Sashe 223
Mafari Hargitsin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A hankali Falmata ta É—aga idanun ta ta É—ora ganin ta kan kyakkyawar doguwar matar da take tsaye gaban ta tana jifan ta da tsadaddan murmushin da yake sake fiddo zallar kyau da wayewar ta , ba sai an faÉ—a mata ba ta fahimci ita ce Mahaifiyar Yumna , kenan wannan ce Siyama matar Youssouf tuno da matsayin da suke kai a wajen juna ya sa tayi saurin juyawa ta É—aga taku tana barin wajen , zuciyar ta cike da tunanin abunda ya kawo su haka ? Ko sakin nata aka zo kawo mata tare da matar tasa ?
Karɓa irin ta girma da girmamawa ita iyalan Maimartaba suka samu daga wajen Prof da nasa iyalan , duk kuwa da cewa ba'a san da zuwansu ba , hakan bai hana a shiga hidima da su ba ka'in da na'in babu ƙyashi Prof ya buɗe bakin Aljihu aka shiga hidima da su kamar daman can an san da zuwan su dan haka basu tarar da gidan tare da wata alama ta ƙasƙanci ba .
Gidan Attajiri suka tarar da ya matuƙar birge su a matsayin gidan su Matar da Youssoufa yake aure , duk sai jikin Ammi da Asma'u '( yar Hajiya Mama ) yayi sanyi da daman su biyun ne suka zo da wata manufa ta daban , sai suka ga ko su sai dai su gwadawa gidan su Falmata sarauta amma ba dai su ƙasƙantar da su ba . ( Daman Bare-bari ai ba daganan ba indai fagen bajinta ne ) .
Tunda Falmata ta shige ɗaki bata fito ba a ciki tayi sallar ta ta magarib da isha'i ta hau gado ta lulluɓu bayan ta kashe wutar ɗakin , ta rasa takamaimai halin da zuciyar ta take ciki , farin-ciki ne ko saɓanin sa ?
"watau sai yau ya waiwayo ta ? Bayan yasan ya mata laifi , yasan cewa dole tana jiran sa , yasan kuma a halin da take ciki da halin da ta baro wajen sa a ciki .
Can ƙasan ranta kuwa , So take ta ji ko da tashin ƙamshin sa ko kuwa amon muryar sa dan ta san cewa ya zo amma ko alama bata ji ɗuriyar sa ba a gidan .
Sai juye-juye take yi akan gadon , juyi ta sake yi lokacin da taji an turo ƙofar an shigo gami da kunna wutar ɗakin haske ya gauraya da sauri ta miƙe zaune bayan ta yaye mayafin da ta rufu da shi ,
Khaalty Rahima ta gani a tsaye a bakin ƙofa , daga inda take tana iya hango ɓacin ran da yake shimfiɗe kan fuskar ta ,
" Mama sannu da shigowa .
Khaalty Rahima bata amsa ba sai da ta ƙaraso kusa da ita , sannan tace " me kike a ɗaki ke kaɗai ? Kina sane da baƙin da suke gidan nan domin ki suka zo , "yan uwan mijin ki ne na jini , wai me yake damun ki ne ? Aina kika koyo wannan mugun halin na walaƙanta mutane ?
A ɗan tsorace Falmata tace , kiyi haƙuri Maman mu , un daman ai naga Yakaka tana wajen su suna hira .
Daƙuwa Khaalty Rahima tayi mata da hannuwanta duk biyu , " kin ci gidan ku Falmata, dangin Mijin Yakaka ne ko naki ? To bari na faɗa miki gara tun wuri kiyi watsi da wannan banzan halin ki daina dan kuwa ba inda zai kai ki , Mijin ki ɗan Manyan mutane ne gaba da baya ɗan sarauta ne shi da 'yan uwan sa halin girma da girmamawa cikin sa suka taso , shi aka saba gwada musu , muddin kika ce zaki je musu da saɓanin sa ke ce za ki sha wahala kiyi baƙin jini a wajen su ba ke ba har ya'yan da zaki haifa musu .
Shigowar Amnee bai sa Khaalty Rahima ta tsagaita ba ta cigaba da cewa , " ki tashi ki shirya ki fito kije ki gaishe su da kyau da kyau biyu daga ciki yayun mijin ki ne ɗaya kuma ƙanwar sa ce ƙaramar su , ɗayar kuwa kishiyar ki ce nasan ba zaki gagara sanin cewa 'yar uwar sa bace da suke 'ya'yan Mace da Namiji dan haka gara ki nutsu kiyi hankali ki daina wannan futsancin naki da tsagerancin wofi ,idan ba ma Allah yayi ba ina ke ina su ?
Unm, unm , unm Rahima banda gori kuma , ai shi arziƙi da ɗaukaka na Allah ne , amma 'yata ke ma baki kyauta ba baƙon ka ai abun girmamawa yake a wajen ka , bare kuma waɗannan da suke tafe tun daga wata ƙasa musamman domin tafiya dake , ki shirya kije ku gaisa har can falon Baa Alaji za'a raka ki akwai Manyan mutane da suka zo tare ɗaya daga cikin su Baffan Maigidan ki ne kuma shine waziri garin su sai kuma wasu manya daga wajen su dan haka kiyi shiga ta kamala sosai ko na shirya ki ?
Sai a lokacin Falmata ta ɗago kanta da hakan ya bawa ƙwallar idanun ta da suka taru damar zubowa faɗan da Khaalty Rahima ta mata ya haɗu mata da tasowar miƙin irin cin mutuncin da 'yan uwan Youssoufa suka masu a Niamey da yana daga cikin dalilan da yasa ta bar shi wutsiya a zage.
Muryar ta na rawa tace " Maman mu da Amnee ku yi haƙuri ku yafe min , amma ni bazan koma ba.
Kallon da suka bita da shi bai sa ta tsaya ba cikin kuka ta cigaba da cewa
" 'yan uwan sa basa sona zagin mu suka dunga yi suna min gori har iyayena suka aibata sun ce É—an uwan su ya sake ni me zai yi da ni 'yar gudun Hijira 'yar matsiyata Mama har cewa suka yi ...
" Khalass Amnee tace tana zama a gefen ta ta riko ta zuwa jikin ta , kukan da take yi ya taɓa ran su sun kuma fahimce ta , daman Khaalty Rahima ta riga ta san akwai wani dalilin da yasa falmata ta yi mu su yadda tayi , tasan halin 'yar ta Falmata mutum ce mai zuciya da gudun raini , ko kusa bata yadda a taka ta ba tare da ta rama ba .
Amnee ta cigaba da cewa
"Ko ma me suka ce miki ai ga su dai yanzu iyayen su sun taso su da aiken zuwa su koma da ke cikin girmamawa saboda kin riga kin zama wata ɓangare na jikin su , kiyi haƙuri ɗaukaka bata zuwa a sauƙaƙe , sai an zage damtse an ware ƙwanji wajen neman ta an kuma haɗa da haƙuri da juriya , wa ya faɗa miki inda samun ɗaukakar ka yake zai kasance kewaye da masoyan ka ? Ai ɗaukaka mai tasiri ita ce wacce aka ratsa tsakanin maƙiya wajen samun ta .
" ki zama jaruma Fatima-zara gidan sarauta kike aure , Yarima kike aure watarana idan da rai Matar sarki za ki zama dan haka saurin fushi ai ba naki bane .
"Sau da dama akwai wuraren da fushi baya yin tasiri sai fa saɓanin sa watau kwantar da kai da kawaici , hannun da ya juri miƙo maka gorar duma kana shan ruwan ciki da ɗaci , sannu kan hankali watarana shi zai miƙo maka gorar zuma tattaciya ka kwankwaɗa daga zaƙin ta , muddin kayi haƙuri saboda kome na duniya ɗan haƙuri ne kiyi haƙuri ki maida kome ba kome ba , kin ji ko ?
Gyaɗa kai tayi tana share hawayen ta , zuciyar ta taji tana sanyaya daga ɗacin da ya cunkushe mata rai , ko ba kome yau sun tako sun ga tushen ta inda Mahaifiyar ta ta taso gidan wanda yake matsayin Mahaifi a wajen su , sun kuma san cewa ita ba walaƙantatciya bace har irin yadda suke zato tare da yin iƙirari , daidai gwargawdo Prof ya zama inuwar fakewar su .
" shiga wankan maza ki fito na shirya ki kin ji ko ?
Amnee ta sake cewa hakan lokacin da Khaalty Rahima ta juya tana barin É—akin .
Da taimakon Hasken da yake falon tar kamar rana Siyama ta ɗora ganin ta akan Falmata wacce tun kafin ƙarasowar ta wajen ƙamshin sassanyan turaren wutan da Amnee ta turare ta da shi iri daban-daban da kuma humra ya ratsa ƙofofin hancin su .
'yar ƙibar da tayi bai sa takun tafiyar ta mai kyau sauyawa ba , tana shirye cikin turarriyar koriyar lafaya mai adon manyan furanni launin jaa mai duhu , da ta naɗa ta akan wata doguwar rigar atamfa mai launin kore mai haske tayi ɗaurin ɗankwali sassauƙa fuskar ta babu wata kwalliya sai ɗan kunnen ta dogo ruwan silver da ya amshi 'yar zagayyar fuskar ta mai ƙaramin kyau .
fuskar ta ɗauke da 'yar madaidaiciyar fara'a ta ƙaraso .
Yanzu ne ta ga Fatima-zahra sosai , sai dai bata hango abu guda da ya razana ta game da ita ba da ya wuce yarintar ta , ko ba a faɗa mata ba ta ga alamu da dama a bayyane yarinya ce ɗanya da bata wuce shekaru goma sha tara zuwa ishirin ba da in kuwa hakane a kiyaste zata iya girme mata da shekaru aƙalla takwas zuwa tara , ba shakka tauraruwar ta zata daɗe tana haskawa .
Murmushi tayi lokacin da take miƙewa , kafin falmata ta ƙarasa durkuson da take shirin yi ta ɗago ta , ɗago kan ta Falmata tayi suka yi musayar kallo kowaccen su da taƙaitatcen murmushi akan fuskar ta ,
" Kul ki daina yawan durƙuso ƙamna ta , so kike ki yiwa ɗiyan mu lahani ? Ƙaraso ki zamna ni na amshi durƙuson na gaishe da yayun mu ,
Hannun ta ta jaa suka ƙarasa kujerar da ta taso daga kai , maimakon Falmata ta zauna akan kujerar da take mata nuni sai ta zauna a ƙasa ta shiga gaishe da Ammi da Asma'u da suke bin su da kallo , suka amsa mata kamar ɗazu a taƙaice suka ɗora da tambayar ta lafiyar jikin ta ? Murmushi tayi bata amsa ba .
Karɓa irin ta girma da girmamawa ita iyalan Maimartaba suka samu daga wajen Prof da nasa iyalan , duk kuwa da cewa ba'a san da zuwansu ba , hakan bai hana a shiga hidima da su ba ka'in da na'in babu ƙyashi Prof ya buɗe bakin Aljihu aka shiga hidima da su kamar daman can an san da zuwan su dan haka basu tarar da gidan tare da wata alama ta ƙasƙanci ba .
Gidan Attajiri suka tarar da ya matuƙar birge su a matsayin gidan su Matar da Youssoufa yake aure , duk sai jikin Ammi da Asma'u '( yar Hajiya Mama ) yayi sanyi da daman su biyun ne suka zo da wata manufa ta daban , sai suka ga ko su sai dai su gwadawa gidan su Falmata sarauta amma ba dai su ƙasƙantar da su ba . ( Daman Bare-bari ai ba daganan ba indai fagen bajinta ne ) .
Tunda Falmata ta shige ɗaki bata fito ba a ciki tayi sallar ta ta magarib da isha'i ta hau gado ta lulluɓu bayan ta kashe wutar ɗakin , ta rasa takamaimai halin da zuciyar ta take ciki , farin-ciki ne ko saɓanin sa ?
"watau sai yau ya waiwayo ta ? Bayan yasan ya mata laifi , yasan cewa dole tana jiran sa , yasan kuma a halin da take ciki da halin da ta baro wajen sa a ciki .
Can ƙasan ranta kuwa , So take ta ji ko da tashin ƙamshin sa ko kuwa amon muryar sa dan ta san cewa ya zo amma ko alama bata ji ɗuriyar sa ba a gidan .
Sai juye-juye take yi akan gadon , juyi ta sake yi lokacin da taji an turo ƙofar an shigo gami da kunna wutar ɗakin haske ya gauraya da sauri ta miƙe zaune bayan ta yaye mayafin da ta rufu da shi ,
Khaalty Rahima ta gani a tsaye a bakin ƙofa , daga inda take tana iya hango ɓacin ran da yake shimfiɗe kan fuskar ta ,
" Mama sannu da shigowa .
Khaalty Rahima bata amsa ba sai da ta ƙaraso kusa da ita , sannan tace " me kike a ɗaki ke kaɗai ? Kina sane da baƙin da suke gidan nan domin ki suka zo , "yan uwan mijin ki ne na jini , wai me yake damun ki ne ? Aina kika koyo wannan mugun halin na walaƙanta mutane ?
A ɗan tsorace Falmata tace , kiyi haƙuri Maman mu , un daman ai naga Yakaka tana wajen su suna hira .
Daƙuwa Khaalty Rahima tayi mata da hannuwanta duk biyu , " kin ci gidan ku Falmata, dangin Mijin Yakaka ne ko naki ? To bari na faɗa miki gara tun wuri kiyi watsi da wannan banzan halin ki daina dan kuwa ba inda zai kai ki , Mijin ki ɗan Manyan mutane ne gaba da baya ɗan sarauta ne shi da 'yan uwan sa halin girma da girmamawa cikin sa suka taso , shi aka saba gwada musu , muddin kika ce zaki je musu da saɓanin sa ke ce za ki sha wahala kiyi baƙin jini a wajen su ba ke ba har ya'yan da zaki haifa musu .
Shigowar Amnee bai sa Khaalty Rahima ta tsagaita ba ta cigaba da cewa , " ki tashi ki shirya ki fito kije ki gaishe su da kyau da kyau biyu daga ciki yayun mijin ki ne ɗaya kuma ƙanwar sa ce ƙaramar su , ɗayar kuwa kishiyar ki ce nasan ba zaki gagara sanin cewa 'yar uwar sa bace da suke 'ya'yan Mace da Namiji dan haka gara ki nutsu kiyi hankali ki daina wannan futsancin naki da tsagerancin wofi ,idan ba ma Allah yayi ba ina ke ina su ?
Unm, unm , unm Rahima banda gori kuma , ai shi arziƙi da ɗaukaka na Allah ne , amma 'yata ke ma baki kyauta ba baƙon ka ai abun girmamawa yake a wajen ka , bare kuma waɗannan da suke tafe tun daga wata ƙasa musamman domin tafiya dake , ki shirya kije ku gaisa har can falon Baa Alaji za'a raka ki akwai Manyan mutane da suka zo tare ɗaya daga cikin su Baffan Maigidan ki ne kuma shine waziri garin su sai kuma wasu manya daga wajen su dan haka kiyi shiga ta kamala sosai ko na shirya ki ?
Sai a lokacin Falmata ta ɗago kanta da hakan ya bawa ƙwallar idanun ta da suka taru damar zubowa faɗan da Khaalty Rahima ta mata ya haɗu mata da tasowar miƙin irin cin mutuncin da 'yan uwan Youssoufa suka masu a Niamey da yana daga cikin dalilan da yasa ta bar shi wutsiya a zage.
Muryar ta na rawa tace " Maman mu da Amnee ku yi haƙuri ku yafe min , amma ni bazan koma ba.
Kallon da suka bita da shi bai sa ta tsaya ba cikin kuka ta cigaba da cewa
" 'yan uwan sa basa sona zagin mu suka dunga yi suna min gori har iyayena suka aibata sun ce É—an uwan su ya sake ni me zai yi da ni 'yar gudun Hijira 'yar matsiyata Mama har cewa suka yi ...
" Khalass Amnee tace tana zama a gefen ta ta riko ta zuwa jikin ta , kukan da take yi ya taɓa ran su sun kuma fahimce ta , daman Khaalty Rahima ta riga ta san akwai wani dalilin da yasa falmata ta yi mu su yadda tayi , tasan halin 'yar ta Falmata mutum ce mai zuciya da gudun raini , ko kusa bata yadda a taka ta ba tare da ta rama ba .
Amnee ta cigaba da cewa
"Ko ma me suka ce miki ai ga su dai yanzu iyayen su sun taso su da aiken zuwa su koma da ke cikin girmamawa saboda kin riga kin zama wata ɓangare na jikin su , kiyi haƙuri ɗaukaka bata zuwa a sauƙaƙe , sai an zage damtse an ware ƙwanji wajen neman ta an kuma haɗa da haƙuri da juriya , wa ya faɗa miki inda samun ɗaukakar ka yake zai kasance kewaye da masoyan ka ? Ai ɗaukaka mai tasiri ita ce wacce aka ratsa tsakanin maƙiya wajen samun ta .
" ki zama jaruma Fatima-zara gidan sarauta kike aure , Yarima kike aure watarana idan da rai Matar sarki za ki zama dan haka saurin fushi ai ba naki bane .
"Sau da dama akwai wuraren da fushi baya yin tasiri sai fa saɓanin sa watau kwantar da kai da kawaici , hannun da ya juri miƙo maka gorar duma kana shan ruwan ciki da ɗaci , sannu kan hankali watarana shi zai miƙo maka gorar zuma tattaciya ka kwankwaɗa daga zaƙin ta , muddin kayi haƙuri saboda kome na duniya ɗan haƙuri ne kiyi haƙuri ki maida kome ba kome ba , kin ji ko ?
Gyaɗa kai tayi tana share hawayen ta , zuciyar ta taji tana sanyaya daga ɗacin da ya cunkushe mata rai , ko ba kome yau sun tako sun ga tushen ta inda Mahaifiyar ta ta taso gidan wanda yake matsayin Mahaifi a wajen su , sun kuma san cewa ita ba walaƙantatciya bace har irin yadda suke zato tare da yin iƙirari , daidai gwargawdo Prof ya zama inuwar fakewar su .
" shiga wankan maza ki fito na shirya ki kin ji ko ?
Amnee ta sake cewa hakan lokacin da Khaalty Rahima ta juya tana barin É—akin .
Da taimakon Hasken da yake falon tar kamar rana Siyama ta ɗora ganin ta akan Falmata wacce tun kafin ƙarasowar ta wajen ƙamshin sassanyan turaren wutan da Amnee ta turare ta da shi iri daban-daban da kuma humra ya ratsa ƙofofin hancin su .
'yar ƙibar da tayi bai sa takun tafiyar ta mai kyau sauyawa ba , tana shirye cikin turarriyar koriyar lafaya mai adon manyan furanni launin jaa mai duhu , da ta naɗa ta akan wata doguwar rigar atamfa mai launin kore mai haske tayi ɗaurin ɗankwali sassauƙa fuskar ta babu wata kwalliya sai ɗan kunnen ta dogo ruwan silver da ya amshi 'yar zagayyar fuskar ta mai ƙaramin kyau .
fuskar ta ɗauke da 'yar madaidaiciyar fara'a ta ƙaraso .
Yanzu ne ta ga Fatima-zahra sosai , sai dai bata hango abu guda da ya razana ta game da ita ba da ya wuce yarintar ta , ko ba a faɗa mata ba ta ga alamu da dama a bayyane yarinya ce ɗanya da bata wuce shekaru goma sha tara zuwa ishirin ba da in kuwa hakane a kiyaste zata iya girme mata da shekaru aƙalla takwas zuwa tara , ba shakka tauraruwar ta zata daɗe tana haskawa .
Murmushi tayi lokacin da take miƙewa , kafin falmata ta ƙarasa durkuson da take shirin yi ta ɗago ta , ɗago kan ta Falmata tayi suka yi musayar kallo kowaccen su da taƙaitatcen murmushi akan fuskar ta ,
" Kul ki daina yawan durƙuso ƙamna ta , so kike ki yiwa ɗiyan mu lahani ? Ƙaraso ki zamna ni na amshi durƙuson na gaishe da yayun mu ,
Hannun ta ta jaa suka ƙarasa kujerar da ta taso daga kai , maimakon Falmata ta zauna akan kujerar da take mata nuni sai ta zauna a ƙasa ta shiga gaishe da Ammi da Asma'u da suke bin su da kallo , suka amsa mata kamar ɗazu a taƙaice suka ɗora da tambayar ta lafiyar jikin ta ? Murmushi tayi bata amsa ba .