Sashe 260
Mafari Hargitsin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tana shiga wayar ta ta ɗauka ta ƙira Amnee suka gaisa wacce ta dunga mata nasiha tana kwantar mata da hankali kan dawowar Sofi a ƙarshe ta miƙawa Mamar su wayar .
Suka gaisa kafin su yi 'yar hira da rabin ta labarin diramar Bulama ne wanda aka kai shi makarantar kwana ta firamari amma ya gudo da kukan sa da kome a cewar sa ba zai iya barin Mamar Bulama ba .
Yakaka ta yi ta dariya tana jin ƙauna tare da tausayin ƙanin ta wanda ba su wani shaƙu da juna ba.
A ƙarshe suka yi Sallama tana sauƙe wayar ta ƙira Falmata nan ma hirar suka sha sai dai a cikin muryar Falmatan ta iya jin tana da damuwa da nan take hankalin ta ya tashi dan haka ta matsa mata kan sai faɗa mata me yake damun ta ? Ko haihuwar ce ta zo ?
Falmata bata ɓoyewa Yakaka kome nan ta faɗa mata irin matsananciyar damuwar da take ciki kan barin ta da Youssouf yayi ya tafi wajen aiki ta ɗora da cewa "kuma fa Yakaka sau uku kawai muke waya a rana kuma sau biyu kawai muke Appel vidéo a rana kafin ya tafi kuma ba haka ya min alƙawari ba cewa yayi kawai koyaushe yana tare da ni .
Shiru Yakaka tayi tana jinjina rikicin Falmata a zuciyar ta kafin ta ce "Falmata waya har sau uku a rana ? Ga kuma vidieo call ? Sau biyar fa kenan kike jin sa bai yi yawa ba Falmata ?
Kin san fa tare da matar sa yake a can , sannan ita ma tana da hakki a kan sa bakya ganin za ki shiga hakkin ta dayawa idan ya zama koyaushe kuna tare a waya ? Ni dai fatana Allah yasa bakwa doguwar wayar dare Falmata abunda duk ba za ka so ayi ma ba kar fa ka yiwa wanin ka '
Tsit Falmata tayi daga can tana É—an turo baki kamar Yakaka na ganin ta sai cewa tayi "to ai nima ina da hakkin ni ba barina yayi ba ma gaba É—aya ya tafi da ita ba ? ina cewa kullum tare suke kwana ? Meye dan kawai mun yi waya ?
Yakaka tana danne dariyar ta ta ce "a ah wallahi da kome muddin aka ce za ki dunga ratsa tsakanin lokutan da ya kamata ace yana tare da ita to ba shakka kina shiga hakkin ta haba mana Falmata ban fa san ki da zalunci ba , dan Miji yafi son ki kar ki yadda ki biye masa ya dunga ƙuntatawa matar sa .
Ni yanzu da Yaya dakta yafi son Sofi akaina za ki so ya dunga min abunda babu daÉ—i akan ta ?
Girgiza kai Falmata tayi tana jin duk jikinta yayi sanyi ta ce "ki daina cewa haka Yakaka Yaya dakta yana son ki ba zai taɓa walakanta ki akan Sofi ba.
"Kuma nima ba wai so nake ya dunga walakanta matar sa akaina ba kawai dai.
ÆŠan shiru tayi tana numfasawa kafin ta ce "Yakaka ina son shi ne dayawa zuciyata tana min ciwo idan har na tuno yana can tare da ita ni kuma ga ni nan da ciki himm ina fama.
"Ki rage kishi Falmata kowacce mace tana son Mijinta amma domin a zauna lafiya babu cutarwa sai a dunga sassautawa ana tausar zuciya kin jin ko Gimbiya Falmata., ke ce fa Uwargidan Sarki watarana uwayen gida da kawaici aka san su domin suke jagorar Gida .
Sassauƙar dariya Falmata tayi tana jin ranta na yin sanyi ƙaunar 'yar uwar ta na kawo mata
****
Kafin cikar sati ƙarfi da yaji Yakaka ta koma zaman ɗaki saboda yadda Sofi ta kasa ta tsare alhalin ta san Yakaka tana matuƙar shakkun ta .
Muddin ta fito falo to aiki za tayi ta bar wajen ko kuma idan Doctor Hamza yana nan wanda shi bai san yadda yinin su yake kasancewa ba idan baya gidan .
Babu abinda yafi daÉ—a tayarwa da Yakaka hankali irin ji da tayi Doctor Hamza a jiya da dare yace cikin kwanaki biyu masu zuwa zai yi tafiya zuwa jahar Kano za shi asibitin koyarwa na Kano yin wani aiki na kwanaki uku "kenan zai bar su daga ita sai Sofi a gidan 'yar sakewar ma da take samu tayi a cikin awowi ishirin da huÉ—un idan yana nan zasu zama babu .
Hakan ya daɗa sanyayar mata da jiki har wani ɗan zazaaɓi take ji yana kama ta bayan bugun zuciyar ta da take ji yana sauyawa a bayan kowacce sa'a ɗaya ga kasala da ta dirar mata .
Bayan fitar sa aiki da ƙyar ta iya lallaɓawa ta fito yin girkin rana da ta san Sofi za ta iya buƙata ba wai dan cikin ta ba saboda ita gaba ɗaya ma yau tunda ta tashi bata sha'awar kome dan ko da suka zauna karin kumallo bata iya cin kome ba sai ruwan shai da ta zubawa cikin ta.
Ba irin rarrashin da Doctor Hamza bai mata ba kan ta ci abinci amma ta gagara dan kan shi yayi shiru ya bar ta bayan ya gama nazarin ta.
Fitowar ta daga ɗakin ya zo lokaci guda da ƙwanƙwasa ƙofar gidan da aka yi dan haka ta ɗan saurara jin ana sake ƙwanƙwasawa yasa ta taho ta buɗe ƙofar .
Musayar kallo suka yi ita da wacce take tsaye a dokin ƙofar tana jifan ta da siririn murmushi mai tarin ma'anoni .
An-anty Samy .
Ta ambata a harÉ—e ,
"Yaks Amarya a gidan Doctor , matsa min hanya mana na wuce ko kuwa na koma ne ba'a maraba da ni ?
Da sauri ta matsa tana girgiza kai da 'yar fara'a tace "a ah ina maraba da ke mana Anty Samy sannu da zuwa .
Tayi gaba Samy baby ta bi bayan ta tana ƙare mata kallo .
Suna ƙarasawa tsakiyar Falon Sofi na sauƙowa daga sama wata 'yar shewa suka yi ita da Samy Baby kafin su taho su rungume juna suna 'yan ƙananun maganganun su na shaiɗana .
Samy baby za ta zauna Sofi tayi maza ta hana ta "friend me za ki zauna yi anan ? Ta shi mu tafi sama akwai muhimman maganganun da kin san nan ba muhallin yin su bane ba .
"Ok friend
Samy baby ta furta haka tana miƙewa tsaye ta ɗau jakar ta kafin ta mayar da ganin ta kan Yakaka wacce take rakuɓe a gefe wata 'yar iskar dariya tayi mai kama da shewa
"Hehehe Yaks kenan ka ga manyan amare masu harin miƙamin uwargida an gaishe ki Yaks da tsaurin ido .
Shiru Yakaka tayi bata ce ƙala ba gaisuwar da ta yi niyyar yi ma ta fasa jin yadda Samy Baby take mata ba'a sarai ta fahimta .
Kitchen ta koma su kuma su ka hau sama suna shiga É—aki Samy Baby ta lailayo wata ashariya ta kwatsawa Sofi .
"Kina me Sofi ? Nace kina me har kika bari yarinyar nan ta samu sakewar da zata fara haramar ajiye ƙwai a gidan nan ? Na shiga uku Sofi ina mai tabbatar miki taki ta kusan ƙarewa a gidan nan .....
Sofi da lokaci ɗaya ta diririce idanun ta suka sake shigewa ciki da in'ina a muryar ta tace "me..me ..kika ce ban..ban fahimta ba wanne irin ƙwai kuma kamar wata kaza'
"Yo ai ga ki nan babbar kaza Sofi tunda har kika kasa gane Yarinyar nan Yaks tana da shigar ciki kike zaune baki sake baki É—au kowanne irin mataki ba...
Bata ankara ba ta ji Sofi ta sakar mata Mari da yasa shiru ya gifta wajen .
Kafin ta tsinkayo muryar Sofi tana cewa "kar ki sake min wannan mummunan Fatan mummunan zancen ,
"kin yi hauka ne Sofi za ki mare ni ?
"A turu nake Samira ya za ki zo kina barazanar fasa min zuciya da mugun fata ki sa na faɗi na mutu tun kwanana bai ƙare ba .
Gyara fuska Samy Baby tana ƙoƙarin shanye fushin ta saboda tarkon da take son ɗanawa kar ya lalace ta sassauta muryar tace
"Wallahi tallahi I swear Sofi Yarinyar nan ciki ne da ita ki nutsu ki dawo hankalin ki tun wuri mu yiwa tufka hanci kafi....
Wani razanannan ihu da Sofi tayi da ya amsa gidan gaba ɗaya sai da yasa Yakaka wacce take kitchen ta zabura tana dafe ƙirji a take taji zuciyar ta ta hautsina da daman tunda tafara girkin warin Albasa ke ɗaga mata hankali.
Ba shiri ta bar baro kitchen ta wuce É—aki tana mayar da numfashi "anya Sofi kan ta É—aya ?
"Samira da gaske kike ? da gaske kike da gaske ?
Kamar an safure ta ta miƙe tayi hanyar fita daga ɗakin da gudu Samy baby ta bita ta riƙo ta .
Kufcewa tayi tana watsa mata wani mugun kallo kafin cikin muryar da ta buÉ—u kamar ba ta ta ba tace "ki bar ni naje na kashe ta na farka mata ciki na zo miki da É—an tayin cikin na ta wallahi sai na kashe ta.
Kallon baki da hankali Samy baby ta jefa mata kafin ta ce .
"Dallah Sofi ki nutsu ya kike abu kamar wacce ba tayi karatu ba ? Kina abu kamar wata jahila kina tunanin yanzu idan kika je kika kashe 'yar mutane ke ma za ki rayu da Hamzan ne ba tare da an miki É—aurin rai da rai ba ko kuwa ke ma a kashe ki.
"Na yarda a kashe ni idan na kashe ta akan dai mu rayu ni da ita alhalin ta raba ni da farin-ciki na ina ji ina gani bakin-ciki zai kashe ni na mutu na bar mata duniyar su rayu ita da Mijina .
"Na yarda za ta mutu amma ba ta irin wannan hanyar da kike son bi ba ko da kashe ta kike son yi ki bari sai an kauda-bara ta yadda za ki kashe ba tare da an samu mai iya É—aga ido ya dube ki ba ko kuwa ma kawai a mata abunda zai kashe ta ba tare da an zarge ki ba .
"Ta yaya faÉ—a min hanyar ?
Suka gaisa kafin su yi 'yar hira da rabin ta labarin diramar Bulama ne wanda aka kai shi makarantar kwana ta firamari amma ya gudo da kukan sa da kome a cewar sa ba zai iya barin Mamar Bulama ba .
Yakaka ta yi ta dariya tana jin ƙauna tare da tausayin ƙanin ta wanda ba su wani shaƙu da juna ba.
A ƙarshe suka yi Sallama tana sauƙe wayar ta ƙira Falmata nan ma hirar suka sha sai dai a cikin muryar Falmatan ta iya jin tana da damuwa da nan take hankalin ta ya tashi dan haka ta matsa mata kan sai faɗa mata me yake damun ta ? Ko haihuwar ce ta zo ?
Falmata bata ɓoyewa Yakaka kome nan ta faɗa mata irin matsananciyar damuwar da take ciki kan barin ta da Youssouf yayi ya tafi wajen aiki ta ɗora da cewa "kuma fa Yakaka sau uku kawai muke waya a rana kuma sau biyu kawai muke Appel vidéo a rana kafin ya tafi kuma ba haka ya min alƙawari ba cewa yayi kawai koyaushe yana tare da ni .
Shiru Yakaka tayi tana jinjina rikicin Falmata a zuciyar ta kafin ta ce "Falmata waya har sau uku a rana ? Ga kuma vidieo call ? Sau biyar fa kenan kike jin sa bai yi yawa ba Falmata ?
Kin san fa tare da matar sa yake a can , sannan ita ma tana da hakki a kan sa bakya ganin za ki shiga hakkin ta dayawa idan ya zama koyaushe kuna tare a waya ? Ni dai fatana Allah yasa bakwa doguwar wayar dare Falmata abunda duk ba za ka so ayi ma ba kar fa ka yiwa wanin ka '
Tsit Falmata tayi daga can tana É—an turo baki kamar Yakaka na ganin ta sai cewa tayi "to ai nima ina da hakkin ni ba barina yayi ba ma gaba É—aya ya tafi da ita ba ? ina cewa kullum tare suke kwana ? Meye dan kawai mun yi waya ?
Yakaka tana danne dariyar ta ta ce "a ah wallahi da kome muddin aka ce za ki dunga ratsa tsakanin lokutan da ya kamata ace yana tare da ita to ba shakka kina shiga hakkin ta haba mana Falmata ban fa san ki da zalunci ba , dan Miji yafi son ki kar ki yadda ki biye masa ya dunga ƙuntatawa matar sa .
Ni yanzu da Yaya dakta yafi son Sofi akaina za ki so ya dunga min abunda babu daÉ—i akan ta ?
Girgiza kai Falmata tayi tana jin duk jikinta yayi sanyi ta ce "ki daina cewa haka Yakaka Yaya dakta yana son ki ba zai taɓa walakanta ki akan Sofi ba.
"Kuma nima ba wai so nake ya dunga walakanta matar sa akaina ba kawai dai.
ÆŠan shiru tayi tana numfasawa kafin ta ce "Yakaka ina son shi ne dayawa zuciyata tana min ciwo idan har na tuno yana can tare da ita ni kuma ga ni nan da ciki himm ina fama.
"Ki rage kishi Falmata kowacce mace tana son Mijinta amma domin a zauna lafiya babu cutarwa sai a dunga sassautawa ana tausar zuciya kin jin ko Gimbiya Falmata., ke ce fa Uwargidan Sarki watarana uwayen gida da kawaici aka san su domin suke jagorar Gida .
Sassauƙar dariya Falmata tayi tana jin ranta na yin sanyi ƙaunar 'yar uwar ta na kawo mata
****
Kafin cikar sati ƙarfi da yaji Yakaka ta koma zaman ɗaki saboda yadda Sofi ta kasa ta tsare alhalin ta san Yakaka tana matuƙar shakkun ta .
Muddin ta fito falo to aiki za tayi ta bar wajen ko kuma idan Doctor Hamza yana nan wanda shi bai san yadda yinin su yake kasancewa ba idan baya gidan .
Babu abinda yafi daÉ—a tayarwa da Yakaka hankali irin ji da tayi Doctor Hamza a jiya da dare yace cikin kwanaki biyu masu zuwa zai yi tafiya zuwa jahar Kano za shi asibitin koyarwa na Kano yin wani aiki na kwanaki uku "kenan zai bar su daga ita sai Sofi a gidan 'yar sakewar ma da take samu tayi a cikin awowi ishirin da huÉ—un idan yana nan zasu zama babu .
Hakan ya daɗa sanyayar mata da jiki har wani ɗan zazaaɓi take ji yana kama ta bayan bugun zuciyar ta da take ji yana sauyawa a bayan kowacce sa'a ɗaya ga kasala da ta dirar mata .
Bayan fitar sa aiki da ƙyar ta iya lallaɓawa ta fito yin girkin rana da ta san Sofi za ta iya buƙata ba wai dan cikin ta ba saboda ita gaba ɗaya ma yau tunda ta tashi bata sha'awar kome dan ko da suka zauna karin kumallo bata iya cin kome ba sai ruwan shai da ta zubawa cikin ta.
Ba irin rarrashin da Doctor Hamza bai mata ba kan ta ci abinci amma ta gagara dan kan shi yayi shiru ya bar ta bayan ya gama nazarin ta.
Fitowar ta daga ɗakin ya zo lokaci guda da ƙwanƙwasa ƙofar gidan da aka yi dan haka ta ɗan saurara jin ana sake ƙwanƙwasawa yasa ta taho ta buɗe ƙofar .
Musayar kallo suka yi ita da wacce take tsaye a dokin ƙofar tana jifan ta da siririn murmushi mai tarin ma'anoni .
An-anty Samy .
Ta ambata a harÉ—e ,
"Yaks Amarya a gidan Doctor , matsa min hanya mana na wuce ko kuwa na koma ne ba'a maraba da ni ?
Da sauri ta matsa tana girgiza kai da 'yar fara'a tace "a ah ina maraba da ke mana Anty Samy sannu da zuwa .
Tayi gaba Samy baby ta bi bayan ta tana ƙare mata kallo .
Suna ƙarasawa tsakiyar Falon Sofi na sauƙowa daga sama wata 'yar shewa suka yi ita da Samy Baby kafin su taho su rungume juna suna 'yan ƙananun maganganun su na shaiɗana .
Samy baby za ta zauna Sofi tayi maza ta hana ta "friend me za ki zauna yi anan ? Ta shi mu tafi sama akwai muhimman maganganun da kin san nan ba muhallin yin su bane ba .
"Ok friend
Samy baby ta furta haka tana miƙewa tsaye ta ɗau jakar ta kafin ta mayar da ganin ta kan Yakaka wacce take rakuɓe a gefe wata 'yar iskar dariya tayi mai kama da shewa
"Hehehe Yaks kenan ka ga manyan amare masu harin miƙamin uwargida an gaishe ki Yaks da tsaurin ido .
Shiru Yakaka tayi bata ce ƙala ba gaisuwar da ta yi niyyar yi ma ta fasa jin yadda Samy Baby take mata ba'a sarai ta fahimta .
Kitchen ta koma su kuma su ka hau sama suna shiga É—aki Samy Baby ta lailayo wata ashariya ta kwatsawa Sofi .
"Kina me Sofi ? Nace kina me har kika bari yarinyar nan ta samu sakewar da zata fara haramar ajiye ƙwai a gidan nan ? Na shiga uku Sofi ina mai tabbatar miki taki ta kusan ƙarewa a gidan nan .....
Sofi da lokaci ɗaya ta diririce idanun ta suka sake shigewa ciki da in'ina a muryar ta tace "me..me ..kika ce ban..ban fahimta ba wanne irin ƙwai kuma kamar wata kaza'
"Yo ai ga ki nan babbar kaza Sofi tunda har kika kasa gane Yarinyar nan Yaks tana da shigar ciki kike zaune baki sake baki É—au kowanne irin mataki ba...
Bata ankara ba ta ji Sofi ta sakar mata Mari da yasa shiru ya gifta wajen .
Kafin ta tsinkayo muryar Sofi tana cewa "kar ki sake min wannan mummunan Fatan mummunan zancen ,
"kin yi hauka ne Sofi za ki mare ni ?
"A turu nake Samira ya za ki zo kina barazanar fasa min zuciya da mugun fata ki sa na faɗi na mutu tun kwanana bai ƙare ba .
Gyara fuska Samy Baby tana ƙoƙarin shanye fushin ta saboda tarkon da take son ɗanawa kar ya lalace ta sassauta muryar tace
"Wallahi tallahi I swear Sofi Yarinyar nan ciki ne da ita ki nutsu ki dawo hankalin ki tun wuri mu yiwa tufka hanci kafi....
Wani razanannan ihu da Sofi tayi da ya amsa gidan gaba ɗaya sai da yasa Yakaka wacce take kitchen ta zabura tana dafe ƙirji a take taji zuciyar ta ta hautsina da daman tunda tafara girkin warin Albasa ke ɗaga mata hankali.
Ba shiri ta bar baro kitchen ta wuce É—aki tana mayar da numfashi "anya Sofi kan ta É—aya ?
"Samira da gaske kike ? da gaske kike da gaske ?
Kamar an safure ta ta miƙe tayi hanyar fita daga ɗakin da gudu Samy baby ta bita ta riƙo ta .
Kufcewa tayi tana watsa mata wani mugun kallo kafin cikin muryar da ta buÉ—u kamar ba ta ta ba tace "ki bar ni naje na kashe ta na farka mata ciki na zo miki da É—an tayin cikin na ta wallahi sai na kashe ta.
Kallon baki da hankali Samy baby ta jefa mata kafin ta ce .
"Dallah Sofi ki nutsu ya kike abu kamar wacce ba tayi karatu ba ? Kina abu kamar wata jahila kina tunanin yanzu idan kika je kika kashe 'yar mutane ke ma za ki rayu da Hamzan ne ba tare da an miki É—aurin rai da rai ba ko kuwa ke ma a kashe ki.
"Na yarda a kashe ni idan na kashe ta akan dai mu rayu ni da ita alhalin ta raba ni da farin-ciki na ina ji ina gani bakin-ciki zai kashe ni na mutu na bar mata duniyar su rayu ita da Mijina .
"Na yarda za ta mutu amma ba ta irin wannan hanyar da kike son bi ba ko da kashe ta kike son yi ki bari sai an kauda-bara ta yadda za ki kashe ba tare da an samu mai iya É—aga ido ya dube ki ba ko kuwa ma kawai a mata abunda zai kashe ta ba tare da an zarge ki ba .
"Ta yaya faÉ—a min hanyar ?