Sashe 38
Alkalamin Kaddara ta Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Matar malan kam wajen baki ta koma hankali kwonce biki ya ci gaba da tafia tana mai basu dukan kulawar da ta dace tamkar yar uwarta ta jinni ake aurarwa, ita itace uwar gidan malan, ita sukai aure na budurwa da saurayi da malan, ita din yar gidan wani hamshakin mai kudi ne, sun hada kansu da kansu da Malan da soyaya hakan ya sa rashin haihuwarsa baya daga mata hankalin zama da shi sam, abinda ke damunta matarsa ce sai ko wadinnan mutanem dake kayar mata da gaba da irin tsoron da ake yawan bata a kansu ana fada mata cewar idan ta yi sake wani abu ya faru tsakanin yan matan nan da malan ta shiga uku ta lalace tana ji tana gani mijinta zai gagareta
Sai dai a yau, a irin abinda ya faru a yau
ta idasa zubar da dukan wani makamin neman fitina da yaki da take yi da yan matan nan
Ko a da ta san babu abinda sukai mata, matsalarsu daya ce na mijinta na matukar girmama al'amarinsu, sannan amaryarsa na karra rura wutar kiyayar hakan
Aman idan ta yiwa abin nan duban tsanaki wai ita meye ribarta a ciki? Ita din dake tirata tana sakata tsanarsu ita dinma ba barinta ta yi ba, sannan au dukansu sun rigaya sun sani ne idan har Malan ya yi niyar auren NAHIDT basu isa su hanna shi ba domin Malan ba sakaran namijin da zai tsaya mace ta haramta masa abinda Allah ne ya halata masa ba, ba zai wulakanta su ba, aman kuma ba zai yi faduwar tasan da har zasu hanna masa aure ba matsawar ba haramun bane, to fa zai aikata ne
A yau ta fara shayin lamarin yarinyar nan SHUWWAR
Da ake cewa hadasa ga mai rabo taki ce , to fa tabas yana kasancewa a lamuran yarinyar
A aure auren da take yi bata taba auren marar mutunci ba, sake saken da ake yi mata bata taba haduwa da wawan da ya yi tsaye kan sai ta maida masa dukiyar aurensa ba, kai idanma ba rufewar ido ta mutanen dake hadasa mata masifa ba sunna gani da zarar an saketan take samun wani na gani na fada ya aureta da daraja duda zagin da ake yi mata cewar karuwa ce kanwar karuwai ce , bazawara ce ,meye meye, sannan dukan mutanen anguwar nan sunna mamakin mazan dake sakinta kuma su dawo sunna nacinta gar sai Malan ya yi da gaske koda za'a shafa mata lafia domin akoy wanda sai da Malan ya hada shi da yan hizba aka yi masu tsakani kafin ya shafa mata lafia dan kuwa a ya sake tan ya kuma nace da kai kawo wajenta har sai da ran Malan ya kiya ya nuna me kuma yake so? Ai ba aure tsakaninsu tunda mahaifiyarsa saki uku cir ya saka ya yi mata, ya yi hakuri ya shafa mata lafia
Ga wannan auren irin yadda aka shirya shi, kiri kiri matar Malan amarya ta yi haka ne dan a fasa a cikin dumbin al'uma, sai gashi an yi daurin auren da gaba daya kasar ta dauka ba iya garin ba , an aura mata mutun mai daraja da ganninsa in dai ba a jarida bane to fa kai tsaye dan kana gadarare baka isa ba sai dai idan mugun laifi ka yi wannan fa zaku jone ne ku yi zumunci na dogon lokacin da sai ka yi daka sannin aikata laifi a duniya!
Wadinnan abubuwan da ta hada waje daya ya saka ta yo watsi da komai ta shiga neman kyautatawa mijinta ta yadda koda auren watan ya yi to fa darajarta ba zata yi kasa ba, sai daima ta yi sama
Malan kam yana gama yiwa Hamza bayanin a tashi a ci abinci sukai ido hudu da NAHIDT dake kada kafafuwanta
Idan ba gezau idannuwansa ke masa ba harararsa ne NAHIDT ta yi bayan bai san laifin da ya yi mata ba, abin haushin dayan kuma kanta a bude yake tana ta kade kaden kafa jar yanzun bara rufe gashin kanta ba
Kai ya girgiza ya ka wajen su Aba da suka mike su uku
Abincin ya nuna masu , nan Aba ya yi yar daria yana fadin" Allah ya karra maka lafia ai gida yana cen cike da jama'a, ana ta girke girke abin ba'a cewa komai, ga baki sunna ta cigiyata da Hamza, yanzun zamu tafi da Abansu da Sire, Shima Sire zai je ne wajen MUHYIDEEN din dan a daidaita komai da wajen da za'a saka amaryar kafin yama ta yi, sai dai ina mai son fada maku a kaita da wuri gudun shigar duhu ka san cen anguwar basa bari a sshiga ko a fita da zarar duhu ya shigo sai yasu yasu"
Malan ya fahimta ya kuma gode, a nan ya taka masu bayan sun gama yin magana da Gogonninsu da kuma Hamza a kan maganar NAHIDT da zarar an sada SHUWWA da Fauziya dakunnansu su san yadda zasu yi da ita ta yarda ta koma gidan Aban Hamzan ko kuma ta tare gidan Fauziya kafin Allah ya fitar mata da mijin aurenta itama ta yi aurenta ta yi tafiyarta gidanta, domin ba zasu barta ta sake yin rayuwar zaman kanta ita kadai a gida ba
_________________________________
"Ka bari ka sauka ka huta haka mana son?, A kadan ma kusa minti ashirin ina irga gudun da kake a saman keken nan , ni da kaina na gaji sai haki nake yi bale kai" CHIEF OF ARMY dake dan zagayen keken da MUHYIDEEN ke sama a dakin Gym dinsa yana ta tukawa ba ji ba gani zufa ta gama wanke masa jikinsa gashi bashi da riga sai wandon da tsayinsa bai fi gwuiwarsa ba na gine dake jikinsa ya takarkare sai kikitu yake da keken motsa jiki irin katuwar nan har ya kai ta fara kikau kikau dan kamar wanda yake son gigibeta daga wajen da aka ginata ana sakata
Bakinsa ya dan tabe gannin ko ya nuna irin ya san yana wajen nan bayan du idan ya zo wucewa ta gabansa sai ya kalle shi domin ba'a rufe ido idan ana irin haka juwa ke kwasar mutun ta maka da kas
Dan murmushi ya yi ya ce" Da ka ji kunya idan aka ji yau da ni kake fushi MUHAY"
yanzunma bai ce da shi A ba hakan ya saka shi tsayawa a gabansa yana kallonsa ya ce" Meye laifin a ciki?, MUHAY tausaya mata na yi yarinyar abin tausayi ce, kai baka taimako ne?, Ka ga kar ka ilata kanka domin an sanar mon tunda ka zo nan ka shige baka kuma fito ba, karka zarta abinda zuciyarka ke iya dauka ka ilata kanka dan an maka aure, idan tsoronta kake ji ka saketa na yafe maka, ka saketa kawai"
Ido ya zarro yana kallon Father dinsa
Tukin da yake yi ya dakatar yana dantse lebensa na kasa da karfi da kuma mamakin Father
Wai me babansa yake so da shi ne kuma? Ba ya daura masa ba? So yake yi Kuma sai ya kashe shi ko me? Ya sani sarai baya son hayaniyar nan dan girman Allah yake yi masa?
Father ya dan duba agogonsa ya sake kallonsa duba da ya tsaya da tukin keken ya ce" Yanzun ni damuwatama ka ga yadda zaka fuskanci matarka ta gida ka fada mata ka yi wani auren a nan tun yanzu ka mata kishiya, ka san mata fa da tsanar kishiya, akoysu kishi sosai, to dai ka fada min zaka yi hakuri ka zauna da ita ko sakinta zaka yi? Sai na koma da sannin abinda zan fadawa iyayenta , rayuwa ce na tabata Allah zai bata wani mai jin kai, mai tausayi, mai son talafawa maraya, mai iya rike maraya da zuciya daya , mai .............."
"Dad please " ya fada a kausashe yana kallon Father da kallon dake nuni da na fahimci inda ka nufa
Sauka ya yi daga saman keken yana daukan tawul dinsa ya karasa wajen kujerar da yake zama ya zauna tawul din a rataye a wuyansa ya jimke hannunsa guda ya rike da dayan hannun a tafinsa yana kallon Father da ya karaso ya zauna shima a saman kujerar yana kallonsa
Furucinsa na nuni da ransa a cinkushe ya ce" Why zaka nuna idan ka isa da ni , irin a tsorace kake da abinda ka yin nan bayan kai ubana ne?, A kan auren mahaukaciya zaka nemi yin kuka dan zan sauta? Father idan ka wankan mari a lokacin ka ce in na yarda na furta mata kalmar saki zaka tsaba min kana tunanin zan kauce maganarka ne? Kennan dai ni maraya ne kuma dan iska ne ta yadda wanda nake kallo a matsayin ubana zai ce min in har bai kai matsayin da yake tunani da ni ba shikenan na aikata????????"
Ya karashe yana mai sake dantse lebensa yana saka idannuwansa cikin na Father wanda jikinsa ya yi mugun sanyi da tarin kaunar MUHYIDEEN a cikin zuciyarsa
Shi ya san yaron yana da tauri aman kuma yanada mugun laushi a wajensu
A hankali ya rike hannunsa yana kallonsa ya ce" I'm sorry Son"
"I'm sorry Muhay, u see idanma akoy taimako to akoy wani ikon Allah a cikin hadin nan, MUHAY lokaci daya na ji yarinyar ta yi min, na ji ina so ta kasance a cikin ahalina, ...... MUHAY kai yarona ne, ina sonka tamkar d'an da na haifa da cikina, mahaifinka aminina ne da bani da na biyunsa, mahaifiyarka yar uwata ce sannan iyalina, "
Dan saurarawa ya yi stll hannayensu a cikin na junna ya ce" Kai ka san da ba haka na yi maka ba da ka aikata abinda zai sake shiga cikin tarihin rayuwarka, ka san da mahaifiyarka ta fara tunanin ko namiji ne abokin dake birgeka a mu'amalar intim?"
Sai dai a yau, a irin abinda ya faru a yau
ta idasa zubar da dukan wani makamin neman fitina da yaki da take yi da yan matan nan
Ko a da ta san babu abinda sukai mata, matsalarsu daya ce na mijinta na matukar girmama al'amarinsu, sannan amaryarsa na karra rura wutar kiyayar hakan
Aman idan ta yiwa abin nan duban tsanaki wai ita meye ribarta a ciki? Ita din dake tirata tana sakata tsanarsu ita dinma ba barinta ta yi ba, sannan au dukansu sun rigaya sun sani ne idan har Malan ya yi niyar auren NAHIDT basu isa su hanna shi ba domin Malan ba sakaran namijin da zai tsaya mace ta haramta masa abinda Allah ne ya halata masa ba, ba zai wulakanta su ba, aman kuma ba zai yi faduwar tasan da har zasu hanna masa aure ba matsawar ba haramun bane, to fa zai aikata ne
A yau ta fara shayin lamarin yarinyar nan SHUWWAR
Da ake cewa hadasa ga mai rabo taki ce , to fa tabas yana kasancewa a lamuran yarinyar
A aure auren da take yi bata taba auren marar mutunci ba, sake saken da ake yi mata bata taba haduwa da wawan da ya yi tsaye kan sai ta maida masa dukiyar aurensa ba, kai idanma ba rufewar ido ta mutanen dake hadasa mata masifa ba sunna gani da zarar an saketan take samun wani na gani na fada ya aureta da daraja duda zagin da ake yi mata cewar karuwa ce kanwar karuwai ce , bazawara ce ,meye meye, sannan dukan mutanen anguwar nan sunna mamakin mazan dake sakinta kuma su dawo sunna nacinta gar sai Malan ya yi da gaske koda za'a shafa mata lafia domin akoy wanda sai da Malan ya hada shi da yan hizba aka yi masu tsakani kafin ya shafa mata lafia dan kuwa a ya sake tan ya kuma nace da kai kawo wajenta har sai da ran Malan ya kiya ya nuna me kuma yake so? Ai ba aure tsakaninsu tunda mahaifiyarsa saki uku cir ya saka ya yi mata, ya yi hakuri ya shafa mata lafia
Ga wannan auren irin yadda aka shirya shi, kiri kiri matar Malan amarya ta yi haka ne dan a fasa a cikin dumbin al'uma, sai gashi an yi daurin auren da gaba daya kasar ta dauka ba iya garin ba , an aura mata mutun mai daraja da ganninsa in dai ba a jarida bane to fa kai tsaye dan kana gadarare baka isa ba sai dai idan mugun laifi ka yi wannan fa zaku jone ne ku yi zumunci na dogon lokacin da sai ka yi daka sannin aikata laifi a duniya!
Wadinnan abubuwan da ta hada waje daya ya saka ta yo watsi da komai ta shiga neman kyautatawa mijinta ta yadda koda auren watan ya yi to fa darajarta ba zata yi kasa ba, sai daima ta yi sama
Malan kam yana gama yiwa Hamza bayanin a tashi a ci abinci sukai ido hudu da NAHIDT dake kada kafafuwanta
Idan ba gezau idannuwansa ke masa ba harararsa ne NAHIDT ta yi bayan bai san laifin da ya yi mata ba, abin haushin dayan kuma kanta a bude yake tana ta kade kaden kafa jar yanzun bara rufe gashin kanta ba
Kai ya girgiza ya ka wajen su Aba da suka mike su uku
Abincin ya nuna masu , nan Aba ya yi yar daria yana fadin" Allah ya karra maka lafia ai gida yana cen cike da jama'a, ana ta girke girke abin ba'a cewa komai, ga baki sunna ta cigiyata da Hamza, yanzun zamu tafi da Abansu da Sire, Shima Sire zai je ne wajen MUHYIDEEN din dan a daidaita komai da wajen da za'a saka amaryar kafin yama ta yi, sai dai ina mai son fada maku a kaita da wuri gudun shigar duhu ka san cen anguwar basa bari a sshiga ko a fita da zarar duhu ya shigo sai yasu yasu"
Malan ya fahimta ya kuma gode, a nan ya taka masu bayan sun gama yin magana da Gogonninsu da kuma Hamza a kan maganar NAHIDT da zarar an sada SHUWWA da Fauziya dakunnansu su san yadda zasu yi da ita ta yarda ta koma gidan Aban Hamzan ko kuma ta tare gidan Fauziya kafin Allah ya fitar mata da mijin aurenta itama ta yi aurenta ta yi tafiyarta gidanta, domin ba zasu barta ta sake yin rayuwar zaman kanta ita kadai a gida ba
_________________________________
"Ka bari ka sauka ka huta haka mana son?, A kadan ma kusa minti ashirin ina irga gudun da kake a saman keken nan , ni da kaina na gaji sai haki nake yi bale kai" CHIEF OF ARMY dake dan zagayen keken da MUHYIDEEN ke sama a dakin Gym dinsa yana ta tukawa ba ji ba gani zufa ta gama wanke masa jikinsa gashi bashi da riga sai wandon da tsayinsa bai fi gwuiwarsa ba na gine dake jikinsa ya takarkare sai kikitu yake da keken motsa jiki irin katuwar nan har ya kai ta fara kikau kikau dan kamar wanda yake son gigibeta daga wajen da aka ginata ana sakata
Bakinsa ya dan tabe gannin ko ya nuna irin ya san yana wajen nan bayan du idan ya zo wucewa ta gabansa sai ya kalle shi domin ba'a rufe ido idan ana irin haka juwa ke kwasar mutun ta maka da kas
Dan murmushi ya yi ya ce" Da ka ji kunya idan aka ji yau da ni kake fushi MUHAY"
yanzunma bai ce da shi A ba hakan ya saka shi tsayawa a gabansa yana kallonsa ya ce" Meye laifin a ciki?, MUHAY tausaya mata na yi yarinyar abin tausayi ce, kai baka taimako ne?, Ka ga kar ka ilata kanka domin an sanar mon tunda ka zo nan ka shige baka kuma fito ba, karka zarta abinda zuciyarka ke iya dauka ka ilata kanka dan an maka aure, idan tsoronta kake ji ka saketa na yafe maka, ka saketa kawai"
Ido ya zarro yana kallon Father dinsa
Tukin da yake yi ya dakatar yana dantse lebensa na kasa da karfi da kuma mamakin Father
Wai me babansa yake so da shi ne kuma? Ba ya daura masa ba? So yake yi Kuma sai ya kashe shi ko me? Ya sani sarai baya son hayaniyar nan dan girman Allah yake yi masa?
Father ya dan duba agogonsa ya sake kallonsa duba da ya tsaya da tukin keken ya ce" Yanzun ni damuwatama ka ga yadda zaka fuskanci matarka ta gida ka fada mata ka yi wani auren a nan tun yanzu ka mata kishiya, ka san mata fa da tsanar kishiya, akoysu kishi sosai, to dai ka fada min zaka yi hakuri ka zauna da ita ko sakinta zaka yi? Sai na koma da sannin abinda zan fadawa iyayenta , rayuwa ce na tabata Allah zai bata wani mai jin kai, mai tausayi, mai son talafawa maraya, mai iya rike maraya da zuciya daya , mai .............."
"Dad please " ya fada a kausashe yana kallon Father da kallon dake nuni da na fahimci inda ka nufa
Sauka ya yi daga saman keken yana daukan tawul dinsa ya karasa wajen kujerar da yake zama ya zauna tawul din a rataye a wuyansa ya jimke hannunsa guda ya rike da dayan hannun a tafinsa yana kallon Father da ya karaso ya zauna shima a saman kujerar yana kallonsa
Furucinsa na nuni da ransa a cinkushe ya ce" Why zaka nuna idan ka isa da ni , irin a tsorace kake da abinda ka yin nan bayan kai ubana ne?, A kan auren mahaukaciya zaka nemi yin kuka dan zan sauta? Father idan ka wankan mari a lokacin ka ce in na yarda na furta mata kalmar saki zaka tsaba min kana tunanin zan kauce maganarka ne? Kennan dai ni maraya ne kuma dan iska ne ta yadda wanda nake kallo a matsayin ubana zai ce min in har bai kai matsayin da yake tunani da ni ba shikenan na aikata????????"
Ya karashe yana mai sake dantse lebensa yana saka idannuwansa cikin na Father wanda jikinsa ya yi mugun sanyi da tarin kaunar MUHYIDEEN a cikin zuciyarsa
Shi ya san yaron yana da tauri aman kuma yanada mugun laushi a wajensu
A hankali ya rike hannunsa yana kallonsa ya ce" I'm sorry Son"
"I'm sorry Muhay, u see idanma akoy taimako to akoy wani ikon Allah a cikin hadin nan, MUHAY lokaci daya na ji yarinyar ta yi min, na ji ina so ta kasance a cikin ahalina, ...... MUHAY kai yarona ne, ina sonka tamkar d'an da na haifa da cikina, mahaifinka aminina ne da bani da na biyunsa, mahaifiyarka yar uwata ce sannan iyalina, "
Dan saurarawa ya yi stll hannayensu a cikin na junna ya ce" Kai ka san da ba haka na yi maka ba da ka aikata abinda zai sake shiga cikin tarihin rayuwarka, ka san da mahaifiyarka ta fara tunanin ko namiji ne abokin dake birgeka a mu'amalar intim?"