Sashe 188
Mafari Hargitsin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da gudu Youssouf ya ƙarasa ya ratsa ta tsakankanin Likitocin da suke zagaye da ita , fuskokin su cike da Alhini ,
Ya tarairayo ta bayan ya zauna a bakin gadon ya ɗagota lokacin da take jaan wani irin numfashi mai tafe da gurnani ciki-ciki , idanunta a buɗe akan fuskar sa ,
Hannun sa ya kai yana goge mata tsinkakken yawun da yake zuba a bakin ta , muryar sa tana karkarwa yake kallon likitocin yana cewa,
" Doctora yaya hakka ? Kuyi wani abu mana , Mama tana hakka alhalin kuna tsaye ?
"Mama, kar ki barni ki dubeni Mama ,
ya ƙira ta da wata irin muryar yana jijjigata a jikinsa ganin yadda idanunta suka yi sama , numfashin da take kokawar riƙewa kuma ya ƙarasa barin jikinta , dukkanin wasu jijiyoyin jikinta suka tsayawa aiki , kamar yadda zuciyarta ta tsaya chak daga barin bugawa na har abada .
Da gudu Yakaka ta ratsa tsakanin su ta kai hannu tana riƙo hannun Mama da yayi wani irin sanyi ƙalau ya sake ,
"Mama tashi mana , me ya same ki haka ? Innalillahi wa inna ilaihi raji'oon .
 Tace da kuka a muryar ta ,
"Mama ,
Falmata ma ta ƙira ta lokacin da ta ƙaraso gurin idanunta basa gani sosai Amma tabbas a yau tana iya hange gefen Fuskar Mama tar-tar , shafa kanta tayi da yake rungume a kirjin Babanta
"Mama meye ya same ki ? Ki tashi Mama , kin ga fa Mamar ki ta asali ta dawo zata rayu da ke , Mama baki ko mata magana ba , bata ji muryar ki ba shine kuma za ki zama haka ? Mama ki tashi ,
Ta ƙarasa maganar tana jijjiga su ita da Youssouf ,
KafaÉ—ar Youssouf Babban likitan ya dafa , yana cewa
" Innalillahi wa inna ilahi raji'oon , kuyi hakuri duk wani ciwo na safiyya ya warke , ta komawa ga Ubangijinta , dukkan wani mai rai mamaci ne kuyi haƙuri , kuyi haƙuri , kuyi addu'a
Baya yayi a hankali yana kaucewa ganin tashin hankalin da yake ƙwarar idanun su su ukun ,da suke kallon sa zuciyar sa cike da tsantsar tausayi , tabbas mutuwar abunda ka haifa akwai ciwo , ciwo kuwa mai raɗaɗin gaske , ɗaya bayan ɗaya likitocin suke ficewa daga ɗakin suka bar guda biyu kawai a tsaye ,
Jikin Youssouf babu inda baya rawa , ya zaro Mama daga ƙirjinsa yana kallon fuskar ta yadda kan ta ya tafi galau ,
Ya sa kukan da yake riƙewa fisge masa , sai ya fashe da kuka mai ƙarfi ya mayar da ita ƙirjin sa da yake wani irin bugu da matsewa tamkar ana daure masa jijiyoyin dake gudanar da jini ta cikin sa ,
amon kukansa ya sa Hajja shigowa É—akin , cikin ranta tana aiyana inda ake gudu nan aka zo aka tsaya , Mama ta rasu ,
Tun-tuni ta ga Alamun mutuwa a tare da yarinyar tunda jikin ya birkice daman ranta yake kai-kawo , Allah sarki mutuwa bata a shekaru , bata barin ƙarami ta ɗau babba domin wai ta jinkirtawa girman sa , ita lokaci kawai take jira , ko ɗan da yake cikin mahaifiyar sa tana ɗauka ,
Falmata wacce hankalinta ya kasa amincewa da mutuwar Mama kamar yadda likita ya faɗa , ƙarasawa tayi ga Yakaka wacce ta zube guiwar ta biyu a ƙasa ta kifa tafukanta biyu akan fuskarta , kuka take marar sauti , illahirin jikinta rawa yake sai ta kai hannu ta dafa ta , a lokacin da Hajja ta nufi wajen Youssouf , da muryar dake bayyana tsoro da tashin hankalin da me ita yake ciki tace ,
"Yakaka , ki tashi , ki tashi ki karɓi Mama mu tafi , mu tafi da ita Yakaka , ko kin manta da Alƙawarin da muka mata tun tana ciki ? Cewa ni da ke zamu kula da ita Yakaka , zamu bata kariya yaya kuma kina gani Mama zata tafi ta bar mu , ?
Alhalin ...Ya.Yakaka ki tashi nace kin san fa mu uku ne kaɗai a duniya Dan Allah kar Mama ta mutu , Mama kar ki barni mana , yaya za ki min haka Mama ? Bayan nayi alƙawarin zaki warke Mama .
Kuka ne ya ci ƙarfin ta har tana shiɗewa numfashinta ya fara yin sama-sama
Da sauri Yakaka ta rungumeta kukan ta yana daɗuwa ta riƙe fuskar ta ,
"Falmata kiyi addu'a , kice innalillahi wa inna ilahi raji'oon , mu da Mama duk Allah ne ya yimu , ya bamu rai da muke rayuwa da shi , kuma shine ya hallicci mutuwa ya sa ta zama mai zare rayukan mu idan lokacin da ya kayyade mana na rabuwar mu da ruhin mu yayi , da ni da ke da Baban ta duk Allah ya fi mu sonta kiyi mata Addu'a Falmata ,
Da ƙarfi Falmata ta rungume Yakaka wacce ƙarfin hali ne kawai take yi domin kadda Falmata tayi rauni dayawa ,ita abunda take ji bata taɓa jin makamancin sa ba wani abu take ji mai ɗaci yana kai kawo a tsakanin zuciya da maƙogoron ta , gaba ɗaya ranta cike yake da duhu da take iya ganin duhun har ga idanunta ,
Hajja tana ƙarasawa ga Youssouf ta shiga bada baki da tunasarwar da ake yiwa wanda aka yiwa mutuwa , itama sharar hawaye take zuciyarta cike da tausayin su , tana kimanta irin zogin da zuciyoyinsu ke ciki kan mutuwar ɗiyar su ,
Sun É—au mintoci kusan goma a haka cikin halin É—imuwar jin zafin mutuwa kafin likitocin biyu su nemi da ya basu Mama zasu zare duk na'urorin su da suka riga suka jona mata ,
Bai dube su ba kamar yadda bai ce kome ba illa bakin sa da tun-tuni yake motsawa da alamun addu'a yake yiwa Æ´ar sa ,
Shi da kan sa ya raba jikinta da duk wasu na'urorin su ba tare da ya ajiye gawar ta ba ya jaa farin mayafin su na asibitin ya rufe fuskarta zuwa jikinta da shi , bayan ya shafe fuskarta da tafin hannun sa .
Cigaba yayi da zama a wajen yana riƙe da ita tamkar wanda ya samu ɗaukewar tunani .
Ganin haka ya sa likitocin da suka rage su biyu suka fita , Hajja ta ƙarasa wajen su Yakaka tana ba su baki , da har yanzu basu bar kuka ba .
Turo ƙofar aka yi Tafeeda ya shigo tare da shi dattijo ne wanda yana sanya ƙafa a ɗakin ƙamshinsa ya gauraye ɗakin da ya sa Youssouf ɗago kansa suka haɗa ido ,
Maimartaba Sarkin Maraɗi Abdoul-azizou Baskore , ya taka ya ƙarasa gaban gadon da Youssouf yake zaune riƙe da Gawar ƴar sa ,
"Youssoufa ,
Ya ƙira sunan sa .
Ɗago da kansa yayi a karo na biyu , laɓɓan bakin sa na karkarwa da kyar ya fisgo kalmomin da a tun farkon samuwar Mama yake tsoron Furta su ga Maimartaba a tsa-tsan idanun sa , a yau neman tsoron ya yi ya rasa a lokacin da Mama ta ƙare ta zama Babu .
" Baaba , É—iyata ce , wannan Mama ce , É—iyata ce , ta rasu , Mama ta rasu ta barni Baaba .
Kuka ya sake fashewa da shi idanun sa na zubar hawayen da suke É—iga akan gawar Mama ,
Maimartaba sai ya zare gilashin idanun sa , da bayyanuwar sabon yanayi akan fuskar sa saɓanin wanda ya shigo da shi ,
Yayi tsumu ! yana kallon Youssouf da yake cigaba da kuka marar sauti , zuciyarsa ce ta rau-rawa saboda dalilai biyu da suka haÉ—e mar a lokaci guda .
a hankali ya kai hannu ya dafa ƙafaɗar Youssouf ɗin, cike da tausasawa a muryar sa mai ƙwarjini yace ,
"Youssoufa kayi haƙuri dukkanin mai rai Mamaci yake , Rayukan mu kuma ababen aro ne a gare mu da babu shakka masu komawa ne ga Ubangijin da ya bamu aron su a domin mu bauta masa , Ka dogara ga Ubangiji da zuciya ɗaya, kada ka dogara ga abin da kake tsammani ka sani , a cikin dukan abin da kake yi, ka tuna da Ubangiji, shi kuma zai nuna maka hanyar da yake daidai , Sam, kada ka yarda ka ɗauki kanka kai mai hikima ne fiye da yadda kake, kai dai ka ji tsoron Ubangiji, ka rabu da aikata saɓo , Idan ka kiyaye wannan, zai zamar maka kamar magani mai kyau, ya warkar da raunukanka, ya kuma sawwaƙe maka azabar da kake ciki ,
"Miƙata ga Tafeeda ka taso mu tafi ga yi mata sutura zuwa miƙata ga kabarinta ,Allah ya jiƙanta , Allah shi sa ta zama dalilin samun afouwar Ubangiji a gareka .
Kalaman Maimartaba sunyi tasiri ga duhuntatciyar zuciyar sa mai ciwo , dan haka sai ya sasssuta riƙon da yayi wa gawar Mama , ya miƙata ga Tafeeda zuciyar sa na tuno masa rana ta farko da ya fara karɓar ta da tafukansa , ya rungumeta a ƙirjinsa , sai ga shi a yau ya zareta daga jikinsa da hannunsa , zarewa irin ta har Abada , ji yayi tamkar bazai iya ba , tamkar wani sashi na ransa ne ya bar jikinsa .
A hankali Tafeeda ya samu damar zareta daga jikinsa , wanda shima tasa zuciyar tayi laushi tausayin Youssouf ɗin ya cika zuciyar sa tare da ƙarin tsoron Allah , da ya tuna irin ƙauna da tsantsar son da Youssouf yake yiwa wannan ɗiyar , da har ta kai ya zaɓe ta bisa ga kowa da kome nashi , duk a domin ya rayu tare da ita .,
Sai ga shi domin Ubangiji ya yi masa babbar jarabawa sai ya sanya mutuwa ta raba tsakanin su , a kuma lokacin da kome ya rinchaɓe masa a dalilinta , lalle wannan jarabawa ce maigirma ,
Mayafin da aka rufe mata fuska da shi ya buÉ—e lokacin da yake É—aga ta , Maimartaba ya dubi fuskarta da tsantsar tausayi cike a ransa ,
"Ubangiji yasa ki zamto dagga Æ´a'Æ´an da zasu zam silar samun afouwar Allah ga iyayen su daga tarin zunuba su ,
"Amin Amin Amin,
Hajja ta amsa tana sharar ƙwalla ,
Ya tarairayo ta bayan ya zauna a bakin gadon ya ɗagota lokacin da take jaan wani irin numfashi mai tafe da gurnani ciki-ciki , idanunta a buɗe akan fuskar sa ,
Hannun sa ya kai yana goge mata tsinkakken yawun da yake zuba a bakin ta , muryar sa tana karkarwa yake kallon likitocin yana cewa,
" Doctora yaya hakka ? Kuyi wani abu mana , Mama tana hakka alhalin kuna tsaye ?
"Mama, kar ki barni ki dubeni Mama ,
ya ƙira ta da wata irin muryar yana jijjigata a jikinsa ganin yadda idanunta suka yi sama , numfashin da take kokawar riƙewa kuma ya ƙarasa barin jikinta , dukkanin wasu jijiyoyin jikinta suka tsayawa aiki , kamar yadda zuciyarta ta tsaya chak daga barin bugawa na har abada .
Da gudu Yakaka ta ratsa tsakanin su ta kai hannu tana riƙo hannun Mama da yayi wani irin sanyi ƙalau ya sake ,
"Mama tashi mana , me ya same ki haka ? Innalillahi wa inna ilaihi raji'oon .
 Tace da kuka a muryar ta ,
"Mama ,
Falmata ma ta ƙira ta lokacin da ta ƙaraso gurin idanunta basa gani sosai Amma tabbas a yau tana iya hange gefen Fuskar Mama tar-tar , shafa kanta tayi da yake rungume a kirjin Babanta
"Mama meye ya same ki ? Ki tashi Mama , kin ga fa Mamar ki ta asali ta dawo zata rayu da ke , Mama baki ko mata magana ba , bata ji muryar ki ba shine kuma za ki zama haka ? Mama ki tashi ,
Ta ƙarasa maganar tana jijjiga su ita da Youssouf ,
KafaÉ—ar Youssouf Babban likitan ya dafa , yana cewa
" Innalillahi wa inna ilahi raji'oon , kuyi hakuri duk wani ciwo na safiyya ya warke , ta komawa ga Ubangijinta , dukkan wani mai rai mamaci ne kuyi haƙuri , kuyi haƙuri , kuyi addu'a
Baya yayi a hankali yana kaucewa ganin tashin hankalin da yake ƙwarar idanun su su ukun ,da suke kallon sa zuciyar sa cike da tsantsar tausayi , tabbas mutuwar abunda ka haifa akwai ciwo , ciwo kuwa mai raɗaɗin gaske , ɗaya bayan ɗaya likitocin suke ficewa daga ɗakin suka bar guda biyu kawai a tsaye ,
Jikin Youssouf babu inda baya rawa , ya zaro Mama daga ƙirjinsa yana kallon fuskar ta yadda kan ta ya tafi galau ,
Ya sa kukan da yake riƙewa fisge masa , sai ya fashe da kuka mai ƙarfi ya mayar da ita ƙirjin sa da yake wani irin bugu da matsewa tamkar ana daure masa jijiyoyin dake gudanar da jini ta cikin sa ,
amon kukansa ya sa Hajja shigowa É—akin , cikin ranta tana aiyana inda ake gudu nan aka zo aka tsaya , Mama ta rasu ,
Tun-tuni ta ga Alamun mutuwa a tare da yarinyar tunda jikin ya birkice daman ranta yake kai-kawo , Allah sarki mutuwa bata a shekaru , bata barin ƙarami ta ɗau babba domin wai ta jinkirtawa girman sa , ita lokaci kawai take jira , ko ɗan da yake cikin mahaifiyar sa tana ɗauka ,
Falmata wacce hankalinta ya kasa amincewa da mutuwar Mama kamar yadda likita ya faɗa , ƙarasawa tayi ga Yakaka wacce ta zube guiwar ta biyu a ƙasa ta kifa tafukanta biyu akan fuskarta , kuka take marar sauti , illahirin jikinta rawa yake sai ta kai hannu ta dafa ta , a lokacin da Hajja ta nufi wajen Youssouf , da muryar dake bayyana tsoro da tashin hankalin da me ita yake ciki tace ,
"Yakaka , ki tashi , ki tashi ki karɓi Mama mu tafi , mu tafi da ita Yakaka , ko kin manta da Alƙawarin da muka mata tun tana ciki ? Cewa ni da ke zamu kula da ita Yakaka , zamu bata kariya yaya kuma kina gani Mama zata tafi ta bar mu , ?
Alhalin ...Ya.Yakaka ki tashi nace kin san fa mu uku ne kaɗai a duniya Dan Allah kar Mama ta mutu , Mama kar ki barni mana , yaya za ki min haka Mama ? Bayan nayi alƙawarin zaki warke Mama .
Kuka ne ya ci ƙarfin ta har tana shiɗewa numfashinta ya fara yin sama-sama
Da sauri Yakaka ta rungumeta kukan ta yana daɗuwa ta riƙe fuskar ta ,
"Falmata kiyi addu'a , kice innalillahi wa inna ilahi raji'oon , mu da Mama duk Allah ne ya yimu , ya bamu rai da muke rayuwa da shi , kuma shine ya hallicci mutuwa ya sa ta zama mai zare rayukan mu idan lokacin da ya kayyade mana na rabuwar mu da ruhin mu yayi , da ni da ke da Baban ta duk Allah ya fi mu sonta kiyi mata Addu'a Falmata ,
Da ƙarfi Falmata ta rungume Yakaka wacce ƙarfin hali ne kawai take yi domin kadda Falmata tayi rauni dayawa ,ita abunda take ji bata taɓa jin makamancin sa ba wani abu take ji mai ɗaci yana kai kawo a tsakanin zuciya da maƙogoron ta , gaba ɗaya ranta cike yake da duhu da take iya ganin duhun har ga idanunta ,
Hajja tana ƙarasawa ga Youssouf ta shiga bada baki da tunasarwar da ake yiwa wanda aka yiwa mutuwa , itama sharar hawaye take zuciyarta cike da tausayin su , tana kimanta irin zogin da zuciyoyinsu ke ciki kan mutuwar ɗiyar su ,
Sun É—au mintoci kusan goma a haka cikin halin É—imuwar jin zafin mutuwa kafin likitocin biyu su nemi da ya basu Mama zasu zare duk na'urorin su da suka riga suka jona mata ,
Bai dube su ba kamar yadda bai ce kome ba illa bakin sa da tun-tuni yake motsawa da alamun addu'a yake yiwa Æ´ar sa ,
Shi da kan sa ya raba jikinta da duk wasu na'urorin su ba tare da ya ajiye gawar ta ba ya jaa farin mayafin su na asibitin ya rufe fuskarta zuwa jikinta da shi , bayan ya shafe fuskarta da tafin hannun sa .
Cigaba yayi da zama a wajen yana riƙe da ita tamkar wanda ya samu ɗaukewar tunani .
Ganin haka ya sa likitocin da suka rage su biyu suka fita , Hajja ta ƙarasa wajen su Yakaka tana ba su baki , da har yanzu basu bar kuka ba .
Turo ƙofar aka yi Tafeeda ya shigo tare da shi dattijo ne wanda yana sanya ƙafa a ɗakin ƙamshinsa ya gauraye ɗakin da ya sa Youssouf ɗago kansa suka haɗa ido ,
Maimartaba Sarkin Maraɗi Abdoul-azizou Baskore , ya taka ya ƙarasa gaban gadon da Youssouf yake zaune riƙe da Gawar ƴar sa ,
"Youssoufa ,
Ya ƙira sunan sa .
Ɗago da kansa yayi a karo na biyu , laɓɓan bakin sa na karkarwa da kyar ya fisgo kalmomin da a tun farkon samuwar Mama yake tsoron Furta su ga Maimartaba a tsa-tsan idanun sa , a yau neman tsoron ya yi ya rasa a lokacin da Mama ta ƙare ta zama Babu .
" Baaba , É—iyata ce , wannan Mama ce , É—iyata ce , ta rasu , Mama ta rasu ta barni Baaba .
Kuka ya sake fashewa da shi idanun sa na zubar hawayen da suke É—iga akan gawar Mama ,
Maimartaba sai ya zare gilashin idanun sa , da bayyanuwar sabon yanayi akan fuskar sa saɓanin wanda ya shigo da shi ,
Yayi tsumu ! yana kallon Youssouf da yake cigaba da kuka marar sauti , zuciyarsa ce ta rau-rawa saboda dalilai biyu da suka haÉ—e mar a lokaci guda .
a hankali ya kai hannu ya dafa ƙafaɗar Youssouf ɗin, cike da tausasawa a muryar sa mai ƙwarjini yace ,
"Youssoufa kayi haƙuri dukkanin mai rai Mamaci yake , Rayukan mu kuma ababen aro ne a gare mu da babu shakka masu komawa ne ga Ubangijin da ya bamu aron su a domin mu bauta masa , Ka dogara ga Ubangiji da zuciya ɗaya, kada ka dogara ga abin da kake tsammani ka sani , a cikin dukan abin da kake yi, ka tuna da Ubangiji, shi kuma zai nuna maka hanyar da yake daidai , Sam, kada ka yarda ka ɗauki kanka kai mai hikima ne fiye da yadda kake, kai dai ka ji tsoron Ubangiji, ka rabu da aikata saɓo , Idan ka kiyaye wannan, zai zamar maka kamar magani mai kyau, ya warkar da raunukanka, ya kuma sawwaƙe maka azabar da kake ciki ,
"Miƙata ga Tafeeda ka taso mu tafi ga yi mata sutura zuwa miƙata ga kabarinta ,Allah ya jiƙanta , Allah shi sa ta zama dalilin samun afouwar Ubangiji a gareka .
Kalaman Maimartaba sunyi tasiri ga duhuntatciyar zuciyar sa mai ciwo , dan haka sai ya sasssuta riƙon da yayi wa gawar Mama , ya miƙata ga Tafeeda zuciyar sa na tuno masa rana ta farko da ya fara karɓar ta da tafukansa , ya rungumeta a ƙirjinsa , sai ga shi a yau ya zareta daga jikinsa da hannunsa , zarewa irin ta har Abada , ji yayi tamkar bazai iya ba , tamkar wani sashi na ransa ne ya bar jikinsa .
A hankali Tafeeda ya samu damar zareta daga jikinsa , wanda shima tasa zuciyar tayi laushi tausayin Youssouf ɗin ya cika zuciyar sa tare da ƙarin tsoron Allah , da ya tuna irin ƙauna da tsantsar son da Youssouf yake yiwa wannan ɗiyar , da har ta kai ya zaɓe ta bisa ga kowa da kome nashi , duk a domin ya rayu tare da ita .,
Sai ga shi domin Ubangiji ya yi masa babbar jarabawa sai ya sanya mutuwa ta raba tsakanin su , a kuma lokacin da kome ya rinchaɓe masa a dalilinta , lalle wannan jarabawa ce maigirma ,
Mayafin da aka rufe mata fuska da shi ya buÉ—e lokacin da yake É—aga ta , Maimartaba ya dubi fuskarta da tsantsar tausayi cike a ransa ,
"Ubangiji yasa ki zamto dagga Æ´a'Æ´an da zasu zam silar samun afouwar Allah ga iyayen su daga tarin zunuba su ,
"Amin Amin Amin,
Hajja ta amsa tana sharar ƙwalla ,