Sashe 238
Mafari Hargitsin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Cikin tsawa yace "to waye zai sace ta? Waye maƙiyi na da ya wucce ke ? Ina da wani Maƙiyi bayan ki ? Za....
"Wallahi kana da Maƙiyiyar da ta wucce ni wacce ita tayi sanadin faruwa duk wassu abubuwa marasa kyau da sun ka samu rayuwar ka .
"Wacece itta ?
Ya tambaye ta a daƙile
Da sauri ta amsa masa da "Hajiya Mama.
Yamutsa fuska yayi kamar yana son tuna inda ya taɓa jin sunan .
Ganin haka ya sa Maimounatou cigaba da cewa " Baka da wata maƙiyiyar da ta wuve Hajiya Saratu , Matar Mahaifin ku Mahaifiyar Mammadou Hajiya Mama.
"Ita ta wanzu tsawon shekaru tana bin ka da sharri da ita da Tsohuwar Matar kakan ku Hajiya Uwa su biyun sune suka fara lalata rayuwar ka ta hanyar yi maka mummunan sihiri,
" su suka sa ka zama mashayin giya "giyar burkutu , su suka sa kayi zina da yarinya Amina wacce take 'yar uwa ga É—aya daga cikin matan da za ka aura,
Su suka yi ma Asiri tun kana É—an shekaru biyar bai fara aiki ba sai da ka shekara goma sha takwas , ranar da ka cika shekaru goma sha takwas a ranar ka fara shan barasa, ranar da ka cika shekara talatin a ranar ka fara yin zina a kuma ranar ...''
Ɗago ta Youssouf yayi ya haɗa ta da jikin bango gaba ɗaya jikin sa tsuma yake cikin ɗimauta yake cewa "ƙarya kike yi , ke maƙaryaciya ce maha'inciya munafuka ki faɗa min gaskiyar aina duk kika samu wannan bayanin ? .
Idanun Maimounatou sun fito waje amma bata haƙura da magana ba ta cigaba da cewa " kuma Hajiya Mama bata daina sabunta aikin asirin ba ko bayan mutuwar Hajiya uwa babban burin su ka rasa ƙima da darajarka ta ɗan sarki da hakan zai sa ka gaza wajen hawa kujerar mulkin Maradi , a wayi gari Mammadou shi ne Sarki.
"Duk abunda nake faɗa maka a yau gaskiya ne babu ɗigon ƙarya ko ɗaya a ciki, ita da bakin ta ta faɗa min idan kuma kana son samun tabbaci da kuma hakan zai kai ga karya duk wasu sihiri da aka maka kuma har yau suke aiki a kan ka , ka koma Maraɗi ki tafi tsohon sashin Hajiya Uwa a babban falon ta cikin ɗaki na biyu daga hannu hagu ka bincika ɗakin a cikin armoire asirin da aka maka yake .
" Ka je ka fasa kome , Ka ɓata kome , muddin kana son cigaba da yin rayuwar da babu dabaibayin sihiri a cikin ta .
"A ƙarshe ina baka tabbacin Hajiya Mama tana da hannu wajen ɗarsuwar duk wani baƙin-ciki a rayuwar ka dan haka ba tamtama a wannan karon ma ita ta sace Fatima .
Sakwaf ! Youssouf ya sake ta ta faɗi a ƙasa kalamanta na ratsa duk wasu jijiyoyin cikin ƙwaƙwalwar sa suna aikawa da saƙon gaugawa zuwa cerebrum na kwakwalwar sa har zuwa temporal lobe da anan take ya fara ƙoƙarin tuno masa da duk wasu motsi da lamurarran Hajiya Mama a kan sa .
"Yadda take kyarar sa tun yana ƙanƙanin sa , da ya fara girma ya mallaki hankali sai yana lura da ko ganin sa bata son yi sannan duk wani abu na farin-ciki idan ya same shi bata taya shi murna haka kuma na baƙin ciki , kai ko jinyar da yayi na kwanan nan ma bata taɓa masa ya jiki ba , bare ta jajanta masa , a duk lamuransa idan ba ɓacewar Falmata ba bai taɓa jin ta sanya bakin ta ciki ba ya daɗe da sanin bata ƙaunar sa .
"To amma anya hakan ya isa ya sa shi yarda da cewa Hajiya Mama Matar Mahaifinsa ita ce ta sace Matar sa ?
Girgiza kan sa yayi yana jin haÉ—uwar kalaman su su biyun masu cin karo da juna a can Maradi Hajiya Mama tace Maimounatou ce ta sa aka É—auke Fatima , anan kuma Maimounatou tace Hajiya Mama ce ta sa aka É—auke Fatima .
"Waye mai gaskiya a tsakanin su ?
Abu mafi girma da ya fahimta a tsukin lokacin shine wata ɓoyayyar alaƙa da take tsakanin su biyun da bai taɓa kaiwa ga sani ba .
Kalaman Maimounatou akwai ɓurɓushin gaskiya a cikin su Musamman cikakken bayanin da tayi masa kan lokutan da munanan al'umuran da suka faru a rayuwar sa suka fara faruwa .
"Ya zama dole na koma Maradi , na koma domin samun tabbaci tsakanin ƙarya da gaskiya .
Da sasaarfa ya juya yana barin wajen , Maimounatou da take zaune dirshan a ƙasa tana mayar da numfashi cikin wata irin murya tace "Youssouf ka min afouwa ka yafe min ka sake bani dama .
Tsayuwa yayi ba tare da ya juyo ba yace "Na sake ki saki Ukku Maimounatou kada kuma kiyi fatan abunda zai sake nuna mana fuskokin juna a zahiri .
Ihun da Maimounatou ta sa sai da ya ƙarade harabar ofishin kafin ya bar da'irar wajen yana iya jiyo hargowar ta tana ƙiran sunan sa .
"Youssoufa.
"Youssoufa ka dawo wallahi nayi nadama .
Bata taɓa sanin cikin wasanni ta ta haɗo da zuciyar ta ba sai a yau da Youssoufa ya rayu bayan so da tayi ta gille masa rayuwar sa ya kuma dawo ya sake ta irin sakin da babu kome , a dai-dai lokacin da ita kuma zuciyar ta ta haƙaƙe da cewa ta daɗe cikin mayen son sa tun tana ƙaryata kan ta akan haka har a ƙarshe ta saduda ta kuma shiga addu'a ka'in da na'in Allah ya tashi kafaɗun sa ya dawo su cigaba da rayuwar su .
haƙiƙa tayi asarar Miji irin wanda ba zata samu madadin sa ba . To wa ma zai sake auren ta ?
Kenan ita bata ci ribar kome ba sai fa ta lalacewar suna a idanun al'umma ta zama mujiya abar zunÉ—e .
Zuciyar ta taji tana wani irin narkewa da nadama marar iyaka , tsoron halin da zata tafi ta tadda a rayuwar gidan su na huda ta da tun da ta kwashi tsawon satika bakwai a kulle babu wanda ya leƙo daga gidan su ko wani dangi nata ta san cewa kurar ta tayi kuka ta kuma riga ta dusashe tayi duhu a idanun kowa na ta .
Kwanciya tayi a ƙasa tana wani irin kuka tare da jin yadda zuciyar ta ke zogi kamar zata fashe a tsukin lokacin zaɓar mutuwa take son yi akan rayuwar da zata tarar a gaba .
Kai tsaye Youssoufa ainashin cikin ofishin ya koma inda ya nemi da a ba shi takaddun neman belin waÉ—an da ake tsare da su .
Baya cikin nutsuwar sa ya ciccike inda ya bada tabbacin yin afuwa ga Masu laifin su biyu da ake tuhuma da yunƙurin kashe shi a matsayin sa na wanda suka yiwa laifin ya sanya hannun ya janye ya musu afuwa a sake su .
Bayan gajerar muhawarar da Youssouf bai bada hankalin sa ba ya ƙirgo wasu kuɗaɗe ya ajiye a gaban teburin ya miƙe yana barin wajen bayan sun yi Sallama.
A waje ya tarar da Bilal cikin motar direban da Mijin Ubbo ya turo ya ɗauke su idan sun gama bai shiga motar ba ya ƙira Bilal ya fito .
"Ka shigga ciki za'a fito da Mammadou ku tafi gidan ubbo tare ni akwai inda zan tai .
Bai jira amsar sa ba ya taka da sauri yana barin wajen .
Wani ƙaramin Hotel ya je ya kama ɗaki na kwana guda (HOTÈL TÉNÉRÉ) tun da ya shiga ɗakin ya kashe wayoyin sa yayi sallah yayi zaune tunaninnika na masa rubdugu .
ji yake kamar ya buɗi ido ya gan shi a maraɗi wani irin hali ya kasance a ciki tsawon ƙarshen yinin zuwa cikin daren da ya tsinci tsawon sa fiye da na darare uku a wajen sa .
Asubar farko ya miƙa mukullin ɗakin ya bar otel zuwa tashar mota .
Mota ta farko da ta tashi zuwa Maraɗi da misalin ƙarfe shidda na safe cif sun kama hanya tare da Youssoufa da ya kasa jiran karfe biyun ranar jirgi ya tafi da shi .
Ya zaɓi tafiyar motar saboda ya san duk inda ƙarfe biyu na ranar tayi yana cikin Maraɗi .
Maradi .
Tun ajiya da Hajiya Umma da shi kan sa Maimartaba suka kasa samun layin Youssoufa suke cikin fargaba duk kuwa da cewa sun yi waya da Bilal har ma da Mammadou cewar suna lafiya kuma Youssoufa ma yana lafiya sai dai su ma basu san inda yake ba kuma basu samun wayar sa.
Bayan addu'a babu abunda Hajiya Umma take yi saboda jikin ta yana bata wani abu ya faru ko kuma zai faru ko mai kyau ko marar kyau .
kuma kawo yanzu ta fahimci ƙaunar da ɗan ta yake yiwa Falmata marar misaltuwa ce ba yadda ta iya dan dole ta fara addu'ar Allah ya bayyana Fatima ko dan Youssouf ya samu nutsuwa .
Ga Hajiya Mama kuwa yau ranar farin-ciki ce a wajen ta dan kuwa har 'yar ƙaramar walima ta haɗa na farin-cikin dawowar ɗan ta mafi soyuwa a wajen ta da aka yiwa sharri aka garƙame ta gayyaci ƙawayen ta na ƙud da ƙud dan su zo taya ta murna .
Matar Mammadou da ake ƙira Zainaba ita ma a nata gidan sai murna tare da shirin taryar Mijin ta .
Kamar kullum yau ma bayan an tafi Sallar Azahar Hajiya Mama ta kashe jiki ta nufi shiyar Hajiya Uwa ta buÉ—e ta shiga .
Ƙarfe biyu saura mintuna goma taxi da ta ɗauko Youssoufa daga tasha ta sauke sa baya cikin nutsuwar sa ya biya mai taxi .
Da sassarfa yake taku ya nufi cikin gidan kallo É—aya zaka masa ka matsa daga hanya ko da kuwa ba ka san ko shi wanene bane .
Ta gaban Fada ya zo ya wuce akan idanun Maimartaba da kowa na cikin fadar wanda hakan shine na farko da Youssoufa ya zo ya wuce ta gaban Mahaifin sa bai ƙarasa ya gaishe shi ba , abu ne da bai faruwa mutum ya taka ƙofar fada bai shiga ya kai gaisuwa ba .
"Wallahi kana da Maƙiyiyar da ta wucce ni wacce ita tayi sanadin faruwa duk wassu abubuwa marasa kyau da sun ka samu rayuwar ka .
"Wacece itta ?
Ya tambaye ta a daƙile
Da sauri ta amsa masa da "Hajiya Mama.
Yamutsa fuska yayi kamar yana son tuna inda ya taɓa jin sunan .
Ganin haka ya sa Maimounatou cigaba da cewa " Baka da wata maƙiyiyar da ta wuve Hajiya Saratu , Matar Mahaifin ku Mahaifiyar Mammadou Hajiya Mama.
"Ita ta wanzu tsawon shekaru tana bin ka da sharri da ita da Tsohuwar Matar kakan ku Hajiya Uwa su biyun sune suka fara lalata rayuwar ka ta hanyar yi maka mummunan sihiri,
" su suka sa ka zama mashayin giya "giyar burkutu , su suka sa kayi zina da yarinya Amina wacce take 'yar uwa ga É—aya daga cikin matan da za ka aura,
Su suka yi ma Asiri tun kana É—an shekaru biyar bai fara aiki ba sai da ka shekara goma sha takwas , ranar da ka cika shekaru goma sha takwas a ranar ka fara shan barasa, ranar da ka cika shekara talatin a ranar ka fara yin zina a kuma ranar ...''
Ɗago ta Youssouf yayi ya haɗa ta da jikin bango gaba ɗaya jikin sa tsuma yake cikin ɗimauta yake cewa "ƙarya kike yi , ke maƙaryaciya ce maha'inciya munafuka ki faɗa min gaskiyar aina duk kika samu wannan bayanin ? .
Idanun Maimounatou sun fito waje amma bata haƙura da magana ba ta cigaba da cewa " kuma Hajiya Mama bata daina sabunta aikin asirin ba ko bayan mutuwar Hajiya uwa babban burin su ka rasa ƙima da darajarka ta ɗan sarki da hakan zai sa ka gaza wajen hawa kujerar mulkin Maradi , a wayi gari Mammadou shi ne Sarki.
"Duk abunda nake faɗa maka a yau gaskiya ne babu ɗigon ƙarya ko ɗaya a ciki, ita da bakin ta ta faɗa min idan kuma kana son samun tabbaci da kuma hakan zai kai ga karya duk wasu sihiri da aka maka kuma har yau suke aiki a kan ka , ka koma Maraɗi ki tafi tsohon sashin Hajiya Uwa a babban falon ta cikin ɗaki na biyu daga hannu hagu ka bincika ɗakin a cikin armoire asirin da aka maka yake .
" Ka je ka fasa kome , Ka ɓata kome , muddin kana son cigaba da yin rayuwar da babu dabaibayin sihiri a cikin ta .
"A ƙarshe ina baka tabbacin Hajiya Mama tana da hannu wajen ɗarsuwar duk wani baƙin-ciki a rayuwar ka dan haka ba tamtama a wannan karon ma ita ta sace Fatima .
Sakwaf ! Youssouf ya sake ta ta faɗi a ƙasa kalamanta na ratsa duk wasu jijiyoyin cikin ƙwaƙwalwar sa suna aikawa da saƙon gaugawa zuwa cerebrum na kwakwalwar sa har zuwa temporal lobe da anan take ya fara ƙoƙarin tuno masa da duk wasu motsi da lamurarran Hajiya Mama a kan sa .
"Yadda take kyarar sa tun yana ƙanƙanin sa , da ya fara girma ya mallaki hankali sai yana lura da ko ganin sa bata son yi sannan duk wani abu na farin-ciki idan ya same shi bata taya shi murna haka kuma na baƙin ciki , kai ko jinyar da yayi na kwanan nan ma bata taɓa masa ya jiki ba , bare ta jajanta masa , a duk lamuransa idan ba ɓacewar Falmata ba bai taɓa jin ta sanya bakin ta ciki ba ya daɗe da sanin bata ƙaunar sa .
"To amma anya hakan ya isa ya sa shi yarda da cewa Hajiya Mama Matar Mahaifinsa ita ce ta sace Matar sa ?
Girgiza kan sa yayi yana jin haÉ—uwar kalaman su su biyun masu cin karo da juna a can Maradi Hajiya Mama tace Maimounatou ce ta sa aka É—auke Fatima , anan kuma Maimounatou tace Hajiya Mama ce ta sa aka É—auke Fatima .
"Waye mai gaskiya a tsakanin su ?
Abu mafi girma da ya fahimta a tsukin lokacin shine wata ɓoyayyar alaƙa da take tsakanin su biyun da bai taɓa kaiwa ga sani ba .
Kalaman Maimounatou akwai ɓurɓushin gaskiya a cikin su Musamman cikakken bayanin da tayi masa kan lokutan da munanan al'umuran da suka faru a rayuwar sa suka fara faruwa .
"Ya zama dole na koma Maradi , na koma domin samun tabbaci tsakanin ƙarya da gaskiya .
Da sasaarfa ya juya yana barin wajen , Maimounatou da take zaune dirshan a ƙasa tana mayar da numfashi cikin wata irin murya tace "Youssouf ka min afouwa ka yafe min ka sake bani dama .
Tsayuwa yayi ba tare da ya juyo ba yace "Na sake ki saki Ukku Maimounatou kada kuma kiyi fatan abunda zai sake nuna mana fuskokin juna a zahiri .
Ihun da Maimounatou ta sa sai da ya ƙarade harabar ofishin kafin ya bar da'irar wajen yana iya jiyo hargowar ta tana ƙiran sunan sa .
"Youssoufa.
"Youssoufa ka dawo wallahi nayi nadama .
Bata taɓa sanin cikin wasanni ta ta haɗo da zuciyar ta ba sai a yau da Youssoufa ya rayu bayan so da tayi ta gille masa rayuwar sa ya kuma dawo ya sake ta irin sakin da babu kome , a dai-dai lokacin da ita kuma zuciyar ta ta haƙaƙe da cewa ta daɗe cikin mayen son sa tun tana ƙaryata kan ta akan haka har a ƙarshe ta saduda ta kuma shiga addu'a ka'in da na'in Allah ya tashi kafaɗun sa ya dawo su cigaba da rayuwar su .
haƙiƙa tayi asarar Miji irin wanda ba zata samu madadin sa ba . To wa ma zai sake auren ta ?
Kenan ita bata ci ribar kome ba sai fa ta lalacewar suna a idanun al'umma ta zama mujiya abar zunÉ—e .
Zuciyar ta taji tana wani irin narkewa da nadama marar iyaka , tsoron halin da zata tafi ta tadda a rayuwar gidan su na huda ta da tun da ta kwashi tsawon satika bakwai a kulle babu wanda ya leƙo daga gidan su ko wani dangi nata ta san cewa kurar ta tayi kuka ta kuma riga ta dusashe tayi duhu a idanun kowa na ta .
Kwanciya tayi a ƙasa tana wani irin kuka tare da jin yadda zuciyar ta ke zogi kamar zata fashe a tsukin lokacin zaɓar mutuwa take son yi akan rayuwar da zata tarar a gaba .
Kai tsaye Youssoufa ainashin cikin ofishin ya koma inda ya nemi da a ba shi takaddun neman belin waÉ—an da ake tsare da su .
Baya cikin nutsuwar sa ya ciccike inda ya bada tabbacin yin afuwa ga Masu laifin su biyu da ake tuhuma da yunƙurin kashe shi a matsayin sa na wanda suka yiwa laifin ya sanya hannun ya janye ya musu afuwa a sake su .
Bayan gajerar muhawarar da Youssouf bai bada hankalin sa ba ya ƙirgo wasu kuɗaɗe ya ajiye a gaban teburin ya miƙe yana barin wajen bayan sun yi Sallama.
A waje ya tarar da Bilal cikin motar direban da Mijin Ubbo ya turo ya ɗauke su idan sun gama bai shiga motar ba ya ƙira Bilal ya fito .
"Ka shigga ciki za'a fito da Mammadou ku tafi gidan ubbo tare ni akwai inda zan tai .
Bai jira amsar sa ba ya taka da sauri yana barin wajen .
Wani ƙaramin Hotel ya je ya kama ɗaki na kwana guda (HOTÈL TÉNÉRÉ) tun da ya shiga ɗakin ya kashe wayoyin sa yayi sallah yayi zaune tunaninnika na masa rubdugu .
ji yake kamar ya buɗi ido ya gan shi a maraɗi wani irin hali ya kasance a ciki tsawon ƙarshen yinin zuwa cikin daren da ya tsinci tsawon sa fiye da na darare uku a wajen sa .
Asubar farko ya miƙa mukullin ɗakin ya bar otel zuwa tashar mota .
Mota ta farko da ta tashi zuwa Maraɗi da misalin ƙarfe shidda na safe cif sun kama hanya tare da Youssoufa da ya kasa jiran karfe biyun ranar jirgi ya tafi da shi .
Ya zaɓi tafiyar motar saboda ya san duk inda ƙarfe biyu na ranar tayi yana cikin Maraɗi .
Maradi .
Tun ajiya da Hajiya Umma da shi kan sa Maimartaba suka kasa samun layin Youssoufa suke cikin fargaba duk kuwa da cewa sun yi waya da Bilal har ma da Mammadou cewar suna lafiya kuma Youssoufa ma yana lafiya sai dai su ma basu san inda yake ba kuma basu samun wayar sa.
Bayan addu'a babu abunda Hajiya Umma take yi saboda jikin ta yana bata wani abu ya faru ko kuma zai faru ko mai kyau ko marar kyau .
kuma kawo yanzu ta fahimci ƙaunar da ɗan ta yake yiwa Falmata marar misaltuwa ce ba yadda ta iya dan dole ta fara addu'ar Allah ya bayyana Fatima ko dan Youssouf ya samu nutsuwa .
Ga Hajiya Mama kuwa yau ranar farin-ciki ce a wajen ta dan kuwa har 'yar ƙaramar walima ta haɗa na farin-cikin dawowar ɗan ta mafi soyuwa a wajen ta da aka yiwa sharri aka garƙame ta gayyaci ƙawayen ta na ƙud da ƙud dan su zo taya ta murna .
Matar Mammadou da ake ƙira Zainaba ita ma a nata gidan sai murna tare da shirin taryar Mijin ta .
Kamar kullum yau ma bayan an tafi Sallar Azahar Hajiya Mama ta kashe jiki ta nufi shiyar Hajiya Uwa ta buÉ—e ta shiga .
Ƙarfe biyu saura mintuna goma taxi da ta ɗauko Youssoufa daga tasha ta sauke sa baya cikin nutsuwar sa ya biya mai taxi .
Da sassarfa yake taku ya nufi cikin gidan kallo É—aya zaka masa ka matsa daga hanya ko da kuwa ba ka san ko shi wanene bane .
Ta gaban Fada ya zo ya wuce akan idanun Maimartaba da kowa na cikin fadar wanda hakan shine na farko da Youssoufa ya zo ya wuce ta gaban Mahaifin sa bai ƙarasa ya gaishe shi ba , abu ne da bai faruwa mutum ya taka ƙofar fada bai shiga ya kai gaisuwa ba .