Sashe 121
Alkalamin Kaddara ta Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wata muryar mai iso da shigowar sarakin ta saka shi sake maida dubansa kyam a kan wanda zai shigo
A tarihin masarautun kasar nan, masarautar gidansu ce kadai aka yiwa zamanin iso da mai shigowa, a zamanin sarautar dan uwansa ya goge wannan, bayan ya rasu shi ya dawo da ita aman kuma ta wata siga daban, sai ga tsohuwar sanarwar tana shiga dodon kunnensa, wanda hakan ya saka shi sake neman zurmuwa a wani tunani daban
Shin wani karamin kwaron sarki ne ya dauki wannan sanarwa ya maida ita kasarsa? Da kuwa ya ga ikon Allah domin idan takamar kasar cewa an dade da juya babin yaki da kuwa sun tsogalo rigima da aljani, dan kuwa shi da kansa zai dauki takobi ya sare kan tsageran sarkin da ya dauki busa da kuma kida irin na masarautarsu!
Hanya aka buda, sandarsa ta fara bayana a wajen a hannunsa, sanda mai ruwan ta mahaifinsa sak, wace take da ado irin ta mahaifinsa
Mutane da yawa wa'inda suka rayu da mahaifinsa suka kuma san adon rawani irin na mahaifinsa ne suka mike hankali tashe sunna zuba idannuwansu a saman mutumen da ya bayana a lokaci daya da tsayuwa da mayar da kai gefe tak irin na sarkin garinsu marigayi Allah ya jikan rai
Da kakarfar muryar wannan tsoho jikinsa na daukan tsuma ya bude bakinsa yana fadin" GYARA KIMTSI MUTANEN GARINA, GYARA KIMTSI GA NADIN ALLAH, GYARA KIMTSI BANDA HAYANIYA, GYARA KIMTSI GA JINNI NA SARAUTA, SARKIN GARINA MAI TAUSAYINMU, MAI KAUNARMU, KAWUNNANKU A KASA DOMIN MAGABACINMU NE TAKAWARKA LAFIYA SARKI DAN SARKI JIKAN SARKI *UMAR ABDULAHI BINE MUTALAB*, Ga da a wajen IBRAHIMA DA KHAMISSSSSS, ........"
Watau tunda aka ambaci sunnan nan sarki Khamisss ya daina fahimtar abinda yake faruwa, haka kuma idannuwansa suka dawo kallon gabansa tarrrr ya ringa fitar da numfashi ta bakinsa, har sai da UMAR ABDULAHI BINE MUTALAB ya zauna a kujerar dake hade da tasa, sannan CHIEF OF ARMY MUHYIDEEN MUHAY ya zauna a dayan barin da a da wani ne a sama aman a yanzu ya tashi
Yana zama ya sauke ajiyar zuciya hadi da sake ambaton sunnan Allah da fatan Allah ya bashi dama kar ya fashe da kuka a zaunen nan da yake a gaban mutumen nan da ya wulakantar da rayuwarsa, yana fata yadda ya ga dare ya ga rana to ya jure wannan moment din
Dogaren da suka zube a gabansa, datijai wa'inda suka yo zamani da mahaifinsa ne yake kallo, da kallo irin na soyaya mai tarra kwala a cikin idannuwa
Sai kuma a hankali ya daga masu kai dake nuni da ya amsa gaisuwarsu baki daya
A zabure sarki KHAMIS ya juyo a lokacin da baban shehin limamin Yah sheik ya amsa wannan gayata da dumbin kauna bayan an masa bayani a boye ya kuma zo da dukan kwarin gwuiwarsa duda matarsa bata jima da haihuwa ba ya zamto shine wanda zai daura auren a wannan lokaci ya yi gyaran murya a nutse ya shiga gabatar da dukkan abinda ya dace , ga kuma mai amsa kuwa a gefe yana fadin komai a cikin amsa kuwar ta yadda yan cikon gida ke ji da kunnayensu haka kuma yan nesa da nesa
Cikin kankanin lokaci aka daura auren MUHAMMAD da NAHIDT UMAR ABDULAHI BINE MUTALAB bisa sadaki kwakwara mai motsi wanda ana gama sanarwar daurin auren mai amsa kuwa ya sanar da babar murya sannan ya sake buda muryarsa ya sanar da sako kamar haka" SUGABAN Sojojin kasar nan watau MUHYIDEEN MUHAY yana mai sanar da dukan wani farar hula cewa ya ja ya koma , yana godiya da halartar daurin auren da aka yi yana fatan alkhairi"
Ana fadin haka sojojin suka shiga bada kokari ta wajen janye mutanen da suka tabata babu su a cikin hurumin maganar cikin mutuntatawa ba cikin wulakantarwa ba har suka idasa janye su gaba daya sannan suka sake zagaye wajen da iya wa'inda abin ya shafa
Ajiyar zuciya Muhammad ya yi yana sake sadda kansa, haka dukkan yawancin wasu manya manyan wajen kawunnansu a kasa suke a sade ciko harda shi din da kansa sarki Khamissss
Sosai ya iya controling din kansa a sanyaye sosai ya furta"Zaka iya hakuri da goyar dake son kaika wuta ka adana tsufanka ka rufawa kanka asiri ka yi aiki na ilimi ka mika kayan aron dake hannunka kuwa Papah ba tare da an wulakantar da junna da tashin tashina ba? Domin shi rufin asiri dadi gareshi koda a wajen mai laifi ne, ina fata alfarmar rufa maka nima Allah ya rufa min"
Kamar yadda ya dauki maganar haka shima ya dago da dogon kallo jikinsa na bari
Zufar dake tsago a jikinsa mai tarin yawa ce, hankalinsa a tashe ya furta" Ta yaya? Ta yaya ka rayu bayan irin ukubar da ka gani? Ta yaya ka warke daga cutar haukan da kake ciki?"
Idannuwansa ya saka cikin nasa tarrrrr a kausashe ya ce" Ta hanyar wanda ya busa maka numfashi, Khamiss Mutalab ta yaya ka kwaci hakin da ba naka ba, ka tura wajen da baka da masaniyar fadawar kafafuwa, ka bi da bita da kulli kuma ka ki kyautatawa kasarka? Ka yi kokarin yin komai da murmushi domin kasarka na kallonka, ana haskaka ne!"
A firgice ya juyo wajen da masu dauka suke, bayanan da suke ne ya sake saka zuciyarsa neman tsayawa
Juyowa ya sake yi a birkice ya ce" Kana nufin na baka kujerar da a kanta na aikata shirka? Kujerar da na fitar da kai sannan na haukata dan uwana? Kujerar da nake mulka da dukkan karfina? Kana so ka ce ni zan baka kujerar nan? Mema zai sa na baka ne?"
Ajiyar zuciya ya sake saukewa yana fadin" Bama so ka tona mu sai ka tona mu?, Khamiss a yanzu ace a barka a saman kujerar nan da shekara goma zai zamto ne idan ranka bai fita daga gangar jikinka ba to fa tsufa irin sosai din nan zai kama ka wanda zaka dawo baka fahimtar komai dake gabanka, haka ka zaba ne? Kuma ka san ko da karfin Allah zan iya amsa, bale talakawana suka ce ka sauka ka bani abinda yake nawa!"
Zai kuma yin wata maganar a gigice Muhyideen ya karkato kadan shima ya make murya sosai, sai dai ina, muryar tasa ba zata fita a hankali sosai din ba ya dan dube su ya dan yi murmushi ya ce" Allah ya karra lafiya a gaskiya idan aka amshi kujerar nan ta laluma ni aka cuta, inaga fa har rantsuwa na yi kan sai na yi wasan kura da azalumin da ya aikata haka dan na zubar da sheda ta kasance izina ga mai son aikata irin haka, ka ga fa......"
Sai kuwa ya mike ya kwabe babar rigar dake sama hadi da hular dake saman kansa ya zubar, cikin lamari na ikon Allah sai ya kwabe dayar rigarma wace daga ita sai farar ciki kadai ta rage ta cen ciki mai siraran hannaye irin rigar nan dai ta maza sai ko wandon shadar da yake sanye da shi, hakan ya bayanar da bindigar dake jikinsa da manyan damatsunnansa
Hankali kwonce ya juya wajen su Aban Shuwwa da ya yu mutuwar zaune ya wangale baki da hanci yana kallonsa ya karasa a nutse ya dan yi murmushi ya ce" Siriki dan bani Alkur'anin mana"
Ido ya kyafta da sauri, sai kuma ya dan zabura ya bashi alkur'anin da aka zo da shi dan hakan
Ya amsa da hannu bibiyu ya koma gaban sarakan da dukkan wasu masu kallo
Wajen camerar ya juyo ya ce" Ku kashe daukan zaku dauki wajen nadi"
A yadda ya yi maganar a dole suka kashe sunna kyamewa da takaicin rashin daukarwa al'uma wannan rahoto mai dumi dumi
Da kyau ya ajiye alkur'anin saman kujerar ya tsaya a gabansu sosai ya bude muryarsa ya ce" Allah taimaki Baba KHAMIS, inaga ya dace mu yi mu gama dan walahi kade kade nake ji a cikin gidan cen da busa kar aje harda kartin makadan nan aka shiga kuma ita kuma tana wajen, da wahala ta kasa yabawa, Gaskiya ka san kun san abinda ka aikata shi yasa aka sameka a nan, to ba yadda ban yi da su ba kan a yaku masarautar taka a tube maka rawanin ta balbalin balaki suka ce aa, ai kawai a barka da halinka, an cuce ni sosai , sai dai bani da yadda zan yi gaskiya, aman inaga an fara gabatar min da bidi'a, tunda dai sai kwana kwana kuke yi gashi shi kuma d'anka ne ko yayane zai sasauta, ni kuma HUKUMA ne, akoy hakkin ma bima al'uma hakkinta, gashi kuma aban namuma al'umar ne, kawai ka dan fahimta a gama tunda ga takardar saka hannun shugaban kasa ya tuge ka, kun yarda sarauta ta shiga siyasa har ya gama aiki fa, kawai zoben nan ne zaka ciro ka bamu a saukake jirginka na jiranka ka koma ka hada dukkan abinda ka ga zai gyaraka dan bama ja baya da balaki ko na waye da izinin Allah, idan ba haka ba kuwa gaskiya zan Shure komai na fara dankara maka Alkur'ani mai tsarki watau ka rantse ta yadda zaka kuturce, sannan na gabatar da hukunci a kanka a kan laifinka, dan shara'a tana hawa kan tsohon da baya iya motsawama bale kai da karfin kaunar mulki ya sa har yanzu ka iya irgen kudi!"
Da karfi ya idasa maganar wadda da yawa sai da suka rintse idannuwansu ciki harda sarki Khamisss sannan ya sake fadin" Alkalan na wajen, sun auna sun kuma ce kai nawa ne, Baba ka fa aikata kidan sake tashi yake!"
A tarihin masarautun kasar nan, masarautar gidansu ce kadai aka yiwa zamanin iso da mai shigowa, a zamanin sarautar dan uwansa ya goge wannan, bayan ya rasu shi ya dawo da ita aman kuma ta wata siga daban, sai ga tsohuwar sanarwar tana shiga dodon kunnensa, wanda hakan ya saka shi sake neman zurmuwa a wani tunani daban
Shin wani karamin kwaron sarki ne ya dauki wannan sanarwa ya maida ita kasarsa? Da kuwa ya ga ikon Allah domin idan takamar kasar cewa an dade da juya babin yaki da kuwa sun tsogalo rigima da aljani, dan kuwa shi da kansa zai dauki takobi ya sare kan tsageran sarkin da ya dauki busa da kuma kida irin na masarautarsu!
Hanya aka buda, sandarsa ta fara bayana a wajen a hannunsa, sanda mai ruwan ta mahaifinsa sak, wace take da ado irin ta mahaifinsa
Mutane da yawa wa'inda suka rayu da mahaifinsa suka kuma san adon rawani irin na mahaifinsa ne suka mike hankali tashe sunna zuba idannuwansu a saman mutumen da ya bayana a lokaci daya da tsayuwa da mayar da kai gefe tak irin na sarkin garinsu marigayi Allah ya jikan rai
Da kakarfar muryar wannan tsoho jikinsa na daukan tsuma ya bude bakinsa yana fadin" GYARA KIMTSI MUTANEN GARINA, GYARA KIMTSI GA NADIN ALLAH, GYARA KIMTSI BANDA HAYANIYA, GYARA KIMTSI GA JINNI NA SARAUTA, SARKIN GARINA MAI TAUSAYINMU, MAI KAUNARMU, KAWUNNANKU A KASA DOMIN MAGABACINMU NE TAKAWARKA LAFIYA SARKI DAN SARKI JIKAN SARKI *UMAR ABDULAHI BINE MUTALAB*, Ga da a wajen IBRAHIMA DA KHAMISSSSSS, ........"
Watau tunda aka ambaci sunnan nan sarki Khamisss ya daina fahimtar abinda yake faruwa, haka kuma idannuwansa suka dawo kallon gabansa tarrrr ya ringa fitar da numfashi ta bakinsa, har sai da UMAR ABDULAHI BINE MUTALAB ya zauna a kujerar dake hade da tasa, sannan CHIEF OF ARMY MUHYIDEEN MUHAY ya zauna a dayan barin da a da wani ne a sama aman a yanzu ya tashi
Yana zama ya sauke ajiyar zuciya hadi da sake ambaton sunnan Allah da fatan Allah ya bashi dama kar ya fashe da kuka a zaunen nan da yake a gaban mutumen nan da ya wulakantar da rayuwarsa, yana fata yadda ya ga dare ya ga rana to ya jure wannan moment din
Dogaren da suka zube a gabansa, datijai wa'inda suka yo zamani da mahaifinsa ne yake kallo, da kallo irin na soyaya mai tarra kwala a cikin idannuwa
Sai kuma a hankali ya daga masu kai dake nuni da ya amsa gaisuwarsu baki daya
A zabure sarki KHAMIS ya juyo a lokacin da baban shehin limamin Yah sheik ya amsa wannan gayata da dumbin kauna bayan an masa bayani a boye ya kuma zo da dukan kwarin gwuiwarsa duda matarsa bata jima da haihuwa ba ya zamto shine wanda zai daura auren a wannan lokaci ya yi gyaran murya a nutse ya shiga gabatar da dukkan abinda ya dace , ga kuma mai amsa kuwa a gefe yana fadin komai a cikin amsa kuwar ta yadda yan cikon gida ke ji da kunnayensu haka kuma yan nesa da nesa
Cikin kankanin lokaci aka daura auren MUHAMMAD da NAHIDT UMAR ABDULAHI BINE MUTALAB bisa sadaki kwakwara mai motsi wanda ana gama sanarwar daurin auren mai amsa kuwa ya sanar da babar murya sannan ya sake buda muryarsa ya sanar da sako kamar haka" SUGABAN Sojojin kasar nan watau MUHYIDEEN MUHAY yana mai sanar da dukan wani farar hula cewa ya ja ya koma , yana godiya da halartar daurin auren da aka yi yana fatan alkhairi"
Ana fadin haka sojojin suka shiga bada kokari ta wajen janye mutanen da suka tabata babu su a cikin hurumin maganar cikin mutuntatawa ba cikin wulakantarwa ba har suka idasa janye su gaba daya sannan suka sake zagaye wajen da iya wa'inda abin ya shafa
Ajiyar zuciya Muhammad ya yi yana sake sadda kansa, haka dukkan yawancin wasu manya manyan wajen kawunnansu a kasa suke a sade ciko harda shi din da kansa sarki Khamissss
Sosai ya iya controling din kansa a sanyaye sosai ya furta"Zaka iya hakuri da goyar dake son kaika wuta ka adana tsufanka ka rufawa kanka asiri ka yi aiki na ilimi ka mika kayan aron dake hannunka kuwa Papah ba tare da an wulakantar da junna da tashin tashina ba? Domin shi rufin asiri dadi gareshi koda a wajen mai laifi ne, ina fata alfarmar rufa maka nima Allah ya rufa min"
Kamar yadda ya dauki maganar haka shima ya dago da dogon kallo jikinsa na bari
Zufar dake tsago a jikinsa mai tarin yawa ce, hankalinsa a tashe ya furta" Ta yaya? Ta yaya ka rayu bayan irin ukubar da ka gani? Ta yaya ka warke daga cutar haukan da kake ciki?"
Idannuwansa ya saka cikin nasa tarrrrr a kausashe ya ce" Ta hanyar wanda ya busa maka numfashi, Khamiss Mutalab ta yaya ka kwaci hakin da ba naka ba, ka tura wajen da baka da masaniyar fadawar kafafuwa, ka bi da bita da kulli kuma ka ki kyautatawa kasarka? Ka yi kokarin yin komai da murmushi domin kasarka na kallonka, ana haskaka ne!"
A firgice ya juyo wajen da masu dauka suke, bayanan da suke ne ya sake saka zuciyarsa neman tsayawa
Juyowa ya sake yi a birkice ya ce" Kana nufin na baka kujerar da a kanta na aikata shirka? Kujerar da na fitar da kai sannan na haukata dan uwana? Kujerar da nake mulka da dukkan karfina? Kana so ka ce ni zan baka kujerar nan? Mema zai sa na baka ne?"
Ajiyar zuciya ya sake saukewa yana fadin" Bama so ka tona mu sai ka tona mu?, Khamiss a yanzu ace a barka a saman kujerar nan da shekara goma zai zamto ne idan ranka bai fita daga gangar jikinka ba to fa tsufa irin sosai din nan zai kama ka wanda zaka dawo baka fahimtar komai dake gabanka, haka ka zaba ne? Kuma ka san ko da karfin Allah zan iya amsa, bale talakawana suka ce ka sauka ka bani abinda yake nawa!"
Zai kuma yin wata maganar a gigice Muhyideen ya karkato kadan shima ya make murya sosai, sai dai ina, muryar tasa ba zata fita a hankali sosai din ba ya dan dube su ya dan yi murmushi ya ce" Allah ya karra lafiya a gaskiya idan aka amshi kujerar nan ta laluma ni aka cuta, inaga fa har rantsuwa na yi kan sai na yi wasan kura da azalumin da ya aikata haka dan na zubar da sheda ta kasance izina ga mai son aikata irin haka, ka ga fa......"
Sai kuwa ya mike ya kwabe babar rigar dake sama hadi da hular dake saman kansa ya zubar, cikin lamari na ikon Allah sai ya kwabe dayar rigarma wace daga ita sai farar ciki kadai ta rage ta cen ciki mai siraran hannaye irin rigar nan dai ta maza sai ko wandon shadar da yake sanye da shi, hakan ya bayanar da bindigar dake jikinsa da manyan damatsunnansa
Hankali kwonce ya juya wajen su Aban Shuwwa da ya yu mutuwar zaune ya wangale baki da hanci yana kallonsa ya karasa a nutse ya dan yi murmushi ya ce" Siriki dan bani Alkur'anin mana"
Ido ya kyafta da sauri, sai kuma ya dan zabura ya bashi alkur'anin da aka zo da shi dan hakan
Ya amsa da hannu bibiyu ya koma gaban sarakan da dukkan wasu masu kallo
Wajen camerar ya juyo ya ce" Ku kashe daukan zaku dauki wajen nadi"
A yadda ya yi maganar a dole suka kashe sunna kyamewa da takaicin rashin daukarwa al'uma wannan rahoto mai dumi dumi
Da kyau ya ajiye alkur'anin saman kujerar ya tsaya a gabansu sosai ya bude muryarsa ya ce" Allah taimaki Baba KHAMIS, inaga ya dace mu yi mu gama dan walahi kade kade nake ji a cikin gidan cen da busa kar aje harda kartin makadan nan aka shiga kuma ita kuma tana wajen, da wahala ta kasa yabawa, Gaskiya ka san kun san abinda ka aikata shi yasa aka sameka a nan, to ba yadda ban yi da su ba kan a yaku masarautar taka a tube maka rawanin ta balbalin balaki suka ce aa, ai kawai a barka da halinka, an cuce ni sosai , sai dai bani da yadda zan yi gaskiya, aman inaga an fara gabatar min da bidi'a, tunda dai sai kwana kwana kuke yi gashi shi kuma d'anka ne ko yayane zai sasauta, ni kuma HUKUMA ne, akoy hakkin ma bima al'uma hakkinta, gashi kuma aban namuma al'umar ne, kawai ka dan fahimta a gama tunda ga takardar saka hannun shugaban kasa ya tuge ka, kun yarda sarauta ta shiga siyasa har ya gama aiki fa, kawai zoben nan ne zaka ciro ka bamu a saukake jirginka na jiranka ka koma ka hada dukkan abinda ka ga zai gyaraka dan bama ja baya da balaki ko na waye da izinin Allah, idan ba haka ba kuwa gaskiya zan Shure komai na fara dankara maka Alkur'ani mai tsarki watau ka rantse ta yadda zaka kuturce, sannan na gabatar da hukunci a kanka a kan laifinka, dan shara'a tana hawa kan tsohon da baya iya motsawama bale kai da karfin kaunar mulki ya sa har yanzu ka iya irgen kudi!"
Da karfi ya idasa maganar wadda da yawa sai da suka rintse idannuwansu ciki harda sarki Khamisss sannan ya sake fadin" Alkalan na wajen, sun auna sun kuma ce kai nawa ne, Baba ka fa aikata kidan sake tashi yake!"