Sashe 92
Alkalamin Kaddara ta Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Mama ta gyada kanta tana mai yi masa adu'a sannan sukai salama ta sake maida hankalinta kan wajen labulayen da aka cenza da komai tana mai sake kula da tsaftar wajen da komai, sannan tana cike da farin cikin gannin yan matan murna ta ki ta boye kanta a saman fuskokinsu, ci gaba ta yi da taya su aikin itama cike da kula tana mai raya lalle lalle zata shirya tarewar Shuwwa ne, domin itama tana so yaron nata ya tare da iyalinsa wannan karron a ga yaya tafiyar zata tafi ne?
A nutse suka gama gyara ko'ina, sannan suka rufo suka koma bangaren Maman suka shiga girke girke, dama yau girkinta ne, hakan ya sa suka yi zama daya, da kansu sai masu aiki dake dan dauko abin daukowa su mayar da na maidawa suka yi tsararun girke girke, ciki harda favorite girkin da mahaifinsu ya fi so suka gabatarwa da Mama ta kuwa basu hadin kai suka girka masa , watau cus cus da boulette din naman kaza, sai jus na kwakwa mai sanyi , kai abincin saima da ya shiga cikin kwanoni na alfarma ya karra daukan kalla, ba'a cewa komai domin tabas ana iya ciza yatsa wajen dandanonsa
Da yama , wajen karfe shida Dad ya sanarwa Mama cewar sun kusa karasowa ya same su a bangaren bakin gaba dayansu, ashe har sauran matansa ya fada masu cewar su hadu dan tarbar bakim da yake tafe da su
Kasancewar babu wanda ya san wasu bakin ne? Domin basu san cewa wai mararsa lafiyan nan ne za'a tarba haka ba, ya saka su zuwa din
Sai dai sun yi mamakin gannin Matar MUHAY cikin shiga ta bak'ar abaya har kasa, ta yane kanta da mayafin abayar, sannan da bak'ar safa a kafarta, hakama yar uwarta irin shigarta ce a jikinta sak, hakan sai ya fitar da kamaninsu tamkar wasu y'ayan larabawa, kalar fatarsu ta sake amsar shigarsu, nanadewar da suka yiwa dan kwalinsu kuwa ya amshi yannayin fuskarsu, kowace da kamar wanda take yi a cikin iyayensu, sai dai jini da baya karya ne ya sa tashi dayama kana iya tunanin lalle kamarsu daya, sai in ka zauna da su ne zaka gane jinni ne mai karfi a tsakaninsu
Tabas sauran sun yi mamakin ganninsu haka dare dare a falon da ya dauki kaya ya yi wani irin kyau, ga kanshi ga sanyin AC na tashi ta ko'ina, ga lalausan capet ga tsaftar waje, sai dai babu wace ta fitar da mamakinta, aman kuma sun baza ido su ga abinda zai faru, domin shi ai kishi kumalon mata ne, kowace na da kalar nata kishin, bale uwar gidansa da ta gama daukarwa niyar in dai mijin nasu wasu bakin alfarma ne da shi bai tashi saukarsu ba sai yau ranar girkin uwar dan gwal walahi za'a yita kuwa a gidan nan, ita fa ta fa kai makura fa!, Walahil azim ta kai makura
Sunna nan zaune , ba wata hira suke yi ba, TV ce aka kunna aka rage amonta sosai a tashar da basu da aiki sai karatun alkur'ani, shi yake tashi a tausashe hakan ya sa kowace ke abinda ta ga ya fi mata zaman shirun, wata na waya ne, wata na karra harare harare ne, wata na shaaninta hankali kwonce ne, yan matan biyu kuwa kowace a cikin zulumi da kallon hanya suke, zuciyarsu na cike da tunanin yaya jikin iyayen nasu ne?
Wani soja ne guda ya bude kofar ya shigo bayan ya yi salama sannan ya sake bude kofar da kyau
Gaba dayansu ne suka mimike sunna kallon hanyar shigowar
Father ne ya fara bayana kadan , kafin ya sake rike mutumen dake bayansa da kyau dan ya taimaka masa ya shigo da kyau
A lokacin da ya bayana babu wanda bai tsura masa ido a cikinsu ba
Tabas rama ta samu wajen zama a jikin magaifinsu, sai dai abin mamaki annuri ya fara samun wajen zama a yanzu a tare da shi, haka kuma ramar ba kamar wace take hade da muguwar dati da duguzar gashin fuska da na kai din nan bace, a yanzun harda hiraminsa da ya dora a saman kansa, ga manyan idannuwansa farare kal yana kallon mutane da su , haka kuma kamaninsa tamkar ba ciwon ne kadai damuwar rashin maganarsa da saurin sakin fuskarsa ba, kamar a cikin lamarin nasa harda wani abu mai shige da iza, ko nace mulki dake fita a tare da shi
A hankali ya sauke idannuwansa a saman fuskar iyalinsa a karro na biyu kennan bayan sun shigo ta samu shigowar itama ta zubawa yan matan ido bayan ta ja ta tsaya a wajen da take , itama a jikinta sutura ce ta doguwar riga, sai dai tata fara ce sannan budadiya ce sosai hakan ya sa ba'a iya gannin girman ramar tata itama, aman ta fuskarta ana iya gane itama ba jikin ne da ita ba, du ya zube
A hankali ta juyo wajen da yake tsaye ta zuba idannuwanta cikin nasa, sai kuma ta sake waigawa ta sake kallon yan matan da tsoron laifukansu ya hanna su sake dankarowa a guje jikin iyayen nasu, tun bayan zuwan da suka yi na farko
A hankali ta maida kanta kan matan dake tsaitsaye bayan sauran yan matan nan da ta gama yarda cewa nata ne, Harma ta idasa bambance kowace a cikinsu
Muryarta cen ciki tana rawa ta ce" Asalamu alaikum wa rahamatullah wa barakatuhu"
Hawayen dake cikin idannuwan yan matan ne ya bale da kansa
A hankali Shuwwa ta dan daga kafarta bayan Mama ta amsa salamar a bayane da fara'a kwonce saman fuskarta ta nufota ta kamo hannunta harma tana mai yi mata marhabun ta waiga wajen mijin nata da ya ba wannan bawan Allah damar gama fahimtar wajen da yake, tare da wa yake, da mutanen dake gabansa a tsanake ba tare da ya azalzala shi zuwa wajen zama ba ta ce" CHIEF, a karaso shi ya zauna, kar tsayuwar tai masa yawa......"
A nutse CHIEF OF ARMY ya ce" Bismillah , mu je wajen zama........."
A hankali ya sake lumshe idannuwansa yana kallon yarinyar da a da sai tana saman kirjinsa take iya yin barci, wace ya tafi sallah masalaci ya barta zata ci abinci ita da yar uwarta, itace ta zama cikakiyar budurwa haka a gabansa a tsaye
A raunane ta ce" Abuiiiiiiiiii "
Sai da zuciyarsa ta buga da wani irin karfin gaske, irin mai motsa soyayar nan ta uba da y'ayansa
A hankali ya sake kallon fuskarta da hawaye suka gaba wankewa, ba ko diz din abin shafe shafe na kwaliya na mata a fuskar tata, aman yadda take walwali zai nuna maka a cikin nutsuwar zuciya take
A cen kasan zuciyarsa ya ringa taslima ga ubangijin talikai, zuciyarsa ta fara sanyaya da kuntacen kuncin da ta dauka na shekara da shekaru, ya fara yarda da maganar matarsa cewa ya yi kokari ya samu y'ayansa da ransa, ta tabata Allahn da ya dora masu wannan jarabawa shine zai zamto gatansu
A hankali ya sake fuskantarta sosai, yana ta kallonta kafin ya sauke idannuwansa a saman fuskar yar uwarta
Oh Nahidt dinsa
Yar matashiyar yarsa mai cike da kamala da fada da ilimi da wayau, yarinyar da ta tashi da zafin nema danma baya bari, itace ta zama wannan budurwar? Ya Allah alhamdulilah y'ayansa ne a hade gasunnan a gabansa?
Mama ce ta raka uwar gidan Dad da kallo a lokacin da ta yi gaba sanann ta sake fadin" Abansu ku karaso mana"
Sannan ta fuskanci Mama dake kallon bayan y'ayan nata, wa'inda sai su kalli mahaifinsu, sai kuma su kalleta a sanyaye ta ce" Ki kirayesu mana Hajia....."
Mama ta dan kure fuskar Maman Muhay da kallo kafin cen ciki ta furta" Sun gane ni?"
Mama ta sakar mata Murmushi itama kasa kasa sosai ta ce" kina tunanin ke Allah bai haska goshinki bamban da na wasu iyayen a idannuwan y'ayanki ba?"
Muryarta kasa kasa sosai ta dago hannunta tana kallon fuskar Mama da yadda ta zauna daf da ita haka ba kyama ba komai ta ce" Na kasa gane yaya aka yi su dake saudiya yara kannana suka samu zuwa nan? Sallah kika je kika taimaka masu? Kece kika rike min y'ayana da mutunci haka! Ashe da na cewa babansu gaba faya duniya kar ya yarda da kowa daga ni sai shi na tafka kuskure, yana iya yarda da daidaiku irinku?"
Mama gannin Mamansu ta rikice, gashi su din kansu a wajen nan da suke yanzun sun jimke hannayensu waje daya sun sada kawunnansu , domin daga mamansu har babansu babu wanda ya yi kiransu, su kuma basu je da gagawa ba dan sun gama tsoratar da kansu, Maman Muhay ta dubesu da tausayawa ta ce" Me kuke jira haka ne? Me kuke jira ne yan matana?"
Ai dama kam jira suke, kiris suke jira a ce, so suke a basu damar aikata hakan
Maganar ta saka kamar ta kunna su da rigai rigai suka kawo kansu wajen mahaifiyarsu da har ta dan fara cirawa zata mike suka koma gaba daya suka zube a saman kujerar suka saka kuka irin mai karfin nan har y'ayan da ita din kanta
A hankali ya bude idannuwansa bayan ya rufe ruf yana tunanin a duniya anya ko harbe wanda ya masa yankan kaunar nan ya yi ya huce kuwa?, Ya raba shi da abinda ya haifa bayan shi ya yi nesa ya bara masa komai da komai?
A zabure ya sauke idannuwansa a kansu gaba dayansu a lokacin da suke fadin" umah, wayo Umanmu, Mamah har kabarinku aka kaimu"
Da karfi Shuwwa ke sake shigewa jikinta tana fadin" Ni dama na san baku mutu ba, ina kuka tafi? Ina kuka je kuka barmu? Ina kuka je?"
Zurbat ya mike daga gefen Dad, da karfin zuciya ya karasa wajen da suke kafin shima ya kai inda suke rukunkume da junna ya rukunkume su da karfi yana rintse idannuwansa
A nutse suka gama gyara ko'ina, sannan suka rufo suka koma bangaren Maman suka shiga girke girke, dama yau girkinta ne, hakan ya sa suka yi zama daya, da kansu sai masu aiki dake dan dauko abin daukowa su mayar da na maidawa suka yi tsararun girke girke, ciki harda favorite girkin da mahaifinsu ya fi so suka gabatarwa da Mama ta kuwa basu hadin kai suka girka masa , watau cus cus da boulette din naman kaza, sai jus na kwakwa mai sanyi , kai abincin saima da ya shiga cikin kwanoni na alfarma ya karra daukan kalla, ba'a cewa komai domin tabas ana iya ciza yatsa wajen dandanonsa
Da yama , wajen karfe shida Dad ya sanarwa Mama cewar sun kusa karasowa ya same su a bangaren bakin gaba dayansu, ashe har sauran matansa ya fada masu cewar su hadu dan tarbar bakim da yake tafe da su
Kasancewar babu wanda ya san wasu bakin ne? Domin basu san cewa wai mararsa lafiyan nan ne za'a tarba haka ba, ya saka su zuwa din
Sai dai sun yi mamakin gannin Matar MUHAY cikin shiga ta bak'ar abaya har kasa, ta yane kanta da mayafin abayar, sannan da bak'ar safa a kafarta, hakama yar uwarta irin shigarta ce a jikinta sak, hakan sai ya fitar da kamaninsu tamkar wasu y'ayan larabawa, kalar fatarsu ta sake amsar shigarsu, nanadewar da suka yiwa dan kwalinsu kuwa ya amshi yannayin fuskarsu, kowace da kamar wanda take yi a cikin iyayensu, sai dai jini da baya karya ne ya sa tashi dayama kana iya tunanin lalle kamarsu daya, sai in ka zauna da su ne zaka gane jinni ne mai karfi a tsakaninsu
Tabas sauran sun yi mamakin ganninsu haka dare dare a falon da ya dauki kaya ya yi wani irin kyau, ga kanshi ga sanyin AC na tashi ta ko'ina, ga lalausan capet ga tsaftar waje, sai dai babu wace ta fitar da mamakinta, aman kuma sun baza ido su ga abinda zai faru, domin shi ai kishi kumalon mata ne, kowace na da kalar nata kishin, bale uwar gidansa da ta gama daukarwa niyar in dai mijin nasu wasu bakin alfarma ne da shi bai tashi saukarsu ba sai yau ranar girkin uwar dan gwal walahi za'a yita kuwa a gidan nan, ita fa ta fa kai makura fa!, Walahil azim ta kai makura
Sunna nan zaune , ba wata hira suke yi ba, TV ce aka kunna aka rage amonta sosai a tashar da basu da aiki sai karatun alkur'ani, shi yake tashi a tausashe hakan ya sa kowace ke abinda ta ga ya fi mata zaman shirun, wata na waya ne, wata na karra harare harare ne, wata na shaaninta hankali kwonce ne, yan matan biyu kuwa kowace a cikin zulumi da kallon hanya suke, zuciyarsu na cike da tunanin yaya jikin iyayen nasu ne?
Wani soja ne guda ya bude kofar ya shigo bayan ya yi salama sannan ya sake bude kofar da kyau
Gaba dayansu ne suka mimike sunna kallon hanyar shigowar
Father ne ya fara bayana kadan , kafin ya sake rike mutumen dake bayansa da kyau dan ya taimaka masa ya shigo da kyau
A lokacin da ya bayana babu wanda bai tsura masa ido a cikinsu ba
Tabas rama ta samu wajen zama a jikin magaifinsu, sai dai abin mamaki annuri ya fara samun wajen zama a yanzu a tare da shi, haka kuma ramar ba kamar wace take hade da muguwar dati da duguzar gashin fuska da na kai din nan bace, a yanzun harda hiraminsa da ya dora a saman kansa, ga manyan idannuwansa farare kal yana kallon mutane da su , haka kuma kamaninsa tamkar ba ciwon ne kadai damuwar rashin maganarsa da saurin sakin fuskarsa ba, kamar a cikin lamarin nasa harda wani abu mai shige da iza, ko nace mulki dake fita a tare da shi
A hankali ya sauke idannuwansa a saman fuskar iyalinsa a karro na biyu kennan bayan sun shigo ta samu shigowar itama ta zubawa yan matan ido bayan ta ja ta tsaya a wajen da take , itama a jikinta sutura ce ta doguwar riga, sai dai tata fara ce sannan budadiya ce sosai hakan ya sa ba'a iya gannin girman ramar tata itama, aman ta fuskarta ana iya gane itama ba jikin ne da ita ba, du ya zube
A hankali ta juyo wajen da yake tsaye ta zuba idannuwanta cikin nasa, sai kuma ta sake waigawa ta sake kallon yan matan da tsoron laifukansu ya hanna su sake dankarowa a guje jikin iyayen nasu, tun bayan zuwan da suka yi na farko
A hankali ta maida kanta kan matan dake tsaitsaye bayan sauran yan matan nan da ta gama yarda cewa nata ne, Harma ta idasa bambance kowace a cikinsu
Muryarta cen ciki tana rawa ta ce" Asalamu alaikum wa rahamatullah wa barakatuhu"
Hawayen dake cikin idannuwan yan matan ne ya bale da kansa
A hankali Shuwwa ta dan daga kafarta bayan Mama ta amsa salamar a bayane da fara'a kwonce saman fuskarta ta nufota ta kamo hannunta harma tana mai yi mata marhabun ta waiga wajen mijin nata da ya ba wannan bawan Allah damar gama fahimtar wajen da yake, tare da wa yake, da mutanen dake gabansa a tsanake ba tare da ya azalzala shi zuwa wajen zama ba ta ce" CHIEF, a karaso shi ya zauna, kar tsayuwar tai masa yawa......"
A nutse CHIEF OF ARMY ya ce" Bismillah , mu je wajen zama........."
A hankali ya sake lumshe idannuwansa yana kallon yarinyar da a da sai tana saman kirjinsa take iya yin barci, wace ya tafi sallah masalaci ya barta zata ci abinci ita da yar uwarta, itace ta zama cikakiyar budurwa haka a gabansa a tsaye
A raunane ta ce" Abuiiiiiiiiii "
Sai da zuciyarsa ta buga da wani irin karfin gaske, irin mai motsa soyayar nan ta uba da y'ayansa
A hankali ya sake kallon fuskarta da hawaye suka gaba wankewa, ba ko diz din abin shafe shafe na kwaliya na mata a fuskar tata, aman yadda take walwali zai nuna maka a cikin nutsuwar zuciya take
A cen kasan zuciyarsa ya ringa taslima ga ubangijin talikai, zuciyarsa ta fara sanyaya da kuntacen kuncin da ta dauka na shekara da shekaru, ya fara yarda da maganar matarsa cewa ya yi kokari ya samu y'ayansa da ransa, ta tabata Allahn da ya dora masu wannan jarabawa shine zai zamto gatansu
A hankali ya sake fuskantarta sosai, yana ta kallonta kafin ya sauke idannuwansa a saman fuskar yar uwarta
Oh Nahidt dinsa
Yar matashiyar yarsa mai cike da kamala da fada da ilimi da wayau, yarinyar da ta tashi da zafin nema danma baya bari, itace ta zama wannan budurwar? Ya Allah alhamdulilah y'ayansa ne a hade gasunnan a gabansa?
Mama ce ta raka uwar gidan Dad da kallo a lokacin da ta yi gaba sanann ta sake fadin" Abansu ku karaso mana"
Sannan ta fuskanci Mama dake kallon bayan y'ayan nata, wa'inda sai su kalli mahaifinsu, sai kuma su kalleta a sanyaye ta ce" Ki kirayesu mana Hajia....."
Mama ta dan kure fuskar Maman Muhay da kallo kafin cen ciki ta furta" Sun gane ni?"
Mama ta sakar mata Murmushi itama kasa kasa sosai ta ce" kina tunanin ke Allah bai haska goshinki bamban da na wasu iyayen a idannuwan y'ayanki ba?"
Muryarta kasa kasa sosai ta dago hannunta tana kallon fuskar Mama da yadda ta zauna daf da ita haka ba kyama ba komai ta ce" Na kasa gane yaya aka yi su dake saudiya yara kannana suka samu zuwa nan? Sallah kika je kika taimaka masu? Kece kika rike min y'ayana da mutunci haka! Ashe da na cewa babansu gaba faya duniya kar ya yarda da kowa daga ni sai shi na tafka kuskure, yana iya yarda da daidaiku irinku?"
Mama gannin Mamansu ta rikice, gashi su din kansu a wajen nan da suke yanzun sun jimke hannayensu waje daya sun sada kawunnansu , domin daga mamansu har babansu babu wanda ya yi kiransu, su kuma basu je da gagawa ba dan sun gama tsoratar da kansu, Maman Muhay ta dubesu da tausayawa ta ce" Me kuke jira haka ne? Me kuke jira ne yan matana?"
Ai dama kam jira suke, kiris suke jira a ce, so suke a basu damar aikata hakan
Maganar ta saka kamar ta kunna su da rigai rigai suka kawo kansu wajen mahaifiyarsu da har ta dan fara cirawa zata mike suka koma gaba daya suka zube a saman kujerar suka saka kuka irin mai karfin nan har y'ayan da ita din kanta
A hankali ya bude idannuwansa bayan ya rufe ruf yana tunanin a duniya anya ko harbe wanda ya masa yankan kaunar nan ya yi ya huce kuwa?, Ya raba shi da abinda ya haifa bayan shi ya yi nesa ya bara masa komai da komai?
A zabure ya sauke idannuwansa a kansu gaba dayansu a lokacin da suke fadin" umah, wayo Umanmu, Mamah har kabarinku aka kaimu"
Da karfi Shuwwa ke sake shigewa jikinta tana fadin" Ni dama na san baku mutu ba, ina kuka tafi? Ina kuka je kuka barmu? Ina kuka je?"
Zurbat ya mike daga gefen Dad, da karfin zuciya ya karasa wajen da suke kafin shima ya kai inda suke rukunkume da junna ya rukunkume su da karfi yana rintse idannuwansa