← Book details Mafari Hargitsin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 118 OF 269

Sashe 118

Mafari Hargitsin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Sai yayi wani zugum kamar soko ya sanya mata ido , ah to shi zata yi wa bariki ?? Ai ya san me ake nufi da budurci , " amma tunaninikan da suke bijiro masa da shuÉ—aÉ—É—en laifin sa suke barazana ga nutsuwar sa saboda zuwan dodo-dodo da suke masa suna sake maimaita kan su tare da bada fassara akan halin da ya riski matar sa a ciki ,

Hannun sa ya kai da ƙarfi ya jawo ta ya jefa kan ta kan ƙirjin sa yana jin yadda iskancin kukan da take yana sake dagula masa lissafi ,

ÆŠan Allah ki min shiru
  Yace da ita , a tsawace

Da yake daman kukan gulma ne sai tayi luf kafin gajiyar biki tare da gajiyar farkon daren su danne ta bacci me matuƙar ƙarfi da daɗi ya silalo ya chafke ta ,

A hankali ya zame ta daga jikin sa ya miƙe daga kan gadon , rigar baccin sa ya ɗauka ya saka , ya fara taku yana barin ɗakin ,

Yayi zurfi a cikin tunanin abun da ka iya je ya dawo cikin rayuwar sa , mama ita take ta kai kawo cikin ran sa , rayuwar É—iyar sa yake hangowa , yana jin wani irin al'amari me girma wanda yake tafe da tsoro akan ta , yana son tsare ta , so yake ya boye ta kar laifin da ya aikata ya shafe ta , tsoro yake kar tarihi ya maimaita kan sa ,

Bakin cikin da yake shaƙa kaɗai a wannan daren yayi masa yawa ma , me yafi ka san cewa matar ka tayi tarayya da wani ta hanyar zina sanya bakin ciki da ruɗani a cikin rai ??

Wani irin kishi me tsanani yake ji , wani irin yanayi yake ji akan ta , ji yake ƙimar ta na zubewa tana zagwanyewa daga ran sa tamkar narkakkiyar roba a cikin wuta , ji yake tamkar yana ƙyamar ta ,

," yaya maimounatu zata min haka,"??
    Yake tambayar kan sa , yana sake maimaitawa ,

  Meyasa ? Meyasa ? Wai meyasa ?

Bai san cewa ya fito har harabar gidan ba sai da ya ji ƙaƙƙarfar iskar dake wajen tana ɗaga rigar sa da bai ɗaure maɗaurin ba , a hankali ya kai hannu ya ja igiyar yana ɗaurewa ,

Tun da ya fito idanun ta suka sauƙa a kan sa saboda daman ta gagara bacci ban da juyi babu abunda take , ita mace ce me zafin kishin abunda take so , dan haka sanin cewa da tayi yau ɗin biyamurdi zai kasance da gimbiya maimouna ya ta'azzara soyuwar ran ta , ya sa bacci gagara ɗaukar ta duk kuwa da iya satar sa ,

   Dan haka ta fito ta barandar ɗakin ta dake sama tana iya hango gaba ɗayan harabar gidan ta kurkusa daga inda take , duk kuwa da sanin da tayi dare ya raba ƙarfe 1:30am , to amma zafin kishi haɗi da bagen so ai rufe idanun me su suke yi .

  Me ya fito da shi a wannan daren ??
   Ta tambayi kan ta

Ta san shi farin sani kamar yadda duk wani motsi nasa yake kusa da zuciyar ta , take kuma iya fassara kowanne motsi nasa

Kada dai inda ya saba fita ya tafi a dai-dai wannan lokacin ya nufa ?? Wani irin tashin hankali ta ji ya taso mata ,
   Zato take ya daina ? Tunda tun bayan dawowar sa daga nigeria bata ji alamun fitar sa ba , bata kuma gan shi ya fita ba ,

Tunanin ta ya katse lokacin da ta ga ya É—aga kan sa sama tare da waiwayowa sashin da take ,

   Da sauri ta tsugunna tana ɓuya a bayan ginin gaban barandar ,

Cigaba yayi da kallon sashin nata lokacin da zuciyar sa ke kitsa masa wataƙila ita ma wannan ɗin da aka liƙa masa , ta riga ta gama sayar da nata mutuncin a waje ,

ya dangana kome da ya faru a matsayin hakkin baiwar Allah yakaka da ya É—auka , ya jagorance ta suka aikata mummunan laifi , shi daman Alhaki ai kuikuyo ne .!

*****

Asubar fari ya hau shiri , garin baki É—aya yayi masa wari , so yake ya tafi , yana son zuwa ya ga mama yasan ganin fuskar ta ne kaÉ—ai zai iya sassauta masa zafin da ran sa ke yi ,

Daga sashin sa kai tsaye cikin gida ya tasamma sashin hajiya umma ba tare da ya dubi sashin kowaccen su ba tsakanin sashin gimbiya maimouna da tun barin sa da yayi cikin dare da sashin siyama wacce bai ko kai da sanin launin kayan da suke cibge a ciki ba ,

Yana ratsa sararik gidan yana amsa gaisuwar bayu da hadiman da suke kai kawo suna gyaran gidan da sanyin safiyar .

A falo na ciki ya tadda hajiya umma tana Azkar , gefen ta ɗan ƙaramin tire ne da aka jera gorar ruwa da ƴan kofunan gilashi ,

Tana ganin sa farin ciki ya bayyana kan sa bisa fuskar ta , cikar haiba da mutuntukar da ta hango tare da shi ya sa ya yi mata ƙwarjini a yau , tabbas aure cikamakin addini ne , cikin sa akwai martaba tare da girma me yawa ,

Gaishe ta yayi sai dai saɓanin da da yake shigewa kusa da jikin ta , yau ɗin tanƙwashe kafafun sa yayi a gaba kaɗan da ita ya sunkuyar da kan sa ,

Kallon tsanaki tayi masa ba sai ya faɗa mata ba ta san yana tare da damuwa me girma wanda a jiya kafin rabuwar su da yamma babu wannan damuwar a tare da shi , dan haka take hasashen ko menene damuwar sa tana da alaƙa da iyalan sa , ita kuma bata da burin zama ɗaya daga cikin iyayen da suke bincikar rayuwar gidan auren ƴaƴan su dan haka sai ta yi kamar bata ga damuwar ta sa ba , ta matsa zuciyar ta da ke son sanin meye ya same shi ?

Yaya kwanan ɗiya na su dukkanin su da fatan kun tashi lafiya ? Basu da buƙatar wani abu ?

Duk kowa lafiya umma na basu buƙatar kome ,

  Umma zan tafi bakin aiki doumin an ƙira ni daga niamey bisa ga wani aiki na gouggawa da ya taso ,

Aiki ? Ba an baka houtu ba na tsawon sati gouda ?

Umma aikin mu na kare rayuka da dukiyoyin al'umma ne koyaushe ana iya ƙiran mu kuma a kowanne yanayi da lokaci , !

Shiru tayi tana nazarin sa , kafin ta jefo masa tambayar da ta sanya shi É—ago kai

Tare da siyama zaku tafi kou ?

Shiru yayi kafin ya tattaro ƙarfin halin da ya yi masa saura
     Niamey zan tafi ba dosso ba Umma , idan na dawo daga niamey zamu tafi dosso tare.

bata jaa ba tayi masa addu'o'i kamar yadda ta saba tare da ƴan nasihohi , ƙarshe ta sake tunasar da shi girman nawin da ke kan sa a yanzu , !

****

Tunda ya hau kujerar zaman sa a jirgin da zai É—aga da shi zuwa niamey ya zurfafa cikin tunani daki-daki ,

Da hantsi ya samu isa ƙofar gidan , kan layin shiru , da yake unguwar babu yawan mutane , ya cire ƙuɗin me taxi ya biya shi , ƙarasawa yayi jikin ƙofar gidan ya ƙwanƙwasa

Hajja wacce take tsakiyar sharar ƴar harabar gidan ta saurara da kyau ta tabbatar cewa gidan nasu ake bugu , ta ajiye tsintsiyar ta ƙaraso jikin ƙofar ta tambaya wanene ??

Hajja ni ne ,
    Ta shaida muryar sa dan haka ta zare sakatar ƙofar ya samu shigowa gidan , sai fara'a take masa tana lale marhabin da shi ,

   Shiga ciki Babban soja bari na ƙarasa ture ɗan wajen nan zan zo mu gaisa , sannu ka sha doguwar tafiye ince kwana kayi a hanya ?

Murmushi yayi ba tare da ya amsa mata ba ya sanya kai cikin gidan ,

Ƙiiii
   Ƙarar turo ƙofar sa ta sanya ta ɗago kan ta ta dubi sashin da ta ji motsi ,

   Hajja sannu da aiki !
Tace cikin Æ´ar muryar ta ,

Bai amsa ba saboda baki ɗaya hankalin sa da idanun sa na ga fuskar mama wacce take jingine da jikin falmata akan cinyar ta  , su duk biyun suna fuskantar ,

Taku ya fara yi yana jin yadda shauƙin son ta ke ɗibar shi , da sassarfa ya ƙarasa gaban su ya tsugunna gami da kai hannun sa ya kama ƴan kafafun ta da suke sanye da ƴar safa ya sunkuyo da fuskar sa ya sumbata yana me rufe idanun sa da jin yadda ƙaunar ta ke sake ratsa shi tare da wata nutsuwa ta musamman , me yake ƙauna irin ta tsakanin ɗa da iyaye ƙarfi tare da tsafta ??.

Lokacin da ya É—ago kan sa falmata ta kawo hannunwan ta duk biyu ta É—ora akan fuskar sa , a hankali tayi yawo da hannuwan ta tana shafar fuskar sa da idanun sa ke rufe ,

Tamkar wuta ta jaa ta ta janye hannuwan ta da sauri , tana É—auke mama ta É—ora kan kafaÉ—ar ta ,

  Da farko tayi zaton hajja ce ta shigo, sanin cewa daga ita sai hajja a gidan .

Wa-waye ne ? Tace tana ƙoƙarin miƙewa ,
  
   Koma ki zauna Fatima ni ne ,

Ya kai hannu yana ƙoƙarin karɓar mama ,

Ta gane muryar sa dan haka ta sakar masa mama a hankali , tana dai-daita numfashin ta da firgici ya sa shi hargitsewa ,

Yana karɓar ta yayi mazauni akan ɗaya daga cikin kujerun wajen ba tare da ya janye idanun sa daga kan ta ba ya shiga sumbatar kumatu zuwa goshin ta ,

Bai ko ji gaisuwar da falmata wacce ta zauna daga ƙasa a gefe take yi masa ba ,
    ita ma shiru tayi ganin bai amsa ba

Shigowar hajja ya sanya shi rungume mama a jikin sa suna gaisawa shi da hajja ,
Chapter 118 · 0% Book details