← Book details Mafari Hargitsin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 186 OF 269

Sashe 186

Mafari Hargitsin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Tafeeda ka ce mouna babu wanda ya san da tabbatuwa lamarin nan sai kai ɗai ?  Sai kouma mu da yanzou ka taho da mu , to Yaya anka yi mouhammadou ya iso nan ? Ko kouwa shi Youssoufa ya ƙiraye shi ?

Cike da nazari Tafeeda ya nisa ,

"Adda ni bansan kome game da wanzuwat shi ba , wataƙila Youssoufa ya ƙiraye shi , sai dai nafi zaton zuwan kan sa yayi ɗauke da wani ƙudiri nashi na daban ,

Duk suka sake yin shiru a motar , bayyanar Mouhammadou a boyayyen gidan Youssoufa na sirri ya sanya su a ruÉ—ani ,

Bayan iyayen su da suka san maganar zaman Youssouf da mace har ma da É—iya ba ta aure ba a ta bakin wasu mutane ,

Tafeeda shine mutum ɗaya tal da yasan haƙiƙanin gaskiyar lamuran , shine kuma ya yi ta ƙoƙari wajen ganin ya wanke Youssouf , ya dunga neman Youssouf da ya dawo su fuskanci matsalar su maganceta tun kafin duniya ta ɗauka .

Amma daga baya  sai Youssouf yaƙi ba shi haɗin kai , wannan dalilin ne ma ya sa shi dole ya samu yayun Youssouf ɗin Adda Ammi , da Ubbo da su ma suke cikin tashin hankali jin cewa ɗan uwansu yana can America tare da karuwa da 'yar su ,

Shi yayi musu bayanai na haƙiƙanin gaskiyar kome cewa ba fa zaman dadiro Youssouf yake yi ba amren yarinyar yake yi daga ƙasar Nigeria wacce kuma ƙanwace ga ainahin uwar yarinyar da ya yiwa ciki ba ta hanyar aure ba ta kuma rasu a wajen haihuwar 'yar .

Ba ƙaramin baƙin-ciki suka shiga ba da jin irin ta'asar da ɗan uwan su ya aikata , har kuma yake da tsaurin idanun cigaba da yin yadda ya ga dama ,

Dan haka suka tsaida shawarar muddin Youssouf ɗin ya dawo su zasu yi takakkiya zuwa gidan da ya ɓuya yake yin rashin gaskiya ,

su kuma sanya dole ya saki amren yarinyar da yake riƙo tare da haɗa ta da ɗiyar su koma da ita can ƙasar su ,

su basa yadda ya gurɓata musu sunan zuri'a da masarautar su , ba kuma zasu amince ya kawo musu baragurbin ɗiyar sa ba , bare wata matar da bata da masauƙi a tsakanin su ,

wacece ita da zata zama sanadin ɓacin ran iyayen su , ta kuma samu damar zama matar ɗan uwan su Yarima sarkin watarana ??

Adda ammi ta ɗau wayar ta tana sake ƙiran layin Youssouf dai-dai lokacin da taxi ɗin da Yakaka tayi shata , ya ajiyeta a ƙofar gidan ta bashi kuɗin sa ,

Ta kama hanyar shiga gidan hannun ta riƙe da kulolin abincin da ta dawo da su daga asibiti , da kyar take taku saboda tsabar gajiya da bacci da ya cika mata ido ,

Adda Ammi tana jin Youssouf ya É—aga wayar bata tsaya amsa gaisuwar sa da yake yi mata ba cikin dakakkiyar muryar ta tace da shi ,

"Youssoufa ga munan ƙofar gidan ka , ka hito ka yi mouna jagora ,

Da 'yar ruɗewa cikin muryar sa lokacin da yake miƙewa yana barin abincin da ya fara ci yace

"Adda ai bani gida maraÉ—i ba kouma na tahoue , ina Niamey ne wajen aikina ,

"Na sani ƙofar gidan ka na niemey ɗin nake magana ko kouwa baka hitowa ka mouna jagora sai mu shiga da kanmu ?

Fitowa yayi hankalin sa a tashe ya nufi ƙofar gidan ko takalma babu a ƙafarsa  ,

A harabar gidan ya ci karo da Yakaka wacce take shigowa , kallon juna suka yi kowannen su ransa a ɓace , ya gota ta kai tsaye ya buɗe ƙofar gidan idanunsa suka sauƙa akansu duk ukun suna fitowa daga motar ,

Yawun bakin sa ya ji ya ƙame , ya rasa halin da yake ciki takamaimai  , ,

da murmushin yaƙe ya ƙaraso gaban su , ya ɗan sosa ƙeya bayan ya rage tsawo ya shiga gaishe su ,

Sama-sama suka amsa suna binsa da kallo ganin yadda duk yake a firgice da alamun rashin gaskiya ,

"Bismillah,
yace da su yana yin gaba , ba tare da ko sau ɗaya ya dubi sashin da Tafeeda yake tsaye ba saboda gudun yadda zata kaya a tsaƙanin su da ya riga ya san cewa shine ya haɗo masa wannan gangamin ,

Da shigar su harabar gidan yayi nufin kai su sashin sa , sai dai tsintar maganar Adda Ammi yayi tana tambayar sa ina matar gidan ?

Cikin dakiya ya waigo , "tana ciki , yace a takaice yana kallon ta ,

"to ai wajen ta yakamata mu shiga duk muyi maganar da take tafe da mu  ,

ÆŠan jim yayi yana kallon ta , cikin shakku , sai dai yadda tayi maganar cikin lumana ya sa ya wuce gaba zuwa sashin Falmata suna bin bayansa ,

Zuciyarsa cike da fatan samun masalaha akan koma menene , fatan sa Allah yasa zuwan su ya gyara kome ,

Suna shiga falon suka tarar da Yakaka a zaune daga ƙasa tana hutawa tare da jiran shigowar Falmata da take zaton ko tana wajen Youssouf zuciyarta ɗauke da ƙudirin fara sanar mata da kome a yau ,

Shigowar su ya sa ta miƙe , fuskarta kadaran-kadahan ta gaishe su ,

Shi Tafeeda bai amsa ba , Ammi da Ubbo ne suka amsa a taƙaice suna ƙare mata kallo sama da ƙasa , zuciyar su na shaida musu wannan me kama da asbinawan ce ta sa ɗan ouwan su kaucewa hanya ??

Ratsawa tayi zata wuce ta bar su Ubbo ta dakatar da ita ,

"baiwar Allah dawo nan , kou ba ita ce  matar gidan ba ?
   ta juya akalar tambayarta ga youssouf

Da sauri Youssouf ya girgiza kai ,
   "Ba itta ce ba ,

To ita wannan wace ?

Adda Ammi ta tambaye shi

a ciki ya amsa ,
"yal ouwatta ce ,
.ubbo tace
"itta ina tai ?
" bacci take , adda domin Allah muyi duk maganar da zamu yi ni da ku ,

"Ke

Adda Ummi ta buɗe murya wajen ƙiran Yakaka wacce har lokacin take rakaɓe daga gefe a tsaye ,

"ki tai ki tado mouna da 'yal ouwakki ku taho tare ,

Yakaka bata san me suke nufi ba hausar tai mata nisa dan haka ta tsaya tsam tana kallon su ta ƙasan ido ,

Youssouf da yanayin Ammi ya fara É—arsa masa tsoro a rai , ya nunawa Yakaka É—akin da Falmata take ciki ,yace

" Fatima tana ciki ki ƙira ta ,

A hankali Yakaka ta tura ƙofar ɗakin Falmata da har kawo yanzu baccin ta take yi ,

Ta ƙarasa bakin gadon a hankali ta dafa ta ,

"Falmata , Falmata , ta ƙira sunan ta tana ɗan jijjigata ,

Buɗe idanunta da suka yi mata nawi tayi , sai kuma ta ware su da sauri ta miƙe zaune tare da riƙe hannun Yakaka da take hango ta dusu-dusu ,

" Yakaka kece ? Ina Mama ? Ya jikin nata ? Ta samu sauƙi ? Tayi bacci ? Bata yi kuka ba ko ?

" jikin Mama da sauƙi na baro ta tana bacci , Yanzu muje falo kina da baƙi ,

" Baƙi ?su waye  ? mu babu wanda yake zuwa wajen mu ai ?

"wasu mata ne ina ga Æ´an uwan sa ne ,

Yakaka tace tana miƙewa tsaye ,

A hankali Falmata ta kai hannu ta laluɓi gilashinta ta sanya a fuskar ta , bayan ta ɗora hijabi akan doguwar rigar jikinta ,

Tare suka fito falon yatsunsu cikin na juna  ,

Har ƙasa Falmata ta durƙusa ta gaishe da matan da ta tarar da ƙamshin su ya cika falon , sannan ta gaishe da Tafeeda ,

Sai tayi shiru jin yadda suka amsa mata a cike da ginshiri ,

"wannan ce matar taka ? Uwar 'yar taka ? Wannan kuma 'yar uwarta ?

Adda ummi ta tambaya tana nuna Falmata da Yakaka da hannun ta a walaƙance ,

"Eh , ah ah , eh ita ce Matata Fatima ,

Kallon sa su duka biyu suka yi jin yace "eh ya kuma ce "Ah ah ,

Gyara zama tayi ta matso kusa daga kan kujerar ,

" ke yarinya kina jina ?

  Falmata wacce ta fahimci da ita ake , ta gyaɗa kai a hankali bayan ta fuskanci inda take iya ganin Matar da take mata magana sosai ,

" daga ina kike ? Su waye iyayen ki  ?

daga Falmata har Yakaka zuciyoyin su suka buga , Sai Falmata ta sake matso Yakaka tana riƙo Hannun ta ,

A hankali Yakaka ta sauƙe ganin ta akan Adda Ammi ,

" Mu 'yan gudun hijira ne a ƙasar Nigeria, kuma iyayen mu duk sun rasu ,

Ƙutawa tayi tana gyaɗa kai cikin buɗaɗɗiyar Muryar tace " kin san Youssouf wanene ?

Girgiza kai  Falmata tayi alamun "ah ah ,
   " shekarar ku nawa kuna amre ?

Youssouf wanda ya fara hango tsoro a fuskar Falmata tare da hasasho inda Adda Ammi zata ƙarƙare maganar ta ya yunƙuro da nufin katse ta

" Adda Ammi  ....
Da hannu ta dakatar da shi , "Youssoufa ba kai nake tambaya ba ,

"yarinya shekarun ku nawa nace da Amre ?

"shida ,
   Falmata tace cikin siriryar muryar , zuciyar ta cike da son sanin yau wacece agaban ta ko dai mahaifiyar Baban Mama ce ??

Muryar ta ya katse mata tunani,

"kin taba ganin wanni daga cikin dangi nashi ya zou inda kuke ? Ko kouwa ku ya taɓa sada ku da dangin sa ?

Shiru Falmata tayi ,

"kin san dalili ??  Bata jira amsar Falmata ba ta ɗora da cewa ,

"sabadda kama dagga kan iyayensa da mou 'yan ouwansa har zouwa kan dangin da masarautar mu zouwa kan mutanen jahar mou baki É—aya ba mou san da amren kou ba ,

"Youssoufa ɗan Sarki ne , Yarima ne shi , yana da iyayen sa suna raye mu yayyensa ne , yana kouma da ƙanne , sannan yana da matan amre har biyu da ɗiyar sa ,
Chapter 186 · 0% Book details