← Book details Mafari Hargitsin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 237 OF 269

Sashe 237

Mafari Hargitsin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

A ƙarshe ba yadda maimartaba ya iya ganin yadda ɗan nasa ya zama yasa ya masa umarnin tafiya bayan ya masa nasiha akan haƙuri da mallakar zuciyar a duk lokacin da rai ya ɓaci sannan ya gargaɗe shi da gujewa ɗaukar mataki cikin fushi .

Ƙarfe goma na ranar jirgi ya ɗaga da shi da Bilal da zai masa rakiya zuwa Niamey .

Bayan tafiyar Youssouf Hajiya Mama ta ƙira Hafsatouwa ta umarce da cewa gobe da sassafe ta kama hanyar Zurun Jahar kebbin Nigeria bayan ta danƙa mata isassun kuɗin da zasu ishe ta .

Duk da cewa Falmata baƙuwa ce a masarauta Maraɗi amma hakan bai hana masarautar ta zama cikin alhini ba kasantuwar ta riga ta zama wani ɓangare na gidan , ko'ina ka ratsa za ka ji bayun gidan suna batun ɓacewar Gimbiya Fatima da cikin jikin ta .

Hajiya Umma da kan ta ta shiga damuwa musamman da ya zama Maimartaba yana ganin har da sakacin ta wajen ɓatan Falmata da har a jiya da dare ya tabbatar mata da hakan cikin fushi .

Hajja kuwa ƙurewar tashin hankali ta shiga tayi kuka har ta bawa aku lada ta haƙura ta rungumi charbi tana addu'ar Allah ya baiyana mata uwarɗakin ta a halin lafiya .

Niamey .

Lokacin da Youssouf ya isa Niamey daga airport kai tsaye babban ofishin 'yan sanda ya nufa inda har lokacin ake cigaba da tsare Mammadou da Maimounatou sakamakon rashin sanin halin da shi yake ciki da hakan ya kawo jinkirin miƙa su kotu a musu hukunci .

Bayan ya cike takardu aka masa iznin ganin su da Mammadou ya nemi ganawa a farko .

Lokacin da aka fito da Mammadou , Youssouf da yake zaune bai san lokacin da ya miƙe ba da sauri ya taka ya taro Mammadou da yake tangaɗi , ba tare da ya damu da tsami da warin da yake tashi daga jikin Mammadoun ba ya kama shi suka zauna .

Da wani irin yanayi a fuskar sa mai tsauri yace "Mammadou ƙaƙa ka zama hakka ? Shin baka da lafiya ne ? Ko kouwa horo ake maka ?

Mammadou da zuciyar sa ta cika taf da farin-cikin ganin Youssouf ya riƙo hannuwan sa duk biyu kafin ya fashe da matsanancin kuka cikin kukan yake cewa "Youssoufa kai min gafara , ka yafe min ɗan ouwana na tuba ka yafe min , nayi nadama marar amfani na kouma yi tir da muguwar uwa irin tawa tare da.....

Da sauri Youssouf ya katse shi yana cewa "Mammadou kar ka tsawaita zance domin ba shi da wani amfani dan kouwa ba zai yi gyara cikin abun da ya wouce ba kouma zouwa ma nayi mu tai gida tare nan ba wajen yin zance bane Mammadou .

Cikin wani irin sauti Mammadou yace "da gaske Youssoufa zowa kayi ka tafi da ni gida ?

Miƙewa Youssouf yayi yana zube hannuwan sa cikin aljihu ya fara taku yana barin wajen ƙarƙashin rakiyar idanun Mammadou da ya bi shi da kallo sai da ya kai ƙofar ficewa daga wajen bai jiyo ba yace "ƙwarai yau kake kwana a gida Mammadou .

Daga haka ya fita yana jin yadda tattaurar zuciyar sa ke son tasowa ta hana shi duk wani afuwa da sassauci da yayi niyyar yi ga É—an uwan nasa .

Ya juya baya ga ƙofar shigowa lokacin da aka taso ƙeyar Maimounatou ta shigo inda yake idanun ta da suka shige ciki ta ware tana kallon sa a take ta shaida ko wanene a gaban ta , sannan 'yar murna da ta fara safko mata jin cewa an zo ganin ta ta koma ciki fargaba mai girma ya mamaye ta da yasa har wasu siraran gumi suka fara tsiyaya ta cikin rigar ta .

cikin raggon taku ta nufi inda yake sai dai kafin ta ƙarasa ya juyo baki ɗayan sa yayi tsaye ƙem a gaban ta da juyowar sa tayi hanzarin sauƙe idanun ta ƙasa tana jin wani yanayi da ta gagara tantance a wanne matsayi zata ajiye shi "kunya ce ? "Nadama ce ? Ko kuwa tsoro ne ?

Bata ankara ba ta gan shi daf da ita kamar an tunkuɗo shi hannuwan sa zube cikin aljihun wondon sa da sautin sa mai amo da ya sake kaurarara yace "Madame, êtes-vous surprises ?

Wani murmushin yaƙe Maimounatou tayi da ya taho da ɗoyin da bakin ta ke yi , ta ɗago kan ta ta saci kallon sa kafin ta wani karya kai gefe ɗaya cikin muryar da ta saba hilatar sa da shi wacce yau ta sake matsewa tace "Pas vraiment, tu ne m'as pas surpris, je sais que tu reviendras vers moi.
Hannun ta ta miƙa da nufin taɓa shi ya jaa baya da sauri yana kokuwa da ɓacin ran sa da idanun sa da suka yi jaa ya mata wani kallon gargaɗi da ya kaɗa mata ciki .

Da baya-baya ya dangana da kan kujerar da take gaban ɗan teburin da yake cikin ɗakin ya zauna yana harɗe ƙafafun sa ɗayan kan ɗaya yace.

" idan kin ka yi tounanin kina da watta sauran dama guda da ta rage miki a gareni kin yaudari kan ki yau ba rana ce ta wassa ba don haka Arrêtez de jouer avec votre propre cœur et de vous dupe.

Wani murmushin ta sake yi kafin ta yi ɗan taku kaɗan tana juya baya ga barin fuskantar sa cikin ƙarfin hali tace " Bana neman watta dama dagga gare ka a yanzou sabbada kuwa duk watta dama na riga na same ta har ma......

Tsawar da ya yi haÉ—i da buga teburin gaban sa shi yasa ta juyowa a firgice , a tsaye ta gan shi fuskar sa da ta duba a lokacin ji tayi marar ta ta cika fam.

Ya matso daf da ita yana nuna ta da yatsan sa ya ce "kadda ki min wassa , ni damisa ne da ban juri wasa ba ban ɗauki wargin mazaje ba a fagen daga na sanya bakin bindiga na fasa ƙoƙon kan su na sa ƙafafu na taka cikin su kar kiyi zaton zan miki sassauci ,

hannun sa ɗaya da yake cikin aljihun sa ya zaro da yake riƙe da ƙaramar bindiga , yayi taku kaɗan zuwa baya kafin ya cigaba da cewa "zan iya tarwatsa kan ki da harsashi bayan na tattaka ki muddin kin ka cigaba da min fi'ili .

Kafin ya mayar da numfashi Maimounatou ta zube akan guiwowin ta ta haɗa tafukan ta biyo tana sakin wani mitsi-tsin kuka mai tafe da sautin tsoran da ruhin ta ke ciki tace jikin ta na ƙyarma tace ,

" Dan Allah kayi haƙuri kar ka kashe ni , wallahi sharrin shaiɗan ne ya sa na aikata abun da na maka ka yafe min .

Wani guntun murmushi Yayi kafin tace
"Ashe kina tsoron Mutuwa ? Ni kuma kin ka nemi kashe ni ? Babu yafiya a tsakanina da ke ko afuwa ba zan iya miki ba muddin baki sanar dani dalilin da yasa kin ka nemi raina ba?

Da sauri Maimounatou tace "wallahi zan faÉ—i dalili .

Komawa yayi ya zauna yana ƙoƙarin sassauta fushin zuciyar sa yace "Vous avez seulement 30 minutes.

Kamar an kunna radio Maimounatou ta shiga ba shi labari tiryan-tiryan tana yi tana kallon sa tana karya wuya da sharar hawaye .

Bai katse ta ba har sai da ta kai ƙarshe

Kan sa a ƙasa yace "menene gaskiyar cewa da kika yi Mammadou ya kawo gubar da kin ka ciyar da ni ?

Girgiza kai tayi cikin ƙaramar murya tace .

"ba shi bane ni na aiki Gnala ta sayo min . sannan cikin kuka ta cigaba da cewa

"Amma wallahi nayi nadama iyakar nadama dan Allah ka min afouwa ka sake bani dama na gyara kuskurena wallahi wannan karon da dukkanin zuciya ta zan zauna da kai zan tallafi soyayyar da kake '.....

ÆŠago da kan sa da yake sunkuiye yayi yana É—an buga tafin hannun sa akan teburin gaban sa yayi wani murmushi mai ciwo .
"Soyayya ? Yanzu kina zaton har kawo yanzu akwai sauran ɗigon na alamar son ki a raina ? Bayan duk abun ƙi da kin ka wanzu wurin aikata shi a gareni..

Huci yayi yana danne ƙiyayyar ta da yake ji mai karfi tana naso a cikin ran sa daga lokacin da ta ambaci sunan Ghaddafi Yacouba Dango a matsayin mutumin da ta nemi kashe shi a kan sa bayan irin ha'intar sa da tayi ta dunga yaudarar sa da sunan soyayya har ya aure ta bayan sun gama tanbaɗewar su da wannan riƙaƙƙen ɗan ta'addan haƙiƙa Maimounatou guba ce ba domin yana yaƙar zuciyar sa da babu abunda zai hana ya harbe ta a lokacin .

Ya tsaya faɗa mata matsayin da take kai a wajen sa a yanzu tamkar ɓata lokaci ne ko kuwa bata wani matsayi na daban da ya wuce wanda takai kai yanzu a wajen sa dan haka ya mayar da ganin sa gefe daga kan fuskar ta da alokacin yake ganin ta da muni fiye da duk wani mummunan abu da ya taɓa cin karo da shi a tsawon rayuwar sa .

"Ina kin ka sa a ka kai Matata ?

A dabar-barce Maimounatou tace wacce matar ka ?

Taku ɗaya yayi ya miƙa hannu ya figo ta tayi zaman 'yan dabaro a gaban sa ya shaƙe wuyan ta kafin ya danna mata bakin bandiga akan ta wata irin razananniyar tsawa ya daka mata yana sake maimaita tambayar ta.

" Ina ki ka kai Fatima-zahra Mata ta nace ? Ki faÉ—a min ko na fasa kan ki .

Baki ɗayan jikin ta ɓari yake ta kasa magana saboda maƙogoron ta da ya shaƙe ya sa ta fara jin ƙamshin mutuwa .

Ta kai mintuna biyu a haka a shaƙe a hannun sa , sai da yayi da gaske tukun ya iya haƙura ya sassauta shaƙar da ya mata ya ingiza ta ta faɗi .

Kan sa ya sake sauƙewa ƙasa yana huci bai ɗago ba yace " za ki faɗa min ko kuwa na kashe ki ?

Tana wani irin kuka Maimounatou tace "wallahi Allah ɗaya kenan bani da watta masaniya kan ɓatan ta .
Chapter 237 · 0% Book details