Sashe 240
Mafari Hargitsin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ko Hajiya Umma bata taɓa zaton sharri da muguntar Hajiya Saratu , bayan irin mummunan asirin da ta yiwa ɗan ta har ya kai da zata iya enlevé surukar ta ?? Wacce irin ƙiyayya ce wannan Hajiya Mama take mata ?
Da hannu Hajiya Umma ta ƙira Ubbo da Siyama waɗan da suma suke tsaye kasaƙe kamar ruwa ya cinye su tace " ku kama ta zouwa sashi na .
Cikin sauri Youssouf ya girgiza kai kafin yace " zan tai da ita da kaina.
Gyaran murya Maimartaba yayi kafin yace
" bar su su tai da ita kai kouma ka biyo ni .
Daga haka ya juya bayu da sauran al'ummar gidan da har kawo yanzu babu wanda ya iya cewa ƙala wasu suka rufa masa baya .
Youssouf bai saki hannun Falmata ba duk da cewa tun da ta ji muryoyin mutane a wajen ta raba jikin ta daga na shi amma ya ƙi sakin hannun ta .
Har Sai da Hajiya Umma ta kama hannun Falmatan ɗaya ta rike sannan tace masa " ka tai ga ƙiran Mahaifin ka , itta tana ƙarƙashin kulawata .
A hankali ya miƙe yana waiwayen Falmata da ta sunkuyar da kan ta ya fita zuciyar sa cike da jin tausayin falmata da ya lura har rama tayi ta fita a kamannin ta duk wai a sanadin sa Hajiya Saratu ta mata haka ?
Ubbo da kan ta ta haÉ—awa Falmata ruwan wanka kamar yadda Hajiya Umma ta umarce ta ,
Hajja wacce yau ta samu damar shiga har uwar ɗakin Hajiya Umma tana sharar hawaye tace " mu je na gasa miki ƙafar ta ki uwarɗakina ko kya ɗan ji daɗin ta sannu kin ji Allah ya miki sakayya .
Hajiya Umma da take kallon Falmata cike da tausayi cikin ran ta wani irin yanayi take ji zuwa yanzu ta fara yarda da cewa kamar da sakacin ta har Hajiya Mama tayi nasarar kama Falmata yarinyar da zuwa yanzu ta fahimci da ita da danginta baki ɗaya basu da wata alaƙa da halin da rayuwar ɗan ta ya kasance a ciki kamar yadda take zato a baya , ashe Hajiya Mama ita ce mafarin kome ba Falmata da 'yar uwar ta ba .
Fuskar ta bata ɓoye halin da zuciyar ta ke ciki ba tace " kar a taɓa mata ƙafar za'a ƙira mai gyara yazo ya duba idan ma kuma asibiti za'a kai ta sai a tafi .
Ɗan lankwasa kai Hajja tayi tace "to bari a jira , O' ni hauwa'u yau na ga kura da fatar akuya ganin idona , wasu mutanen launin hankaka ne da su gaban su fari bayan su baƙi ai ba ƙaramin marar imani bane zai yi kinnafin ɗin ɗan adam ba , yo ai tazarar da take tsakanin kinnafaa da boko haram kaɗan ce , Allah ya raba mu da miyagun mutane .
A hankali Hajiya Umma ta amsa da "Amin dai , tana mayar da kallon ta kan Hajja.
A can ɗakin ganawa ta musamman Maimartaba tare da manyan mutanen Fada nasiha suka dunga yiwa Biyamuradi Youssouf suna tausar zuciyar sa , sun gwada masa girman haƙuri tare da matsayin da mutanen da Allah ya yiwa baiwa da haƙuri suke shi tare a gurin sa
da kusanci da haƙuri ke kawo wa tsakanin Mutum da Mahalccin sa Sannan suka jawo masa ayoyi da hadisai .
A ƙarshe suka bashi tabbaci kan cewa jarabawar Rayuwa ce Allah ya masa domin ya gwada ƙarfin imanin sa dan haka ya bar kome ga Ubangiji da idanun sa zai ga sakayya .
A hankali ya dunga jin nutsuwa na safko masa da kafin wani lokaci ya ji baki ɗaya zuciyar sa ta sauƙa wani irin nutsuwar da ya jima bai ji irin ta ba tana safko masa .
Liman da yake malami masanin Alkur'ani ya cigaba da cewa
"sannan shi sihiri gaskiya ne da masu aikata shi kaÉ—ai suka yi imani da shi ,
"babu shakka cikin kur'ani duk wani magani da warakar kowacce cuta yake dan haka ga ayoyin Alkur'ani masu warware sihiri zan faɗa maka idan za ka iya kayi da kan ka Yousssouf idan kuma ka gaza ka bayar a yi maka ina mai tabbatar maka da cewa dukkanin wani sihiri da anka maka sai ya karye da iznin Allah sannan kuma Allah zai baka kariya daga dukkanin wani mgunta da za'a sake nufar ka da shi ta hanyar sihiri ba zai yi tasiri akan ka ba, ka samu takarda da alƙalami ka rubuta a yanzu Youssoufa ayoyin sune kamar haka :
1). Ta'awwizi da Basmala.
2). Fatiha kafa 7.
3). Aya biyar Ta farkon Suratul Bakara sau 7.
4). Ayoyi biyu ta tsakiyan suratul Bakara wato - Wa ilahukum ilahum wahid la'ilaha illa huwa har karshe sau 7.
5). Ayatul kursiyyu Suratul Bakara aya ta 255 sau 7.
6). Ayoyi uku a karshen Suratul Bakara wato daga baikin Amanarrasul Bakara 284-286 sau 7.
7). Shahidallahu a chikin Al Imran aya ta 18 da 19 sau 7.
8). Inna Rabbakumullahi Ladhi khalaqas samawati wal ardh.. acikin Suratul Al'araf aya ta 54 da 56 sau 7.
9). Afa hasibtum Annama khalaqanakum Abasan suratl Mu'minin aya ta 115 da 118 sau 7.
10). Wa Annahu ta'ala Jaddu rabbina mattakhadha..." a cikin Suratul Jinni aya ta 3 zuwa ta 9 shima kafa 7.
11). Aya goma na farkon Suratul Saffat shima sau 7.
12). Aya Uku na karshen Suratul Hashri wato "Lau anzalna hathal Quran.
13). Aya ta 10 na karshen suratul Yasin su ma sau 7.
14). Kulya ayyuhal kafirun sau 7.
15). Qul huwallahu ahad sau 7.
16). Falaqi sau 7.
17). Nasi sau 7.
A rika tofawa a ruwan zamzam ko ruwan sama ko ayi a duka biyun amma dabam dabam a samo ganyen magarya a dandaka guda bakwai-bakwai har gida 7 wato na kwana 7 Safiya da maraice ana sha ana shafe jiki dashi.
Da fatan ka Fahimta Yossoufa ? Sannan a kome kake kada kayi wassa da ibadar ka domin itta ɗin kariya ce mai girma daga dukkanin abun ƙi , ka faɗaɗa ibarda ka yalwata ta , sannan ka yawaita sadakha domin ita ma kariya ce .'
Youssouf da yake gama rubutu ya É—ago kan sa fuskar sa a nutse yace" na fahimta Malam kuma Nagode Allah shi saka da alkhairi .
Daganan ya baro sashin maimartaba bayan ya musu godiya mai tarin yawa , ya bar su suna cigaba da tattunawa .
Sashin sa ya nufa kai tsaye yayi wanka ya ɗaura alwalar sallar la'asar zuciyar sa da take cike da tausayin Falmata da son sanin halin da take ciki ta sa shi dole ya miƙa hanya zuwa sashin Hajiya Umma .
A zaune ya tarar da Hajiya Umma , a falon ta na ciki da Hajja sai kuma Ubbo suna sake jimamin lamarin banda ɓarin nauyayan kalmomi babu abun da Hajja take yi da lokaci-lokaci ubbo kan yi dariyar wasu kalmomin na Hajja .
Zuciyar Hajiya Umma ta sanyaya da ganin Yousouf ya dawo cikin nutsuwar sa har ma ta gagara ɓoye jin dadin ta .
Tayi hamdalah a bayyane .
Bayan sun gaisa ta ɗan dube shi kafin tace " ƙafar Fatima da akwai ciwo domin kouwa da kyar take iya takawa duk da dai na mata tambayoyi cikin amsar da ta bayar tacce bata da wata damuwa sai ta ƙafar da daman akwai tsohon targaɗe a gurin kuma ta sake gurɗewa dan haka nayi magana a ƙira mai gyara a duba ƙafar ko kuwa asibiti za'a ?
Cike da jin daÉ—in kulawar da ta nuna a karon farko ga Falmata , Youssouf yace "duk wanda kin ka ga yafi dacewa Umma.
"Ka shiga ciki ka gan ta suna É—aki tare da Siyama.
A bisa ɗaya daga cikin gadajen Hajiya Umma biyu da suke ɗakin ya hango ta a zaune tayi wankan ta fes jikin ta sanye da doguwar riga ta atamfa daga gefe Siyama ce a kusa da ita hannun ta riƙe da wani ɗan kyakkyawan tasa ( Bowl ) da aka zuba ferfesun ƙaza a ciki da chokala biyu a ciki fork da soup spoons,
Ganin shigowar sa bai sa Siyama ta fasa kai soup spoon É—in da ta cika da ruwan ferfesun bakin Falmata ba sai dai ta amsa sallamar sa da murmushi akan fuskar ta .
Ƙarasowa bakin gadon Youssouf yayi ya zauna a ɗaya gefen yana bin ƙafar Falmata da kallo wanda ta kumbura daga idon sawun .
Kallon sa ya mayar ga Siyama yana jifatan ta da É—an kyakkyawan murmushi yace
"Siyama kina gatata ƙamnar ki hakka ? Da har kin ka ciyar da ita ba tare da ni kin tuna da cikina ba ?
ÆŠan murmushi Siyama tayi kafin tace " ai itta a yanzu marar lafiya ce kai kouwa ka samu waraka insha Allah .
Murmushi yayi yana mayar da ganin sa kan Falmata yace "Fatima yaya ƙarfin jiki ? Ina ke miki ciwo bayan sawun ki ?
Cikin 'yar ƙaramar murya tace "ba ko'ina sai ƙafar tawa.
Tashi yayi daga bakin gadon ya ɗan yi durƙuso kafin ya kama ƙafar falmata a hankali ya ɗago ta ,
Ganin haka yasa Siyama tayi saurin miƙewa bayan ta ajiye kwanon hannun ta akan ɗan teburin gefen gado (bedside cabinet) .
Ta nufi ficewa daga É—akin " Maman Yumna ina za ki tai ?
Youssouf ya furta haka yana bin ta da kallo
Lumshe idanun ta tayi ba tare da ta jiyo ba tace " zan tai na kawo ma abinci .
Daga haka ta ƙarasa barin ɗakin tana jin yadda suke kokawa tsakanin ta da zuciyar ta da take son ganin baƙin Youssouf da Falmatan.
A hankali ya mayar da ganin sa kan ƙafar Falmatan ya kai ɗan yatsan sa babba ya shafa gurin da ya ɗan kumbura a hankali da yasa Falmata rufe idanun ta a hankali tana jin yadda tsiƙar jikin ta ke tashi tare da wani yanayi da take ji na tausayi mai girma yana huda zuciyar ta , yana bin duk wani saƙo da lungu da ɓurɓushin jin haushin Youssoufa ya maƙale a ran ta kan laifin da take zaton duk yayi su a bisa son rai cikin sanin sa da yin kan sa .
Da hannu Hajiya Umma ta ƙira Ubbo da Siyama waɗan da suma suke tsaye kasaƙe kamar ruwa ya cinye su tace " ku kama ta zouwa sashi na .
Cikin sauri Youssouf ya girgiza kai kafin yace " zan tai da ita da kaina.
Gyaran murya Maimartaba yayi kafin yace
" bar su su tai da ita kai kouma ka biyo ni .
Daga haka ya juya bayu da sauran al'ummar gidan da har kawo yanzu babu wanda ya iya cewa ƙala wasu suka rufa masa baya .
Youssouf bai saki hannun Falmata ba duk da cewa tun da ta ji muryoyin mutane a wajen ta raba jikin ta daga na shi amma ya ƙi sakin hannun ta .
Har Sai da Hajiya Umma ta kama hannun Falmatan ɗaya ta rike sannan tace masa " ka tai ga ƙiran Mahaifin ka , itta tana ƙarƙashin kulawata .
A hankali ya miƙe yana waiwayen Falmata da ta sunkuyar da kan ta ya fita zuciyar sa cike da jin tausayin falmata da ya lura har rama tayi ta fita a kamannin ta duk wai a sanadin sa Hajiya Saratu ta mata haka ?
Ubbo da kan ta ta haÉ—awa Falmata ruwan wanka kamar yadda Hajiya Umma ta umarce ta ,
Hajja wacce yau ta samu damar shiga har uwar ɗakin Hajiya Umma tana sharar hawaye tace " mu je na gasa miki ƙafar ta ki uwarɗakina ko kya ɗan ji daɗin ta sannu kin ji Allah ya miki sakayya .
Hajiya Umma da take kallon Falmata cike da tausayi cikin ran ta wani irin yanayi take ji zuwa yanzu ta fara yarda da cewa kamar da sakacin ta har Hajiya Mama tayi nasarar kama Falmata yarinyar da zuwa yanzu ta fahimci da ita da danginta baki ɗaya basu da wata alaƙa da halin da rayuwar ɗan ta ya kasance a ciki kamar yadda take zato a baya , ashe Hajiya Mama ita ce mafarin kome ba Falmata da 'yar uwar ta ba .
Fuskar ta bata ɓoye halin da zuciyar ta ke ciki ba tace " kar a taɓa mata ƙafar za'a ƙira mai gyara yazo ya duba idan ma kuma asibiti za'a kai ta sai a tafi .
Ɗan lankwasa kai Hajja tayi tace "to bari a jira , O' ni hauwa'u yau na ga kura da fatar akuya ganin idona , wasu mutanen launin hankaka ne da su gaban su fari bayan su baƙi ai ba ƙaramin marar imani bane zai yi kinnafin ɗin ɗan adam ba , yo ai tazarar da take tsakanin kinnafaa da boko haram kaɗan ce , Allah ya raba mu da miyagun mutane .
A hankali Hajiya Umma ta amsa da "Amin dai , tana mayar da kallon ta kan Hajja.
A can ɗakin ganawa ta musamman Maimartaba tare da manyan mutanen Fada nasiha suka dunga yiwa Biyamuradi Youssouf suna tausar zuciyar sa , sun gwada masa girman haƙuri tare da matsayin da mutanen da Allah ya yiwa baiwa da haƙuri suke shi tare a gurin sa
da kusanci da haƙuri ke kawo wa tsakanin Mutum da Mahalccin sa Sannan suka jawo masa ayoyi da hadisai .
A ƙarshe suka bashi tabbaci kan cewa jarabawar Rayuwa ce Allah ya masa domin ya gwada ƙarfin imanin sa dan haka ya bar kome ga Ubangiji da idanun sa zai ga sakayya .
A hankali ya dunga jin nutsuwa na safko masa da kafin wani lokaci ya ji baki ɗaya zuciyar sa ta sauƙa wani irin nutsuwar da ya jima bai ji irin ta ba tana safko masa .
Liman da yake malami masanin Alkur'ani ya cigaba da cewa
"sannan shi sihiri gaskiya ne da masu aikata shi kaÉ—ai suka yi imani da shi ,
"babu shakka cikin kur'ani duk wani magani da warakar kowacce cuta yake dan haka ga ayoyin Alkur'ani masu warware sihiri zan faɗa maka idan za ka iya kayi da kan ka Yousssouf idan kuma ka gaza ka bayar a yi maka ina mai tabbatar maka da cewa dukkanin wani sihiri da anka maka sai ya karye da iznin Allah sannan kuma Allah zai baka kariya daga dukkanin wani mgunta da za'a sake nufar ka da shi ta hanyar sihiri ba zai yi tasiri akan ka ba, ka samu takarda da alƙalami ka rubuta a yanzu Youssoufa ayoyin sune kamar haka :
1). Ta'awwizi da Basmala.
2). Fatiha kafa 7.
3). Aya biyar Ta farkon Suratul Bakara sau 7.
4). Ayoyi biyu ta tsakiyan suratul Bakara wato - Wa ilahukum ilahum wahid la'ilaha illa huwa har karshe sau 7.
5). Ayatul kursiyyu Suratul Bakara aya ta 255 sau 7.
6). Ayoyi uku a karshen Suratul Bakara wato daga baikin Amanarrasul Bakara 284-286 sau 7.
7). Shahidallahu a chikin Al Imran aya ta 18 da 19 sau 7.
8). Inna Rabbakumullahi Ladhi khalaqas samawati wal ardh.. acikin Suratul Al'araf aya ta 54 da 56 sau 7.
9). Afa hasibtum Annama khalaqanakum Abasan suratl Mu'minin aya ta 115 da 118 sau 7.
10). Wa Annahu ta'ala Jaddu rabbina mattakhadha..." a cikin Suratul Jinni aya ta 3 zuwa ta 9 shima kafa 7.
11). Aya goma na farkon Suratul Saffat shima sau 7.
12). Aya Uku na karshen Suratul Hashri wato "Lau anzalna hathal Quran.
13). Aya ta 10 na karshen suratul Yasin su ma sau 7.
14). Kulya ayyuhal kafirun sau 7.
15). Qul huwallahu ahad sau 7.
16). Falaqi sau 7.
17). Nasi sau 7.
A rika tofawa a ruwan zamzam ko ruwan sama ko ayi a duka biyun amma dabam dabam a samo ganyen magarya a dandaka guda bakwai-bakwai har gida 7 wato na kwana 7 Safiya da maraice ana sha ana shafe jiki dashi.
Da fatan ka Fahimta Yossoufa ? Sannan a kome kake kada kayi wassa da ibadar ka domin itta ɗin kariya ce mai girma daga dukkanin abun ƙi , ka faɗaɗa ibarda ka yalwata ta , sannan ka yawaita sadakha domin ita ma kariya ce .'
Youssouf da yake gama rubutu ya É—ago kan sa fuskar sa a nutse yace" na fahimta Malam kuma Nagode Allah shi saka da alkhairi .
Daganan ya baro sashin maimartaba bayan ya musu godiya mai tarin yawa , ya bar su suna cigaba da tattunawa .
Sashin sa ya nufa kai tsaye yayi wanka ya ɗaura alwalar sallar la'asar zuciyar sa da take cike da tausayin Falmata da son sanin halin da take ciki ta sa shi dole ya miƙa hanya zuwa sashin Hajiya Umma .
A zaune ya tarar da Hajiya Umma , a falon ta na ciki da Hajja sai kuma Ubbo suna sake jimamin lamarin banda ɓarin nauyayan kalmomi babu abun da Hajja take yi da lokaci-lokaci ubbo kan yi dariyar wasu kalmomin na Hajja .
Zuciyar Hajiya Umma ta sanyaya da ganin Yousouf ya dawo cikin nutsuwar sa har ma ta gagara ɓoye jin dadin ta .
Tayi hamdalah a bayyane .
Bayan sun gaisa ta ɗan dube shi kafin tace " ƙafar Fatima da akwai ciwo domin kouwa da kyar take iya takawa duk da dai na mata tambayoyi cikin amsar da ta bayar tacce bata da wata damuwa sai ta ƙafar da daman akwai tsohon targaɗe a gurin kuma ta sake gurɗewa dan haka nayi magana a ƙira mai gyara a duba ƙafar ko kuwa asibiti za'a ?
Cike da jin daÉ—in kulawar da ta nuna a karon farko ga Falmata , Youssouf yace "duk wanda kin ka ga yafi dacewa Umma.
"Ka shiga ciki ka gan ta suna É—aki tare da Siyama.
A bisa ɗaya daga cikin gadajen Hajiya Umma biyu da suke ɗakin ya hango ta a zaune tayi wankan ta fes jikin ta sanye da doguwar riga ta atamfa daga gefe Siyama ce a kusa da ita hannun ta riƙe da wani ɗan kyakkyawan tasa ( Bowl ) da aka zuba ferfesun ƙaza a ciki da chokala biyu a ciki fork da soup spoons,
Ganin shigowar sa bai sa Siyama ta fasa kai soup spoon É—in da ta cika da ruwan ferfesun bakin Falmata ba sai dai ta amsa sallamar sa da murmushi akan fuskar ta .
Ƙarasowa bakin gadon Youssouf yayi ya zauna a ɗaya gefen yana bin ƙafar Falmata da kallo wanda ta kumbura daga idon sawun .
Kallon sa ya mayar ga Siyama yana jifatan ta da É—an kyakkyawan murmushi yace
"Siyama kina gatata ƙamnar ki hakka ? Da har kin ka ciyar da ita ba tare da ni kin tuna da cikina ba ?
ÆŠan murmushi Siyama tayi kafin tace " ai itta a yanzu marar lafiya ce kai kouwa ka samu waraka insha Allah .
Murmushi yayi yana mayar da ganin sa kan Falmata yace "Fatima yaya ƙarfin jiki ? Ina ke miki ciwo bayan sawun ki ?
Cikin 'yar ƙaramar murya tace "ba ko'ina sai ƙafar tawa.
Tashi yayi daga bakin gadon ya ɗan yi durƙuso kafin ya kama ƙafar falmata a hankali ya ɗago ta ,
Ganin haka yasa Siyama tayi saurin miƙewa bayan ta ajiye kwanon hannun ta akan ɗan teburin gefen gado (bedside cabinet) .
Ta nufi ficewa daga É—akin " Maman Yumna ina za ki tai ?
Youssouf ya furta haka yana bin ta da kallo
Lumshe idanun ta tayi ba tare da ta jiyo ba tace " zan tai na kawo ma abinci .
Daga haka ta ƙarasa barin ɗakin tana jin yadda suke kokawa tsakanin ta da zuciyar ta da take son ganin baƙin Youssouf da Falmatan.
A hankali ya mayar da ganin sa kan ƙafar Falmatan ya kai ɗan yatsan sa babba ya shafa gurin da ya ɗan kumbura a hankali da yasa Falmata rufe idanun ta a hankali tana jin yadda tsiƙar jikin ta ke tashi tare da wani yanayi da take ji na tausayi mai girma yana huda zuciyar ta , yana bin duk wani saƙo da lungu da ɓurɓushin jin haushin Youssoufa ya maƙale a ran ta kan laifin da take zaton duk yayi su a bisa son rai cikin sanin sa da yin kan sa .