wannan babar rana da mijinta ya wayi gari ya sauke dukkan wani nauyi da yake ji ya masa girma a saman kansa, sai ga matsala ta rashin lafiya ta fado, ta kuma zo da karfi, cikin kudurar ubangiji irin wannan,
Da karfi suka kakamata bayan an gyara mata hijabinta Allah ya taimaketa da masu rufe mata suturarta a kusa, suka samu suka daureta a jikin gadon da take kwonce, irin daurin da ba zata iya jima kanta rauni ko ta daki wanda ke gefenta ba, karfi ne tamkar na aljannu ke jan mutun, domin kana iya watsar da mutanen dake gefenka idan abin ya motsa, yana yi ne kuma yana kwociya
"Walahi walahi sai na kashe MUHYIDEEN da hannuna, sai na kashe shi , yadda yaron nan da uwarsa suka shigo min rayuwar gidana da mijina ina mulkina son raina aman suka zo suka fi karfina ya zamto mijina ya samu yaron nan a matsayin dan da yake fatan samu namiji aman bai samu ba, shine komai nawa da na y'ayana ya dawo hannunsa harta da shawarar abinda ya shafemu sai ya nema a wajensa uwarsa ta ciri ta kullu tabi bokaye ta shanye mini mijina sai yarda ta yi da shi ita karuwar algunguma mai........"
Da sauri ta karasa wajen ya dora hannunsa na hagu a saman bakinta ya damke da mugun karfin da ya sa ta hade da fatar tafin hannun nasa ta gala wani wawan cizon da ya ratsa dukan gaban jikinsa dan azabar zafi harma ya fara ji zufa na neman karyo masa, aman ya danne ya sake dora dayan ya danne bakin nata sosai yana rintse idannuwansa wani irin tsoron Allah na shiga dukkan sasan jikinsa da tsoron haduwa da shi a gobe kiyama da wani laifin, sannan ya sake yarda cewa ko me bawa yake yi a duniya dama Allah ke ara masa , kalilan ke samun dama irin wannan wace zasu bayana kafin su koma ga mahalicinsu, in ka yafe masu to, in baka yafe bama to, dama damarsu basu je a makance ba, watau sunna aikata aikinsu a boye da mugun nufinsu a zukatansu ba
Kallon da Dad ke yi masa, da Mahaifiyarsa ke yi masa, da kuma matar mahaifinsa ke yi masa, a gangaro kan sarakuwarsa dake tare da su, da sirikinsa dake gefe yana tofa mata adu'a a bayan an sake suturtata da hijabinta ya shigo shima yana tofa mata adu'a da nema mata sauki a wajen Allah, gaba daya suka zuba masa ido kowane da yannayi na firgicin furucin bakinta da kuma irin yadda ya damke bakin ya rike kam ya kuma hannata karasa furucinta, aman kuma a yadda take kokowar sai ua saketa zaka tabata da zarar ya saki bakin nan komai na iya faruwa ya saka shi sake gyara tsayuwarsa yana sake damkar bakin nata da hannunsa yana rintse idannuwansa ya ce" Kun san zafin ciwon nan babu abinda baya hadasawa, ciki harda dumumuwa kamar yadda likita ya sheda mana yanzu, dan haka nake so dan Allah ku fita ku dukanku waje har ta samu lafiya"
Dad kallonsa yake yi jikinsa na neman fara bari
Muryarsa na rawa ya ce" Mu fita waje ko ka saki bakinta?, MUHYIDEEN MUHAY, sake min bakinta now!"
MUHYIDEEN ya sada kansa yana girgiza kansa a sanyaye ya ce" Ka yi hakuri Dad, ba zan iya sakin bakinta ba"
Zai yi magana ya ringa jiyo salalamin mutanen dake zagaye da matar Father, sannan ya ringa jin hatsaniya irin sosai din nan, kai harma da furuci kamar haka"Hajia me kike yi haka kar ki cire suturarki mana hajia Innalilahi wa inna ilaihi raj'une menene wannan?"
Da sauri ya kalli wayar domin ba'a yanke kiran ba saima muryar Fathern da ya ji yana fadin" Menene wannan kamar kamun aljannu?, Ke? Ke? Hajia meye wannan kuma?"
Hakan ya sa da dan sauri ya sake kafe fuskarta da kallo yana datse kiran da tunanin abinda ya dace ya yi , ga barcinsa ba wai barinsa ya yi domin maganin yana saka barci sosai, ko yanzu da kyar ya iya mikewa sallar nan
Juyawa ya yi da nufin tafia, sai dai muryarta ta dakatar da shi a lokacin da ta hadasa masa da bugawar zuciya da ta furta" Ina zaka je kuma? Ya ja yaa tsaya yana rike da labulen kofar fitar sannan ya juyo yana kallonta hakan ya sa ta dan daburce kadan tana sosa gaban goshinta ta ce" Gani na yi dare ya yi fa, kuma baka cikin shirin fita aikin dare ko?"
Har ta dire maganar lebenta yake kallo da tuna moment dinsa na dazu da ita
A hankali ya saki kofar ya nufota, hakan ya saka gabanta faduwa, sai dai bata gudu ba ta dake tana kuma kallon fuskarsa
Yana zuwa ya tsaya yana kallon fuskarta ya ce" Kar na fita ne?"
Dan tsuru ta yi tana tambayar kanta tambayar tasa kamar wace take son gane yaren, sai kuma ta dan gumtse bakinta ta bude ta ce" Gani na yi baka ci abincin da kuma ruwan ba gayacen a rufe yadda na barshi"
Wajen abincin ya kai dubansa wanda sai yanzuma shi ya kula da shi har ga Allah, to in ba ita ba ai wata yinwar ta kori wata gaskiya
Bakinsa ya tabr ya juya yana fadin" Cinye abinki na koshi!"
Da ido ta raka shi har ya bacewa ganninta kafin ta sake sauke ajiyar zuciya tana shafa dogon karan hancinta hadi da lumshe idannuwanta ta nufi dakin barcinsa dan gyara masa bed dinsa da tatare gajeran wandonsa dan ta tabata ba zai taba shiryuwa da yarda gajeran wando ba a inda ya cire shi!
______________________________________
Da Mugun sauri ya idasa shiga wajen da likitar sojan ta kawo shi ta nuna masa cewar matar Dad na ciki da likitoci a tare da ita da su Dad din
Hankalinsa tashe ya shiga yana kallon yadda likitan nan ke magana su Dad gaba daya hankalinsu a kansa ga kuma gefe daya likitoci mata biyu da su Mama na ririke da ita tana ta fuzga tana dumumuwa mararsa dadin sauraro masu kamanceceniya da tonon silili da bugun kirji da fitsarar harshe da komai , sannan sai ihun a barta mutuwa zata yi ta yi gunduwa gunduwa take yi, abu shi ba na mai iska ba, shi ba na mai fitar rai ba, shi ba na mahaukaci ba, abu dai abun mamaki da tsoro , abun rikita zuciya tashi daya abun haukata bawa
Likitan ya sake fadin" CHIEF, abinda ke hadasa irin wannan crise din ba komai bane sai rashin lafiya fa muke kira da NERO PALU, shi Nero palu zan iya kwatanta maka shi a matsayin muguwar masasara, watau zazabin dake kama jiki ya cinye karfin jiki har ya haye ya nemi taba kwakwaluwa, tabas wannan zazabi yana da hadari sosai domin bama fatan rashin lafiya ta yiwa mutun yawa har ta kaishi da haka, wannam zazabin idan ya rike mutun mukan hada dukan kokarinmu bayan mun fara rike Allah, domin yana saka mutun ya yi har fiye da haka, ciki harda dabi'u irin na mahaukaci, tube suturar jiki, zage zage, kokowa, neman fita da gudu, sakin kashi a jiki, yakushi ne, dukka ne, magangannu ne masu muni sosai, domin akan shafe dukan wani hankaki na bawa ne a zuba masa rashin hankalin, daidaiku ke yin irin rashin lafiyar nan a cikin hali na summa, dayawansu kuwa idan suka tafi duniyar summan basa dawowa shikenan, wannan zazabi yana da hadarin gaske domin wasun idan suka dawo hayacinsu kwakwaluwarsu na tabuwa, wasu zasu jima sunna yin jinya, wasun kuma sai ka ga Allah ya taimaka sun tashi garas abinsu............ Ba maganar aljannu bane wannan kar ku ce zaku tafi da ita , ku yi hakuri mu daureta haka dan kar ta lahanta jikinta sannan ta lahanta na kusa da ita, in sha Allah zamu bi crise din nan sau da kafa har ta dakatar sai mu saka mata magungunnan fa zasu karra talafa mata wajen sake dawowa hayacinta da samun lafiyar zazabin"
Gaba daya abin wani iri ya zo masu duba da su basu karanta ba, bayan hakan take, Nero palu gaskiya ne, ba cutar iskokai bane cuta ce da zafin zazabi ke hadasa shi har ya haye ya taba kwakwaluwa, daga nan sai abinda Allah ya yi, wasun daga nan ake kwasarsu a kaisu gidan mai rukiya, kana ja da karfi kana kokowa da zazabin da kake fama da shi, malamin na daneka yana tofa maka abubuwan alkhairi yana so ya kwontar da iskokan, wani sa'in akan yi dace Allah ya yiwa abin tsawa, wani sa'in kuma dacen kan hadewa da ALK'ALAMIN kadararka wanda ya riga ya zanna tun kafin a haliceka cewa ta wannan dalili zaka dawo mahaukaci ko ka rasa rayuwarka, ko kuma ka ga baban tashin hankalin da baka taba tunanin akoyshi a cikin duniya ba......kadan daga aikin zafin zazabin nan, baban matsalarsa shine yawanci idan hankalinka ya dauke din nan dukkan wani abu na sirrin ratuwarka ke dagowa ya bayana da bakinka, alkhairi ne ko shari ne, ko menene da bakinka ne zaka fadi cewa ni da nake yin kaza da kaza? ......... Ku tambayi likitoci zasu baku bayani dala dala cewar tabas haka ne kuma hakan ke faruwa
Da wannan lamari aka taki rashin sa'a ya fado a kanta, a daidai wannan gaba, a irin wannan babar rana da mijinta ya wayi gari ya sauke dukkan wani nauyi da yake ji ya masa girma a saman kansa, sai ga matsala ta rashin lafiya ta fado, ta kuma zo da karfi, cikin kudurar ubangiji irin wannan,
Da karfi suka kakamata bayan an gyara mata hijabinta Allah ya taimaketa da masu rufe mata suturarta a kusa, suka samu suka daureta a jikin gadon da take kwonce, irin daurin da ba zata iya jima kanta rauni ko ta daki wanda ke gefenta ba, karfi ne tamkar na aljannu ke jan mutun, domin kana iya watsar da mutanen dake gefenka idan abin ya motsa, yana yi ne kuma yana kwociya
"Walahi walahi sai na kashe MUHYIDEEN da hannuna, sai na kashe shi , yadda yaron nan da uwarsa suka shigo min rayuwar gidana da mijina ina mulkina son raina aman suka zo suka fi karfina ya zamto mijina ya samu yaron nan a matsayin dan da yake fatan samu namiji aman bai samu ba, shine komai nawa da na y'ayana ya dawo hannunsa harta da shawarar abinda ya shafemu sai ya nema a wajensa uwarsa ta ciri ta kullu tabi bokaye ta shanye mini mijina sai yarda ta yi da shi ita karuwar algunguma mai........"
Da sauri ta karasa wajen ya dora hannunsa na hagu a saman bakinta ya damke da mugun karfin da ya sa ta hade da fatar tafin hannun nasa ta gala wani wawan cizon da ya ratsa dukan gaban jikinsa dan azabar zafi harma ya fara ji zufa na neman karyo masa, aman ya danne ya sake dora dayan ya danne bakin nata sosai yana rintse idannuwansa wani irin tsoron Allah na shiga dukkan sasan jikinsa da tsoron haduwa da shi a gobe kiyama da wani laifin, sannan ya sake yarda cewa ko me bawa yake yi a duniya dama Allah ke ara masa , kalilan ke samun dama irin wannan wace zasu bayana kafin su koma ga mahalicinsu, in ka yafe masu to, in baka yafe bama to, dama damarsu basu je a makance ba, watau sunna aikata aikinsu a boye da mugun nufinsu a zukatansu ba
Kallon da Dad ke yi masa, da Mahaifiyarsa ke yi masa, da kuma matar mahaifinsa ke yi masa, a gangaro kan sarakuwarsa dake tare da su, da sirikinsa dake gefe yana tofa mata adu'a a bayan an sake suturtata da hijabinta ya shigo shima yana tofa mata adu'a da nema mata sauki a wajen Allah, gaba daya suka zuba masa ido kowane da yannayi na firgicin furucin bakinta da kuma irin yadda ya damke bakin ya rike kam ya kuma hannata karasa furucinta, aman kuma a yadda take kokowar sai ua saketa zaka tabata da zarar ya saki bakin nan komai na iya faruwa ya saka shi sake gyara tsayuwarsa yana sake damkar bakin nata da hannunsa yana rintse idannuwansa ya ce" Kun san zafin ciwon nan babu abinda baya hadasawa, ciki harda dumumuwa kamar yadda likita ya sheda mana yanzu, dan haka nake so dan Allah ku fita ku dukanku waje har ta samu lafiya"
Dad kallonsa yake yi jikinsa na neman fara bari
Muryarsa na rawa ya ce" Mu fita waje ko ka saki bakinta?, MUHYIDEEN MUHAY, sake min bakinta now!"
MUHYIDEEN ya sada kansa yana girgiza kansa a sanyaye ya ce" Ka yi hakuri Dad, ba zan iya sakin bakinta ba"