← Book details Mafari Hargitsin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 258 OF 269

Sashe 258

Mafari Hargitsin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Ba laifi kika yi ba Wafaa , amma ban ji daÉ—i ba da kika manta cewa na hana ki kiyi aiki ke kaÉ—ai idan har ina gida ko da bacci nake ki dunga tashina muna yi tare .

Murmushi mai bayyana haƙora tayi ta ɗan sauƙe ajiyar zuciya lokacin da ta kashe gas saboda girkin ta ya kammala .

Tana ƙoƙarin juyowa ya sassauta riƙon da ya mata ta juyo tana fuskantar sa.

"Hannun ta ɗaya ta ɗora a ƙirjin sa tana ɗan bubbugawa a shagwaɓe tace "wallahi har hankali na ya tashi ko wani laifin na yi ban sani ba.

Dariya yayi yana riƙe hannun ta yace "laifi kika yi mana meyasa za ki wahalar min da ruhina da kika san koyaushe yana nan ne a  tare da ke , meyasa baki tada gangar jikin ba ? Anyi aikin tare da shi ?

Murmushi tayi tana kallon sa irin waɗannan kalaman nasa su suka ta dilmiye a cikin ƙaunar sa ba tare da ta ankara ba ko kaɗan baya mata ƙouron kalaman sa na soyayya kamar yadda baya ƙasa a guiwa wajen gwada mata ƙauna a zahiri bai kuma jinkirtawa wajen yaba mata a duk lokacin da tayi wani abun a yaba kome ƙanƙantar sa kuwa '

Maza irin sa sukan sauya akalar zuciyar kowacce mace cikin sauƙi .

Sauƙe idanun ta tayi ƙasa tana murmushi saboda wani irin narkakken kallo da yake mata , ita irin salon Soyayyar sa nawi take mata kunya take sa ta har ta dunga jin wani yarrr a jikin ta.

Ko kaɗan bata iya masa martanin kalaman sa , kuma bata jin daɗin hakan so take ita ma ta koya su dunga musayar ƙauna kamar abun zai fi armashi .

Sautin dariyar sa ta ji da yasa ta É—ago kanta da sauri tana kallon sa sai ta ga idanun sa bayan ta yake kallo .

Juya ta yayi yana mata nuni da wasu tattabaru Mata da Miji (aure ) , da suka sauƙa ta gaban tagar kitchen ɗin suna soyayyar su .

"Wow look at them Wafaa so lovely.

Ya furta hakan muryar sa kasa-kasa yana rungumeta ta baya.

Zuba musu ido tayi tana kallon yadda suke sumbatar junan su kamar sa cinye bakin juna, sun matukar birgeta tsuntsaye kenan ma suke wannan soyayyar ? Ba shakka soyayya aba ce mai daÉ—i.

Daga shi har ita shagala suka yi da kallon soyayyar tattabarun mai ban mamaki da Sanya sha'awa tare da nishadi a zuciyar ma'abota soyayya.

Basu Ankara ba Matar ta gayyaci Mijin dan Su cimma maƙurar soyayyar Su ganin haka yasa da sauri Yakaka ta ɗaga tafukan ta biyu tana rufe fuskar ta .

"Habibi mu bar su hakan nan zasu yi sirrin Su.

Ta furta hakan tana ƙoƙarin janye jiki daga wajen .

'Yar dariya Doctor Hamza yayi yana sauƙe mata hannun ta da ta rufe fuskarta da shi

Cike da zolaya a muryar sa yace "ki buÉ—e ido ki kalle su darasi za mu É—auka mu ma anjima sai mu gwada.

tana buÉ—e idanun ta ta gan su a halin da ita bata so da sauri ta sake rufe ido ta juya tana shigar da kan ta kirjin sa har a cikin ranta kunya ta ji .

Rungume ta yayi yana dariya ƙasa-ƙasa kunyar ta na ɗaya daga cikin abunda yasa yake ƙara son ta ,kunya alamun imani ce bayan haka tamkar ado take ga ma'abota ita.

Ƙiran wayar sa da aka yi shi ya katse shirun nasu ya sassauta riƙon da yayi mata kafin ya zaro wayar sa daga aljihu. 

Cikin ransa cike da addu'ar Allah yasa ba É—aya daga cikin waÉ—an da yake zato bane .

Addu'ar sa kuwa bata karɓu ba domin kamar yadda ya zata dai Baba Prof ne da kan sa yake ƙiran sa.

Cike da ladabi ya É—aga kiran suka gaisa kafin ya tsinkayi Baa yana masa maganar da yake gujewa tsawon sati guda .

"Hamza ka kuwa je kun taho da iyalin taka ?

Shiru yayi saboda ya san kawai ya tambaye shi ne ba wai dan bai san cewa bai je ba sai dan ya ba shi damar shigar da uzurin sa.

"Ban tafi ba Baa amma yau dai nake son na je Insha Allah .

"To ka daure dai ka je saboda kullum sai Mahaifiyar ta ta ƙirani bana son kayi wani abunda zai taɓa mana zumuncin mu na dai faɗa maka ina kuma sake maimaita ma shi aure daman haƙuri ke jagorantar sa sannan ba zaka gina gidan ka ba sai ka zama jajirtatcen Namiji tsayayye sannan gidan ka zai zama yadda ake so .

"Ina umartar ka da kaje anjima ka dawo da Matar ka ka kuma cigaba da haƙuri da su su duka biyun aure ibada ne .

"To Baa insha Allah zan je Allah ya ƙara girma.

"Madallah Allah ya muku Albarka baki É—aya.

"Amin

Ya amsa yana sauƙe wayar ya kashe.

Ba sai ya faɗa mata ba daga cikin maganganun sa ta fahimci akan me ake zance da lokacin da ta fahimta ba ƙaramar juriya tayi ba wajen ɓoye razanar ta ta juya tana ƙoƙarin zuba musu abincin a farantin da ta ɗauko .

"Wafaa ya ƙira sunan .

"Na'am ta amsa tana ƙin kallon sa .

Ɗan jimm yayi yana juya zancen da yasan dole ya taɓa mata rai kafin ya tattaro juriyar sa yace .

"Baa da Amnee sun ce Sofi ta dawo , dan haka anjima zan je mu dawo tare.

Wata 'yar fara'ar da take tsakanin laɓɓa ta sakar masa da 'yar dariya tace "Yeehh Anty Sofi Oyo-yo gaskiya naji daɗi Yaya Dacta .

Matso ta yayi yana mata rumfa fuskar sa babu walwala yace "me kika ce ?

"Cewa nayi naji daÉ—i .

Ta sake faÉ—in hakan da siririyar murya ganin yadda ya haÉ—e fuska .

"Ba wannan ba da wanne suna na ji kin ƙirani yanzu ?

Dariya tayi tana tura shi baya ta ce "Anty zata dawo sunan ka na baya ma zai dawo..

Abincin da ta fara zubawa shi ya hana ya sake riƙe ta amma muryar sa bata ɓoye halin da zuciyar sa take ciki na rashin jin daɗi ba yace "Wafaa kar ki rage ko ɗigo na daga yadda muka saba al'amuran mu dan wai Sofi za ta dawo idan kika yi hakan za mu ɓata ni da ke , umarni ne wannan nake ba ki .

Bai sake cewa da ita ƙala ba ya fita daga kitchen. zuciyar ta taji ta ƙuntata "to ita meye laifin ta dan ta ce zata janye sunan da take ƙiran sa da shi a gaban matar sa ? Ita a ganin ta kiyayewa take son yi sanin da tayi Sofi tayi nisa a fagen kishi.

Hawayen da suka cika gurbin idanun ta ne suka zubo , wani irin tsoro take ji kan dawowar Sofi ko yaya zaman su zai sake kasancewa ?

Jikin ta duk a sanyaye ta gama zuba abincin ta ɗauko ta nufi falon , a kan kujera ta hango shi kafin ta ƙaraso ya taryo ta ya karɓe farantin hannun ta , sai ta koma kitchen ta ɗauko masu kayan sha da ta haɗa .

Ɗan shiru ya ratsa tsakani kafin lokacin da ta fara zuba musu haɗaɗɗiyar Maqluba da ƙamshin ta ya ɗau wajen ya tado wa da Doctor Hamza muguwar yunwar da yake ji .

"Wow what a delicious ? a complete meal containing, carbs, protein, fats, fibre, essential vitamins and minerals.

Da murmushi take kallon sa lokacin da ya kai loma ta farko ya haɗiye ya sake ɗiban wata yana lumshe ido ya cigaba da cewa  .

"Wafaa do you know Basmati rice has higher fibre content and is a great option for various meal plans, prevents against Cancer cell formation and prevents constipation against heart health risk.? 

Tana ɓoye dariyar ta ta ɗan girgiza masa kai alamun bata sani ba.

Kazar da ya É—auka ya gutsira ita ya nufo bakin ta da sauran .

Noƙewa tayi tana dariya tace " ni fa ba kaza zan ci ba kawai shinkafar raina ke so.

Wara ido yayi yana mata kallon mamaki kafin yace "Come on ki ci kaza Wafaa chicken is a great source of lean protein and has abundance of selenium, phosphorus, niacin.

Haka ba dan ta so ba ta gutsiri kazar ta ci kafin ya cigaba da bata abincin Suna cikin ci tace "Habibi kai baka cin tumatir Sosai ni kuma shi nafi so ka dunga bani sosai.

Bayan ya haÉ—iye abincin bakin sa yace "eh kuma kina da gaskiya domin shi tomato is a great source of vitamin C, potassium, vitamin k1, folate which are great for normal tissue growth and cell function.

Dariyar da take ta riƙewa tuntuni ita ce ta kufce mata ta shiga ƙyalƙyalawa har tana kwanciya a jikin kujera , shiru yayi yana kallon ta da murmushi a laɓɓan sa daman burin sa kenan ya ga fara'ar ta farin-cikin sa yana tare da walwalar ta.

****

Kamar yadda Doctor Hamza ya alƙawarta A daren ranar bayan Sallar isha'i ya tafi gidan su Sofi domin su dawo tare lokacin da ya ɗora idanun akan ta sai da ya razana saboda ramar da yaga tayi cikin 'yan satika.

Yadda yake zaton za ta masa hauka sai ya ga akasin haka sai nan-nan take yi da shi daga ita har Mahaifiyar ta da hakan yasa dole shi ma ya sau jiki suka ɗan taɓa hira da Momy kori kamar kome bai faru ba.

Inda ya É—an ga alamun sauyi daga wurin su bai wuce lokacin da suka kawo masa girke-girken da aka shirya musamman domin shi sannan su ka matsa kan sai ya ci.

Shi kuwa ya riga ya É—ebi girkin Yakaka ya É—ora da lafiyayyen kunun aya da ta musu dan haka cikin sa a cike yake ha'in babu masaka tsinke , dan haka ya kafe kan cewa shi babu abunda zai iya sake sanyawa a cikin sa sai kuma gobe.

Nan ya ga yadda Sofi tayi kicin-kicin bai bi ta kan ta ba yace tayi sauri ta shirya ta zo su tafi.
Chapter 258 · 0% Book details