← Book details Mafari Hargitsin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 230 OF 269

Sashe 230

Mafari Hargitsin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ɗan jim tayi jin babu wanda ya amsa mata duk kuwa da tasan ana jin ta,  sake sallamar tayi a karo na uku sannan ta tsinkayo muryar wata daga ciki ta amsa , dan haka ta sanya ƙafafun ta ciki a hankali  .

Da ɗai-ɗaya suke mayar da hankalin su kan ta tana tahowa har ta ƙarasa daga gefe kaɗan tayi ɗan gurfano tana gaishe da Hajiya Umma wacce tunda ta shigo ta rage fara'ar da take yi , kamar yadda ta saba amsa mata gaisuwar ba wata kulawa haka yanzun ma ta amsa tana janye ganin ta daga kan ta zuwa gefe kafin ta yunƙura  tana barin wajen baki ɗaya zuwa wata ƙofa daban .

A hankali ta waiga tana É—an kallon sauran matan da suke wajen biyu daga cikin su kawai ta gane "Ubbo da Ammi sauran mata ukun bata gane su ba amma dai suna mata yanayi da su Ubbo , cikin nutsuwa ta gaishe su a kunnen ta Ammi ce kaÉ—ai ta amsa da mutunci sauran matan sama-sama suka amsa ita kuwa Ubbo ko amsawar ma bata yi ba .

Fitowar Siyama daga ɗakin Umma yasa ta ɗago kan ta " sœurs wannan fa ? Kamar ya fi zama a jikina kou ?
Ta ƙarasa zancen tana ɗan yin juyi cikin dakakiyar Shadda "Boo" da ta sha aiki aka mata ɗinkin doguwar riga , nan take wajen ya ɗau ƙaramar sowa suna yaba kyaun da tayi .

cike da burgewa Falmata take kallon ta tana murmushi sosai ta yi mata kyau kwalliyar ta kuma ta ƙayatar da ita .

" kin yi kyau Maman Yumna , muryar Falmata ta ratsa wajen .

Da sauri Siyama ta waiga inda ta ji tashin muryar ta da farkon fitowar ta wajen bata lura da wanzuwar ta ba .

Tana murmushi ta ƙarasa kusan ta kafin tace " Fatima nagoude sosai, yaushe kika shigo ?
"Yanzu na zo . Ta amsa mata a taƙaice
Murmushi tayi kafin ta ɗan yi ƙasa da murya yadda Falmatan ce kaɗai zata iya ji tace " Yau Yarima Biyamuradi ke dawowa , da fatan kin masa shiri ?

Da yanayin ta na rashin magana sosai falmata ta girgiza kan ta kawai tana janye ganin ta daga kan Siyama ta sunkui da kan ta ƙasa duk jin ta take a takure sakamakon  kallon ƙasƙancin da ta lura matan wajen na jifan ta da shi .

Muryar Ubbo ta ratso wajen da take cewa " Siyama kiyi maza ki shirya mana kin tsaya inda bai dace ba , kin san fa Mijin ki na daf da shigowa , kin kuma san ke tauraruwa ce  ba tururuwa ba , ke tauraruwa mai hasken alkhairi ce ba tauraruwa mai wutsiya ba .

Cikin sanyin jiki Siyama ta juya fuskar ta ɗauke da yalwatatcen murmushin jin ɗadin yabo mai kama da ƙirari da Ubbo tayi mata sai dai gefe guda tana jin wani iri da shaguɓen da ta lura Ubbo ta yiwa kishiyoyin ta .

Har tayi taku biyu ta waigo Falmata wacce kanta ke sunkui har lokacin ba tare da ta iya haƙaƙe halin da take ciki ba , ta saita muryar ta sama kaɗan kafin tace " Fatima taho mu tai ki sauya kaya akwai Boo irin ta jikina da tai min yawa nasan zata iya miki dai-dai tunda kin fini ƙiba kuma launin zai amshe ki'...

" ahir É—in ki da arawa kishiya sutura solobiya hala ita batta da sutura ta ratayo wagga tsumma a jikin ta ta taho muna nan tana barin mouna tsamin gwanjo ?

. " ko da shike ba laifin ta ba nan gurin ta ƙurewa kenan , talaka daman yaushe yunwar ciki nashi ya lafa bare ya san suturar da ta amsa sunan sutura ? Bar ta cikin tsummokaran ta da shi yafi dacewa da itta ..

"s'il te plait Adda amm Dan Allah .

Da yanayi na rashin jin daɗi tare da chakuɗuwar tausayi Siyama ta juya ga Falmata lokacin da take mikewa tsaye ,  tayi saurin riƙo hannun ta tana cewa " kiyi haƙuri ƙamnata mu tai na miki le maquillage ki sauya kayan kin ji kou ?

Idanun ta cike da ƙwalla wannan karon cikin wani irin yanayi ta zame hannun ta daga riƙon da siyama ta mata , tana ƙoƙorin danne hawayen da suke neman ɓallowa tace " Nagode Maman Yumna sannan ba sai na sauya kayana ba na jikina ma masu tsarki ne kuma kyauta ce daga Mijina masoyina ,dan shi na saka dan ya gani yaji daɗi ba domin na zama tauraruwa ba ina so ya ganni da su rataye a jikina dan yasan cewa na yaba da kyautar sa .

Dan murmushi tayi kaɗan tana mayar da gani. ta kan su Ubbo daga inda take tana hango ɓacin rai akan fuskokin su da take iya gani dusu-dusu .

" Nagode sosai Maman Yumna , ta sake faÉ—in haka lokacin da take barin wajen .

Dusu-dusu take ganin hanya saboda idanunta da suke cike taf da ƙwalla ga kuma zogin da suke mata.

bata tarar da Hajja inda ta bar ta ba , tana zaton tana ɗakin su a yadda zuciyar ta take yanzu so take ta samu waje ta ɓuya tayi kuka , ciwo ke sasuƙar rarraunar zuciyar ta da daman tana kusa jiran kiris take .

Dan haka a karon farko tun zuwan su gidan ta fito ta ɗau hanya ba tare da tasan takamai-mai ina ta nufa ba bata kuma damu da bayun da suke binta da kallo har  wasun su na yin ƙus-ƙus ba so take tayi nesa da mutane ta samu maɓoyar yin kukan ta masha'in '

Can wani sashin da ta lura da ɗaukewar ƙafa ta shiyar nan ta nufa ,lokacin da ta doshi mashigar sashin tun kafin ta ƙaraso masu gadi biyu suka dakatar da ita , tambayar ta suka yi wacece ita ? Ta basu amsa da ita ce Fatima , suka ce daga ina take ? Tace daga Maiduguri Nigeria .

Juyawa suka yi gefe suna ƙus-ƙus

Cike da gundura ta juya da nufin fasa shiga ta nemi wani wajen saboda gaba ɗaya cikin gidan ne bata son komawa sai ta tsinkayo ɗaya daga cikin bayun yace " Ranki shi daɗe uwargijiyar mu afouwa muke biɗa ki maouna sassauci rashin sani ya sanya mu turjiya ga oumarnin ki baa in miki jagora ƙofa a buɗe take ga Iyalan Yarima Biyamuradi..

Sai suka buɗe mata ƙofar gidan daga inda take tana iya hango ƙawatuwar harabar gidan da shukoki masu furanni da bata ga irin su ba a kan hanyar ta ta zuwa nan , dan haka sai ta sanya ƙafar ta a hankali cikin harabar gidan ƙamshin furanni tare da na sabon fenti da wankin da aka yiwa gidan ya sanya ta lumshe ido ta fara taku tana jin yadda sanyin wajen yake ratsa ta shirun wajen yana samar mata da wata nutsuwa ta musamman sai kawai ta miƙa hanya ba tare da tasan inda zata je ba .

Bakin wasu manyan gine-gine uku ta bullo tana ƙare musu kallo gini ne mai matuƙar kyau da tsari , ta tafi a hankali kan barandar ginin da yake fuskantar ta a tsakiya ta zauna daga bakin barandar ba tare da ta damu da shirun da ya yawaita a wajen ba bare ta ji tsoro sai kunnuwan ta da suke tarwai tana jin sauƙar kukan tsintsaye .

Tana zama ta ji ƙuntatciyar zuciyar ta ta fara warwarewa lokacin da kuka mai ƙarfi ya zo mata , ta dunga tuno yadda baki ɗayan 'yan uwan Youssouf basu son ta ciki har da Mahaifiyar sa kan ta . Sannan shi ɗin ma da ake kome domin sa bai damu da ita ba a halin yanzu ma bata san matsayin ta ba a wajen sa .

A hankali ta kai rigar jikinta hancin ta ta shinshina lokacin da take tuno da kalaman Ubbo da tace duk ta cika musu waje da warin gwanjo , ita bata ji warin da rigar take yi ba sai ma ƙamshi irin na tsadaddun kayan da aka sayo su daga manyan shagunan da suka amsa sunan su da ya chakuɗu da ƙamshin humrar ta yake bada wani irin launin ƙamshi mai sanya shauƙi'

Ajiyar zuciya ta sauƙe cikin ran ta tana tambayar kan ta ko sai yaushe ne su zasu huta daga gorin mutanen duniya ? Sai yaushe ne za'a fara musu kallon mutuntawa ?

Hawayen ta ta shafe da hannun ta tana jin damuwar ta tana raguwa da tayi kukan , daga gefe ta hango bakin fanfo ta yunƙura a hankali ta nufi wajen wanke fuskar ta tayi kuma ta tari ruwan da tafukan ta ta sha , ta kulle fanfon ta dawo ta zauna inda ta tashi .

Wasu kyawawan duwatsu farare kal-kal ta gani daga gefe a É—an gurin da aka killace domin yin shuke-shuke ta sa hannu a hankali ta tsinto su , ta zube su a gaban ta tana kallo cikin ran ta tana tunanin me ake yi da su kuma ?

Jingina kanta tayi da jikin barandar tana rintse idanun ta saboda iskar wajen da take jin ta mata yawa kamar tana ƙara mata ciwon idon .

Da ta rufe idon sai taji daɗi sannu kan hankali taji zaman ya fara mata ba daɗi saboda bayan ta da ya fara ƙagewa , bata damu da ta buɗe idanun ta ba da daman tafi sabawa da duhun dake cikin su.

sai ta kishingiɗa kaɗan da nufin bawa kanta hutu na wani lokaci ,  sassanyar iskar wajen haɗi da shirun da wajen yake da shi da kuma yanayin jikin masu ciki yasa bata jima ba baccin da bata san yaushe ne ya kawo mata ziyara ba ya ɗauke ta a wajen .

Lokacin da Biyamuradi Youssouf ya iso baki É—ayan Masarautar sai ta É—auki murna da kiÉ—e-kiÉ—e tamkar wanda ake gagarumin biki .

Da kyar ya samu ya zille daga fada nan ma domin uzurin da Tafeeda ya shigar ne na cewar da yayi ya kamata ya samu hutu tunda bai cika lafiya ba har yanzu .
Chapter 230 · 0% Book details