Sashe 267
Mafari Hargitsin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bayan cikar sati biyu da kwanaki biyu Amnee ta koma Nigeria inda ta je ta tarar da labari mafi daɗi da Prof ya tare ta da shi kan ya samarwa da ƙanwar sa Rahima Miji .
***
Sheikh Mukhtar ɗaya ne daga cikin jerin ƙannen abokansa da bai yasar da zumunci ba ko bayan mutuwar wansa yake ziyartar sa lokaci zuwa lokaci muddin ya shigo garin Maiduguri daga can ƙasar Saudi-Arabia da yake aiki da zama tare da iyalin sa sama da shekaru ashirin da yayi aure.
Wannan zuwan nasa lokacin da Prof yake tambayar sa iyalin sa yake shaida masa ita matar tasa ta rasu shekarar da wuce .
Prof ya masa ta'aziyya bayan nan ya shawarce shi da kar yayi jinkirin yin wani auren saboda shi aure ibada ne sannan kuma kariya ne .
A lokacin Sheikh Mukhtar ya nuna masa cewa har kawo yanzu dai bai samu matar da ta kwanta masa ba wacce ya yarda da hankalin ta da zai iya danƙa mata amanar tarbiyyar 'ya'yan sa da matar sa ta mutu ta bar masa su huɗu .
Sannu kan hankali cikin dabara irin ta manya Prof ya gabatar masa da Khaalty Rahima cikin sa'a da ganin girman sa Sheikh Mukhtar ya nuna amincewar sa É—ari bisa É—ari muddin dai ita ma ta amince da shi .
Lokacin da aka sanarwa da Khaalty Rahima batun Sheikh Mukhtar bata ƙi ba tunda dai iyayen-goyon ta sun amince ita kuwa me zai ta tayi gardama idan tana da damuwa ɗaya ce ji da tayi ƙasar za ta bari gaba ɗaya ta bar Bulama dan ta sauran 'ya'yan ta mata ta san Allah ya riga ya sanya mata su a hannun nagartattun Mazaje '
Damuwar ta Bulama ne da ya shaƙu da ita fiye da misali sannan babu wani dangin sa na uba da aka samu ɓullowar su har kawo yau duk kuwa da neman da aka ta yi saboda har kawo yau da ake ɗiban shekaru fiye da bakwai da tarwatsa musu gari da 'Yan tawayen Boko Haram suka yi alƙaryar su bata sake kafuwa ba an riga an shafe ta mafi yawan mutanen su kuma sun mutu da take hasashen ciki har da mafiya-yawan dangin Uban su Yakaka da daman ba wani yawa suka cika ba ƙaramar zuri'a ce da su masu gajeran baya .
Duk da ba wai shakkun Bulama zai wahala bane idan har ta bar shi a hannun Amnee sai dai tasirin tsakanin uwa da ɗa ne musamman waɗan da suka shaƙu ya haka raba tsakanin su ba ƙaramin abu bane sai ko Mutuwa .
Ga jin daɗin ta kuma lokacin da suka yi ganawar farko da Sheikh Mukhtar shi da kansa ma ya mata batun riƙon Bulama zai dawo hannun sa daga zarar sun yi aure .
Da yake lamarin ba wai na yara bane cikin satika uku har magana tayi ƙarfi inda nan da satika huɗu mai zuwa za'a ɗaura auren idan ya tashi tafiya nan da watanni biyu ya tafi da Matar sa da ɗan su .
Bayan watanni shida.
Maradi Niger
Siyama tare da Falmata ne tsaye suna Sallama a jikin motar da Biyamuradi Youssoufa yake lafe a ciki yana riƙe da Amina wacce Falmata ta mata laƙabi da ( Ukhtee ) take ƙiran ta haka da kuma sunan ya bi bakin jama'a kowa ma hakan ke ƙiran ta.
Jin Sallamar tasu taƙi yankewa yasa Youssoufa leƙo kan sa yana cewa "Siyama kin ka ce yau aikin rana kin ka tahi yanzou kouwa ga hantsi ta ɗagga ko kouwa kin fara wassa ne da aikin naki ko kouma kin gajiya ne za ki bari dagga farawar ki.?
Da sauri Siyama ta saki hannun Falmata da ta riƙe jin cewa Biyamuradi Youssouf ya sako maganar aikin da da kyar yarda ta nema ta fara zuwa har sai da Maimartaba ya sa baki yace aikin ta na ceton rai ne sannan tun tasowar ta burin ta ne ta zama likitar haƙora ƙaƙa zai hana ta bayan shi ya san daɗin samun cikar buri a rayuwa tunda shi ma babu wanda ya katse masa nasa burin na zama Babban Soja mai yiwa ƙasar sa hidima .
Ba yadda ya iya haka ya haƙura aka samar mata da aiki a babban asibitin jaha tare da sharaɗin ba ita babu bin sa jaharTahoua sai dai shi zai dunga zuwa kamar yadda suke yi a tun can baya .
Babu jaa Siyama ta amince saboda ranta ya afu ga son taimakon Al'ummar ta itama lokaci yayi da za ta bayar daga ilmin da Allah ya hore mata falalar sa .
Baya tayi tana jaan mayafin ta ta rufe cikin ta da ya fara girma da yake nuni da nan ba da jimawa ba Ukhtee za ta samu ƙani ko ƙanwa .
"Ƙamnata Allah shi kiyaye mukku hanya hirar mu ba mai yankewa ce ba ina dai sake faɗa miki dan Allah dagga kin koma ecole ki dagewa karatu kiyi zarra ga abokan karatun ki hakan zai zama abun alfahari ne a gare mu.
Falmata tana murmushi ta amsa da "Insha Allah ba zan baki kunya ba Docteur Siyama nan da wassu 'yan shekaru ƙamnar ki zata zama diplômée.
"Allah shi badda sa'a ƙamna ta.
"Amin .
ta amsa tana shigewa Mota direba ya jaa suna barin gidan , Falmata ta waigo tana miƙa hannu domin ɗaukar Ukhtee da take ta tsalle a jikin Baban ta tana wasa girman jikin ta da wayon ta sun wuce na watannin ta shidda sai dai a kai ta watanni goma .
Noƙewa tayi tana ƙin zuwa ta faɗa jikin Baban ta da sauri tana ƙyaƙƙyala dariya irin ta yaran da lafiya da jin daɗi ya wadace su .
A lokaci ɗaya iyayen nata su ma suka sa dariya suna bin ta da kallon dake cike da ƙauna Falmata ta ɗan jaa kumatun ta "Ukhtee yau ni kike yiwa ƙyauya ? Ai anjima kaɗan za ki zo ne .
Shafa kan ta Youssoufa yayi wanda ya sha adon ribbons irin na yaran gata da ya dace da lallausar sumar kan ta mai tarin yawa da yake sake fiddo kyaun ta da ido bai gajiyawa wajen kallon ta.
"Ki rabbu da ita Fatima kin iya shigga tsakanin É—iya da Mahaifin ta ?
Girgiza kai Falmata tayi tana mai matsowa jikin sa ta kwantar da kan ta ta ɓarin jikin sa na dama ita da ukhtee fuskokin su na kallon juna akan ƙirjin sa .
Haɗa su yayi ya rungume bayan ya sumbanci kan Falmata da yake ƙirjin sa. "Fatima-zahra ina son ku irin son da ba shi da iyaka.
"Biyamuradi Youssoufa mu ma haka muna ƙaunar ka irin ƙaunar da bata da iyaka.
Direban da yake iya jiyo sautin su sai ya ƙara volume ɗin radio da waƙar matashiyar mawaƙiyar nan camelia jordana mai taken mens moi take tashi cikin baitukan ta inda take cewa :
"Je rougis je rougis je rougis
Quand tu me souris
Ô tes yeux menthols
Me mentent et m'affolent
"Oh mens-moi si tu m'aimes
Mais me manque pas
Me manque pas
Me manque pas
"Je défaille à tes mots fous
Mots doux vaudous
Quand je suis dans tes bras
Hé dis, tu penses à quoi ?
Abuja
Sofi lokacin da ta bar gida bayan ta ci uwar wahala kafin ta samu É—an tasi É—in da zai yadda ya É—auke ta taje ta sayar da É—ankunnen gwal É—in da ya rage mata tal a kunnen ta ta biya shi kuÉ—in sa .
Daga nan wani ɗan ƙaramin hotel mai sauƙin kuɗi ya kai ta ta kama ɗaki ta shiga ta zauna a cikin dabarar ta da tayi niyyar ƙullawa na rufewa kowa maganar saki ukun da Hamza ya yi mata har sai zuwa lokacin da aikin boka ya ɗau wuta akan Hamza shi da kansa ta san zai fara neman ta daga nan idan ta gama wana shi ta rama duk irin cin mutumcin da ya mata sai ta nemi da su rufe zancen sakin a tsakanin su kada kowa ya ji su koma su cigaba da zaman su..
Tasha alwashin sai ta walakanta rayuwar Yakaka dan ta ma fasa kashe ta da wuri sai ta mata gashin ƙuma sannan za ta ƙarar da numfashin ta a doron ƙasa..
Kashe wayar ta tayi ta kwanta amma ta gagara bacci saboda tsamin da jikin ta yayi yana mata ciwo na fitar hankali .
Dole ta sa ta tafi asibiti aka bata magunguna ta zo ta sha .
Daren ranar haka ya ƙare mata tana surutan iska .
Washegari kuwa da farar Safiya ta dasa zaman ƙiran Samy Baby sai dai layi ya ƙi shiga wasa-wasa sai da ta shafe tsawon yinin ranar da waya a hannun ta tana ƙiran layin da Samy Baby ta ƙira ta da shi har wayar chaji ya ƙare ta mutu bata samu ta shiga ba
Ta lallaɓa ta sayo kan chaja ta zo tasa bata jira wayar ta cika ba ta dasa daga inda ta tsaya wajen ƙiran layin Samy Baby .
Kafin cikar kwanaki uku Sofi tayi ƙaramar hauka a ɗakin otel saboda dai babu wani saƙo daga Samy baby babu alamar sa kuma ita ta gagara samun ta sannan kuma ko alama bata ga ƙira daga wani nata ba da da har kashe wayar take dan kar a ƙira ta.
Doctor Hamzan da take hasashen aiki ya fara cin sa kuwa duk lokacin da taga alamun Kamfanin Sadarwa sun tura mata saƙo zato take shine .
Haka zata yini sambatun ƙiran sunan sa.
Kafin cikar Sati kuɗin hannun ta ya ƙare da daman fiye da rabi zama take da yunwa tana biyan kuɗin ɗakin da take kwana .
Ala tilas ta fita daga Otel ɗin kawo yanzu kwakwalwar ta ta ƙara birkicewa ta kasa yarda da abun da ya faru da ita yake kuma sake faruwa da ita .
Ciwon mazaunan ta da suka É—uri ruwa tun ranar da ta yanke shi yafi kome É—aga mata hankali saboda azabar da take sha kullum dare bata iya bacci .
Ba arziƙi ta kama hanyar gidan su a birkice kamar sabuwar mahaukaciya .
***
Sheikh Mukhtar ɗaya ne daga cikin jerin ƙannen abokansa da bai yasar da zumunci ba ko bayan mutuwar wansa yake ziyartar sa lokaci zuwa lokaci muddin ya shigo garin Maiduguri daga can ƙasar Saudi-Arabia da yake aiki da zama tare da iyalin sa sama da shekaru ashirin da yayi aure.
Wannan zuwan nasa lokacin da Prof yake tambayar sa iyalin sa yake shaida masa ita matar tasa ta rasu shekarar da wuce .
Prof ya masa ta'aziyya bayan nan ya shawarce shi da kar yayi jinkirin yin wani auren saboda shi aure ibada ne sannan kuma kariya ne .
A lokacin Sheikh Mukhtar ya nuna masa cewa har kawo yanzu dai bai samu matar da ta kwanta masa ba wacce ya yarda da hankalin ta da zai iya danƙa mata amanar tarbiyyar 'ya'yan sa da matar sa ta mutu ta bar masa su huɗu .
Sannu kan hankali cikin dabara irin ta manya Prof ya gabatar masa da Khaalty Rahima cikin sa'a da ganin girman sa Sheikh Mukhtar ya nuna amincewar sa É—ari bisa É—ari muddin dai ita ma ta amince da shi .
Lokacin da aka sanarwa da Khaalty Rahima batun Sheikh Mukhtar bata ƙi ba tunda dai iyayen-goyon ta sun amince ita kuwa me zai ta tayi gardama idan tana da damuwa ɗaya ce ji da tayi ƙasar za ta bari gaba ɗaya ta bar Bulama dan ta sauran 'ya'yan ta mata ta san Allah ya riga ya sanya mata su a hannun nagartattun Mazaje '
Damuwar ta Bulama ne da ya shaƙu da ita fiye da misali sannan babu wani dangin sa na uba da aka samu ɓullowar su har kawo yau duk kuwa da neman da aka ta yi saboda har kawo yau da ake ɗiban shekaru fiye da bakwai da tarwatsa musu gari da 'Yan tawayen Boko Haram suka yi alƙaryar su bata sake kafuwa ba an riga an shafe ta mafi yawan mutanen su kuma sun mutu da take hasashen ciki har da mafiya-yawan dangin Uban su Yakaka da daman ba wani yawa suka cika ba ƙaramar zuri'a ce da su masu gajeran baya .
Duk da ba wai shakkun Bulama zai wahala bane idan har ta bar shi a hannun Amnee sai dai tasirin tsakanin uwa da ɗa ne musamman waɗan da suka shaƙu ya haka raba tsakanin su ba ƙaramin abu bane sai ko Mutuwa .
Ga jin daɗin ta kuma lokacin da suka yi ganawar farko da Sheikh Mukhtar shi da kansa ma ya mata batun riƙon Bulama zai dawo hannun sa daga zarar sun yi aure .
Da yake lamarin ba wai na yara bane cikin satika uku har magana tayi ƙarfi inda nan da satika huɗu mai zuwa za'a ɗaura auren idan ya tashi tafiya nan da watanni biyu ya tafi da Matar sa da ɗan su .
Bayan watanni shida.
Maradi Niger
Siyama tare da Falmata ne tsaye suna Sallama a jikin motar da Biyamuradi Youssoufa yake lafe a ciki yana riƙe da Amina wacce Falmata ta mata laƙabi da ( Ukhtee ) take ƙiran ta haka da kuma sunan ya bi bakin jama'a kowa ma hakan ke ƙiran ta.
Jin Sallamar tasu taƙi yankewa yasa Youssoufa leƙo kan sa yana cewa "Siyama kin ka ce yau aikin rana kin ka tahi yanzou kouwa ga hantsi ta ɗagga ko kouwa kin fara wassa ne da aikin naki ko kouma kin gajiya ne za ki bari dagga farawar ki.?
Da sauri Siyama ta saki hannun Falmata da ta riƙe jin cewa Biyamuradi Youssouf ya sako maganar aikin da da kyar yarda ta nema ta fara zuwa har sai da Maimartaba ya sa baki yace aikin ta na ceton rai ne sannan tun tasowar ta burin ta ne ta zama likitar haƙora ƙaƙa zai hana ta bayan shi ya san daɗin samun cikar buri a rayuwa tunda shi ma babu wanda ya katse masa nasa burin na zama Babban Soja mai yiwa ƙasar sa hidima .
Ba yadda ya iya haka ya haƙura aka samar mata da aiki a babban asibitin jaha tare da sharaɗin ba ita babu bin sa jaharTahoua sai dai shi zai dunga zuwa kamar yadda suke yi a tun can baya .
Babu jaa Siyama ta amince saboda ranta ya afu ga son taimakon Al'ummar ta itama lokaci yayi da za ta bayar daga ilmin da Allah ya hore mata falalar sa .
Baya tayi tana jaan mayafin ta ta rufe cikin ta da ya fara girma da yake nuni da nan ba da jimawa ba Ukhtee za ta samu ƙani ko ƙanwa .
"Ƙamnata Allah shi kiyaye mukku hanya hirar mu ba mai yankewa ce ba ina dai sake faɗa miki dan Allah dagga kin koma ecole ki dagewa karatu kiyi zarra ga abokan karatun ki hakan zai zama abun alfahari ne a gare mu.
Falmata tana murmushi ta amsa da "Insha Allah ba zan baki kunya ba Docteur Siyama nan da wassu 'yan shekaru ƙamnar ki zata zama diplômée.
"Allah shi badda sa'a ƙamna ta.
"Amin .
ta amsa tana shigewa Mota direba ya jaa suna barin gidan , Falmata ta waigo tana miƙa hannu domin ɗaukar Ukhtee da take ta tsalle a jikin Baban ta tana wasa girman jikin ta da wayon ta sun wuce na watannin ta shidda sai dai a kai ta watanni goma .
Noƙewa tayi tana ƙin zuwa ta faɗa jikin Baban ta da sauri tana ƙyaƙƙyala dariya irin ta yaran da lafiya da jin daɗi ya wadace su .
A lokaci ɗaya iyayen nata su ma suka sa dariya suna bin ta da kallon dake cike da ƙauna Falmata ta ɗan jaa kumatun ta "Ukhtee yau ni kike yiwa ƙyauya ? Ai anjima kaɗan za ki zo ne .
Shafa kan ta Youssoufa yayi wanda ya sha adon ribbons irin na yaran gata da ya dace da lallausar sumar kan ta mai tarin yawa da yake sake fiddo kyaun ta da ido bai gajiyawa wajen kallon ta.
"Ki rabbu da ita Fatima kin iya shigga tsakanin É—iya da Mahaifin ta ?
Girgiza kai Falmata tayi tana mai matsowa jikin sa ta kwantar da kan ta ta ɓarin jikin sa na dama ita da ukhtee fuskokin su na kallon juna akan ƙirjin sa .
Haɗa su yayi ya rungume bayan ya sumbanci kan Falmata da yake ƙirjin sa. "Fatima-zahra ina son ku irin son da ba shi da iyaka.
"Biyamuradi Youssoufa mu ma haka muna ƙaunar ka irin ƙaunar da bata da iyaka.
Direban da yake iya jiyo sautin su sai ya ƙara volume ɗin radio da waƙar matashiyar mawaƙiyar nan camelia jordana mai taken mens moi take tashi cikin baitukan ta inda take cewa :
"Je rougis je rougis je rougis
Quand tu me souris
Ô tes yeux menthols
Me mentent et m'affolent
"Oh mens-moi si tu m'aimes
Mais me manque pas
Me manque pas
Me manque pas
"Je défaille à tes mots fous
Mots doux vaudous
Quand je suis dans tes bras
Hé dis, tu penses à quoi ?
Abuja
Sofi lokacin da ta bar gida bayan ta ci uwar wahala kafin ta samu É—an tasi É—in da zai yadda ya É—auke ta taje ta sayar da É—ankunnen gwal É—in da ya rage mata tal a kunnen ta ta biya shi kuÉ—in sa .
Daga nan wani ɗan ƙaramin hotel mai sauƙin kuɗi ya kai ta ta kama ɗaki ta shiga ta zauna a cikin dabarar ta da tayi niyyar ƙullawa na rufewa kowa maganar saki ukun da Hamza ya yi mata har sai zuwa lokacin da aikin boka ya ɗau wuta akan Hamza shi da kansa ta san zai fara neman ta daga nan idan ta gama wana shi ta rama duk irin cin mutumcin da ya mata sai ta nemi da su rufe zancen sakin a tsakanin su kada kowa ya ji su koma su cigaba da zaman su..
Tasha alwashin sai ta walakanta rayuwar Yakaka dan ta ma fasa kashe ta da wuri sai ta mata gashin ƙuma sannan za ta ƙarar da numfashin ta a doron ƙasa..
Kashe wayar ta tayi ta kwanta amma ta gagara bacci saboda tsamin da jikin ta yayi yana mata ciwo na fitar hankali .
Dole ta sa ta tafi asibiti aka bata magunguna ta zo ta sha .
Daren ranar haka ya ƙare mata tana surutan iska .
Washegari kuwa da farar Safiya ta dasa zaman ƙiran Samy Baby sai dai layi ya ƙi shiga wasa-wasa sai da ta shafe tsawon yinin ranar da waya a hannun ta tana ƙiran layin da Samy Baby ta ƙira ta da shi har wayar chaji ya ƙare ta mutu bata samu ta shiga ba
Ta lallaɓa ta sayo kan chaja ta zo tasa bata jira wayar ta cika ba ta dasa daga inda ta tsaya wajen ƙiran layin Samy Baby .
Kafin cikar kwanaki uku Sofi tayi ƙaramar hauka a ɗakin otel saboda dai babu wani saƙo daga Samy baby babu alamar sa kuma ita ta gagara samun ta sannan kuma ko alama bata ga ƙira daga wani nata ba da da har kashe wayar take dan kar a ƙira ta.
Doctor Hamzan da take hasashen aiki ya fara cin sa kuwa duk lokacin da taga alamun Kamfanin Sadarwa sun tura mata saƙo zato take shine .
Haka zata yini sambatun ƙiran sunan sa.
Kafin cikar Sati kuɗin hannun ta ya ƙare da daman fiye da rabi zama take da yunwa tana biyan kuɗin ɗakin da take kwana .
Ala tilas ta fita daga Otel ɗin kawo yanzu kwakwalwar ta ta ƙara birkicewa ta kasa yarda da abun da ya faru da ita yake kuma sake faruwa da ita .
Ciwon mazaunan ta da suka É—uri ruwa tun ranar da ta yanke shi yafi kome É—aga mata hankali saboda azabar da take sha kullum dare bata iya bacci .
Ba arziƙi ta kama hanyar gidan su a birkice kamar sabuwar mahaukaciya .