Sashe 236
Mafari Hargitsin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da wani irin sauti saɓanin wanda aka saba amfani da shi a masarauta yayin da ake gaban sarki Hajja tace " 'Yar nan wannan zancen naki ba gaskiya bane muddin kuma ya zama gaskiya to kune sanadi , saboda abubuwan da kuke yiwa yarinyar nan na tozarci kaɗai ya isa yasa ta zuciya ta bar gidan nan haba mana shin shi talaka ba mutum bane ? Ko kuwa laifin tayi domin ta auri ɗan uwan ku ? Fatima baiwar Allah yarinya ce ƙarama da take da larura wanda idan har baku gwada mata ƙauna ba bai kuwa dace ace kuna tozarta ta ba yanzu me za'a ce ga iyayen ta da kuka yi sanadiyar da ta gudu ba'a san halin da take ciki ba ?..... kasa cigaba tayi da magana saboda kukan da ya ci ƙarfin ta
Hajiya Umma ta yunƙuro zata yi magana da hannu Maimartaba ya dakatar da ita .
"Me yake Faruwa a gidan da ni ban kai ga sani ba ? Waye yake tozarta Al'umma ciki har ma da mutanen da suke amintattun mu da muka amso amarnar su daga hannun mutanen su ?
Shiru aka yi babu mai tsaurin idon iya amsawa .
Kamar daga sama Muryar Youssouf ta ratso wajen inda yake cewa " Fatima ba gudu tayi ba babu makawa É—auke ta aka yi ..
Ya ɗan jinkirta lokacin da idanun kowa ya dawo kan shi zuciyar Hajiya Mama ta fara sauya ƙarfin bugu tana dik-dik-dirim-dim.
"Wa kake tunanin ya É—auke ta ?
Maimartaba ya furta haka cike da nazarin sa ,
Shiru yayi da yasa gumi ya shiga zarya ta cikin rigar Hajiya Mama .
"Maimounatou .
Ya furta hakan da tasowar matsanancin ɓacin rai a muryar sa , ya cigaba da cewa
"Maimounatou ita ta sanya a zo a É—auke Fatima domin cikar burin ta ta wani fanni sai dai a wannan karon ba zan kyale ta ba dole ne na gwada mata ainashin É—abi'ar da na É—au shekaru a wajen koyar ta cikin aikina na na soji .
Muryar Hajiya Mama ita ta ratso wajen cike da wani boyayyen farin-ciki a sautin ta tace " Yarima ni da kaina tunanin da ya fara zowar min kenan ba shakka wannan ɗiyar ta Agades ita ta sanya anka ɗauke wannan yarinya ta ƙwarai kuma dole ayi hanzarin ɗaukar mataki akan haka.
Shiru Maimartaba yayi cikin son yin nazari sai dai hayaniyar da ta fara tashi a tsakanin iyalan sa da duk suka aminta da cewa Maimounatou ce ta tura aka sace Falmata duk kuwa da babu hujja ɗaya da aka samu wanda yake bada tabbaci ga hakan ya dukusar da hanzarin sa musamman lokacin da Youssouf ya miƙe a safure ya taho gaban shi yayi gurfano .
"Ranka shi daÉ—e zan tai Niamey yanzu zan tai na tadda Maimounatou ta faÉ—a min ina ta kai iyalina ?
"Youssoufa ka nutsu wannan batu ne da yake buƙatar nutsuwa da tsawaita bincike , ina maka oumarni da ka jinkirta hanzarin da kake yi har a ƙarƙare bincike a samu madogara .
Da kyar Maimartaba ya shawo kan hayaniyar su bayan ya tabbatar da za'a tsananta bincike kafin tunkarar koma waye da aka samu shaidar yana da hannu a ɓatan Falmata
Bayan fitar su daga Sashin Maimartaba Hajiya Mama bata koma sashin Hajiya Umma ba kai tsaye sashin ta ta koma ba tare da ta zauna cikin 'ya'yan ta da suke ta hira kan batun ɓacewar Matar Youssouf da wasu daga ciki ma daɗin lamarin suke ji saboda ta riga ta gina ƙaƙƙarfar ƙiyayya tsakanin su da Youssouf da duk wani abu na bakin-ciki da zai faru da shi su murna suke yi .
Can ƙuryar ɗakin ta ta shiga ta fara kai kawo cike da tunanin kan mataki na gaba da zata ɗauka wajen cigaba da tsare Falmata dan kada a samu wani lamari ya gifta da asirin ta zai shiga hatsarin tonuwa
A ɗan firgice ta waiga jin motsin shigowa ɗakin Hafsatouwa ce ta ƙaraso gaban ta da sassarfa bayan ta rufe ƙofar .
"Hafsatouwa sirrina yana cikin haɗari ya zama dole ki shirya ki tafi Zuru wajen mai jar-tawada ki amso min wani gagarumin aikin da zai kurumtar , ya makantar idan ya kama ya gurguntar da duk wasu da zasu iya kawo min tsaiko kan ƙudiri na ne ma duk ayi .
" a min aikin da zai shafe tunanin ita kan ta yarinyar nan da ta san sirrin na sannan a mantar da duk wasu makusanta nata daga tunanin ta har sai lokacin da na gaji dan kaina da hukunta ta na sake ta , ke Hansatouwa ina so na zama ni nice , kowa kuma ya zama ba kowa ba , ina nufin kowa da kowa na cikin masarautar Maradi su dawo ƙasan iko na a baɗini da fatan kin gane ?
Cike da jin tsoron yanayin da take hango uwargiyar ta a ciki hafsatouwa ta shiga gyaÉ—a kan ta .
"Oumarnin ki abun bi ne ranki shidaÉ—e uwargijiya ta mai girma .
"Da kyau to ya ya kin yi abunda nace kiyi ?
"Ranki ya daÉ—e tuni nayi .
"Kin ji motsin ta ko kaÉ—an daga inda take ?
" ba wata alama dake nuni da cewa akwai rayayyen mahaluki a bigiren da alama yarinyar bata da taurin kai .
"Idan ta yi haka ta sauƙaƙawa kan ta riskar wasu daga cikin tarin horon da nake mata tanadin su .
"Kina iya tafiya yanzu , idan buƙatar son ganin ki ya zo zan aika a min ƙiran ki .
" To ranki ya daÉ—e godiya nake .
Gaf da Azahar bayan hankulan mafi yawan mutanen gida ya tafi ga haramar sallah Hajiya Mama ta kashe jiki ta nufi tsohon sashin babar ta kuma Uwargidan Sarki Azizou Baskore "Hajiya Uwa .
Da tun bayan rasuwar ta sama da shekaru goma sha takwas babu wanda ya sake zama a sashin ya zama tamkar kufai , sai fa Hajiya Mama da jifa-jifa take zuwa sashin tana yin wasu abubuwan da ta ce raya sashin take yi da yake a matsayin na uwa a gare ta wanda kuma a baɗini daga Allah sai ita sai kuma tsirarun mutanen da tayi haɗakar ƙulla sirrukan ta da su , suka san ainashin abunda take aikata a sashin a duk ƙarshen kowanne wata .
Bayan ta gama nazarin wajen ta tabbatar babu wani mahaluki a wajen da zai iya jin abunda za ta yi ta sanya ɗan makulli ta buɗe ƙofar falon bayan ta ɗau wata leda da take yashe daga kusa da ƙofar .
Kan ta tsaye ta shiga falon ta tura ƙofar ta rufe tana mayar da ganin ta kan Falmata wacce take takure daga can gefe cikin datti da ƙurar da ta maye gurbin shimfiɗar ɗakin ya zama duk inda ka ɗora ganin ka datti ne da tankaɗaɗɗiyar ƙasa kamar an kwaso an zuba ba'a ko iya ganin ainashin dandaryar ɗakin .
A hankali Falmata ta É—ago kan ta dake tsakanin cinyoyin ta da ta haÉ—a su ta takure ba'a ce mai ciki bace .
Taku tayi ta ƙarasa gaban Falmata tashin sautin ta ya biyo bayan ledar da ta wurgawa Falmata
" wataƙila kina jin yunwa ki ɗau abinci ki ci ya rage naki ki cinye shi duk ko kuma ki rage dan anjima .
Falmata da fuskar ta ta kumbura saboda kuka ta buÉ—e bakin ta da take ji ya mata nawi muryar ta bata fita sosai tace "Sallah nake so nayi ki nuna min wajen da zan yi Alwala .
Wani kallon banza Hajiya Mama ta mata kafin ta ƙuta , sai da ta mula sannan tace " ga rairayi nan kina zaune a cikin sa ki buga ƙasa kiyi taimama .
Bata jira ba ta cigaba da cewa " ina sake jaddada miki muddin kina son tsira da rayuwar ki to ki kiyaye abunda zai sa a san kina nan , idan kuwa kin ƙi ji .?
Da zubowar sabbin hawaye Falmata tace "Hajiya Dan Allah ki tausaya min , ki ji tsoron Allah mahalicci da yake kallo tare da jin kowa da kome , ban yi miki kome ba .....
"Ke .
Hajiya Mama ta daka mata tsawar da ya sa Falmata yin shiru " kina son karya doka ta ne ?
Da sauri Falmata ta girgiza kai .
"Tashi , tashi nace ko ?
Da kyar Falmata ta miƙe saboda ƙafar ta da ta ji ciwo a jiya ga yunwa da ƙishirwa , sun sa har jiri take ji bayan ciwo mai tsanani da kan ta yake yi , ta ɗingisa dakyar ta bi bayan Hajiya Mama wacce tayi gaba zuwa wata ƙofa ran ta cike da fatan "Allah yasa afuwa zata mata ta fitar da ita daga wannan wajen .
Da kallo ta bi ɗakin da su shiga wanda ba kome a cikin sa bayan tulin ƙura da yanar-gizon da ya zarta na falon sai fa wani karmamin gadon katako da duk gara ta cinye shi shi ɗaya ƙwal a ɗakin.
"Anan za ki cigaba da zama , ga banÉ—aki nan a ciki amma bani da tabbacin rasa macizai da kunamu a ciki sai ki kula wajen amfani da shi idan ba haka ba kin ga sun hutar da ni daga kashe ki.
Daga haka Hajiya mama ta juya da kusan tare suka juya da Falmata wacce ta zube a ƙasa tana wani irin kuka ta riƙe ƙafar Hajiya Mama tana shisshiƙa kamar ran ta zai fita tace "Hajiya Dan Allah , Allah .....
Hanɓare ta Hajiya Mama tayi ta taka da sauri kafin Falmata ta yunkura ta fita ta rufo ƙofar ta murɗa ɗan makulli .
Tare suke da page 51b
[2/27, 9:35 PM] +234 706 503 6187: MAFARI
( hargitsin Rayuwa )
Umm"muaz
51b
Duk yadda Maimartaba yake tunanin za'a yi samu wata alama da zai nuna ina Falmata take anyi amma babu nasara har aka kwana aka yini babu wani bayani takamaimai na inda take .
Zuwa lokacin kuwa Biyamuradi Youssouf gaba É—aya ya gama birkice musu ya kuma matsa lamba kan son zuwa Niamey wajem Maimounatou dan ta faÉ—i inda ta kai Falmata.
Hajiya Umma ta yunƙuro zata yi magana da hannu Maimartaba ya dakatar da ita .
"Me yake Faruwa a gidan da ni ban kai ga sani ba ? Waye yake tozarta Al'umma ciki har ma da mutanen da suke amintattun mu da muka amso amarnar su daga hannun mutanen su ?
Shiru aka yi babu mai tsaurin idon iya amsawa .
Kamar daga sama Muryar Youssouf ta ratso wajen inda yake cewa " Fatima ba gudu tayi ba babu makawa É—auke ta aka yi ..
Ya ɗan jinkirta lokacin da idanun kowa ya dawo kan shi zuciyar Hajiya Mama ta fara sauya ƙarfin bugu tana dik-dik-dirim-dim.
"Wa kake tunanin ya É—auke ta ?
Maimartaba ya furta haka cike da nazarin sa ,
Shiru yayi da yasa gumi ya shiga zarya ta cikin rigar Hajiya Mama .
"Maimounatou .
Ya furta hakan da tasowar matsanancin ɓacin rai a muryar sa , ya cigaba da cewa
"Maimounatou ita ta sanya a zo a É—auke Fatima domin cikar burin ta ta wani fanni sai dai a wannan karon ba zan kyale ta ba dole ne na gwada mata ainashin É—abi'ar da na É—au shekaru a wajen koyar ta cikin aikina na na soji .
Muryar Hajiya Mama ita ta ratso wajen cike da wani boyayyen farin-ciki a sautin ta tace " Yarima ni da kaina tunanin da ya fara zowar min kenan ba shakka wannan ɗiyar ta Agades ita ta sanya anka ɗauke wannan yarinya ta ƙwarai kuma dole ayi hanzarin ɗaukar mataki akan haka.
Shiru Maimartaba yayi cikin son yin nazari sai dai hayaniyar da ta fara tashi a tsakanin iyalan sa da duk suka aminta da cewa Maimounatou ce ta tura aka sace Falmata duk kuwa da babu hujja ɗaya da aka samu wanda yake bada tabbaci ga hakan ya dukusar da hanzarin sa musamman lokacin da Youssouf ya miƙe a safure ya taho gaban shi yayi gurfano .
"Ranka shi daÉ—e zan tai Niamey yanzu zan tai na tadda Maimounatou ta faÉ—a min ina ta kai iyalina ?
"Youssoufa ka nutsu wannan batu ne da yake buƙatar nutsuwa da tsawaita bincike , ina maka oumarni da ka jinkirta hanzarin da kake yi har a ƙarƙare bincike a samu madogara .
Da kyar Maimartaba ya shawo kan hayaniyar su bayan ya tabbatar da za'a tsananta bincike kafin tunkarar koma waye da aka samu shaidar yana da hannu a ɓatan Falmata
Bayan fitar su daga Sashin Maimartaba Hajiya Mama bata koma sashin Hajiya Umma ba kai tsaye sashin ta ta koma ba tare da ta zauna cikin 'ya'yan ta da suke ta hira kan batun ɓacewar Matar Youssouf da wasu daga ciki ma daɗin lamarin suke ji saboda ta riga ta gina ƙaƙƙarfar ƙiyayya tsakanin su da Youssouf da duk wani abu na bakin-ciki da zai faru da shi su murna suke yi .
Can ƙuryar ɗakin ta ta shiga ta fara kai kawo cike da tunanin kan mataki na gaba da zata ɗauka wajen cigaba da tsare Falmata dan kada a samu wani lamari ya gifta da asirin ta zai shiga hatsarin tonuwa
A ɗan firgice ta waiga jin motsin shigowa ɗakin Hafsatouwa ce ta ƙaraso gaban ta da sassarfa bayan ta rufe ƙofar .
"Hafsatouwa sirrina yana cikin haɗari ya zama dole ki shirya ki tafi Zuru wajen mai jar-tawada ki amso min wani gagarumin aikin da zai kurumtar , ya makantar idan ya kama ya gurguntar da duk wasu da zasu iya kawo min tsaiko kan ƙudiri na ne ma duk ayi .
" a min aikin da zai shafe tunanin ita kan ta yarinyar nan da ta san sirrin na sannan a mantar da duk wasu makusanta nata daga tunanin ta har sai lokacin da na gaji dan kaina da hukunta ta na sake ta , ke Hansatouwa ina so na zama ni nice , kowa kuma ya zama ba kowa ba , ina nufin kowa da kowa na cikin masarautar Maradi su dawo ƙasan iko na a baɗini da fatan kin gane ?
Cike da jin tsoron yanayin da take hango uwargiyar ta a ciki hafsatouwa ta shiga gyaÉ—a kan ta .
"Oumarnin ki abun bi ne ranki shidaÉ—e uwargijiya ta mai girma .
"Da kyau to ya ya kin yi abunda nace kiyi ?
"Ranki ya daÉ—e tuni nayi .
"Kin ji motsin ta ko kaÉ—an daga inda take ?
" ba wata alama dake nuni da cewa akwai rayayyen mahaluki a bigiren da alama yarinyar bata da taurin kai .
"Idan ta yi haka ta sauƙaƙawa kan ta riskar wasu daga cikin tarin horon da nake mata tanadin su .
"Kina iya tafiya yanzu , idan buƙatar son ganin ki ya zo zan aika a min ƙiran ki .
" To ranki ya daÉ—e godiya nake .
Gaf da Azahar bayan hankulan mafi yawan mutanen gida ya tafi ga haramar sallah Hajiya Mama ta kashe jiki ta nufi tsohon sashin babar ta kuma Uwargidan Sarki Azizou Baskore "Hajiya Uwa .
Da tun bayan rasuwar ta sama da shekaru goma sha takwas babu wanda ya sake zama a sashin ya zama tamkar kufai , sai fa Hajiya Mama da jifa-jifa take zuwa sashin tana yin wasu abubuwan da ta ce raya sashin take yi da yake a matsayin na uwa a gare ta wanda kuma a baɗini daga Allah sai ita sai kuma tsirarun mutanen da tayi haɗakar ƙulla sirrukan ta da su , suka san ainashin abunda take aikata a sashin a duk ƙarshen kowanne wata .
Bayan ta gama nazarin wajen ta tabbatar babu wani mahaluki a wajen da zai iya jin abunda za ta yi ta sanya ɗan makulli ta buɗe ƙofar falon bayan ta ɗau wata leda da take yashe daga kusa da ƙofar .
Kan ta tsaye ta shiga falon ta tura ƙofar ta rufe tana mayar da ganin ta kan Falmata wacce take takure daga can gefe cikin datti da ƙurar da ta maye gurbin shimfiɗar ɗakin ya zama duk inda ka ɗora ganin ka datti ne da tankaɗaɗɗiyar ƙasa kamar an kwaso an zuba ba'a ko iya ganin ainashin dandaryar ɗakin .
A hankali Falmata ta É—ago kan ta dake tsakanin cinyoyin ta da ta haÉ—a su ta takure ba'a ce mai ciki bace .
Taku tayi ta ƙarasa gaban Falmata tashin sautin ta ya biyo bayan ledar da ta wurgawa Falmata
" wataƙila kina jin yunwa ki ɗau abinci ki ci ya rage naki ki cinye shi duk ko kuma ki rage dan anjima .
Falmata da fuskar ta ta kumbura saboda kuka ta buÉ—e bakin ta da take ji ya mata nawi muryar ta bata fita sosai tace "Sallah nake so nayi ki nuna min wajen da zan yi Alwala .
Wani kallon banza Hajiya Mama ta mata kafin ta ƙuta , sai da ta mula sannan tace " ga rairayi nan kina zaune a cikin sa ki buga ƙasa kiyi taimama .
Bata jira ba ta cigaba da cewa " ina sake jaddada miki muddin kina son tsira da rayuwar ki to ki kiyaye abunda zai sa a san kina nan , idan kuwa kin ƙi ji .?
Da zubowar sabbin hawaye Falmata tace "Hajiya Dan Allah ki tausaya min , ki ji tsoron Allah mahalicci da yake kallo tare da jin kowa da kome , ban yi miki kome ba .....
"Ke .
Hajiya Mama ta daka mata tsawar da ya sa Falmata yin shiru " kina son karya doka ta ne ?
Da sauri Falmata ta girgiza kai .
"Tashi , tashi nace ko ?
Da kyar Falmata ta miƙe saboda ƙafar ta da ta ji ciwo a jiya ga yunwa da ƙishirwa , sun sa har jiri take ji bayan ciwo mai tsanani da kan ta yake yi , ta ɗingisa dakyar ta bi bayan Hajiya Mama wacce tayi gaba zuwa wata ƙofa ran ta cike da fatan "Allah yasa afuwa zata mata ta fitar da ita daga wannan wajen .
Da kallo ta bi ɗakin da su shiga wanda ba kome a cikin sa bayan tulin ƙura da yanar-gizon da ya zarta na falon sai fa wani karmamin gadon katako da duk gara ta cinye shi shi ɗaya ƙwal a ɗakin.
"Anan za ki cigaba da zama , ga banÉ—aki nan a ciki amma bani da tabbacin rasa macizai da kunamu a ciki sai ki kula wajen amfani da shi idan ba haka ba kin ga sun hutar da ni daga kashe ki.
Daga haka Hajiya mama ta juya da kusan tare suka juya da Falmata wacce ta zube a ƙasa tana wani irin kuka ta riƙe ƙafar Hajiya Mama tana shisshiƙa kamar ran ta zai fita tace "Hajiya Dan Allah , Allah .....
Hanɓare ta Hajiya Mama tayi ta taka da sauri kafin Falmata ta yunkura ta fita ta rufo ƙofar ta murɗa ɗan makulli .
Tare suke da page 51b
[2/27, 9:35 PM] +234 706 503 6187: MAFARI
( hargitsin Rayuwa )
Umm"muaz
51b
Duk yadda Maimartaba yake tunanin za'a yi samu wata alama da zai nuna ina Falmata take anyi amma babu nasara har aka kwana aka yini babu wani bayani takamaimai na inda take .
Zuwa lokacin kuwa Biyamuradi Youssouf gaba É—aya ya gama birkice musu ya kuma matsa lamba kan son zuwa Niamey wajem Maimounatou dan ta faÉ—i inda ta kai Falmata.