Sashe 217
Mafari Hargitsin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ɗan wani guntun murmushi yayi lokacin da wani tunani ya gifta masa nan take , rigar da yayi niyyar sawa ya ajiye a gefen gadon , a nutse ya nufi ƙofar banɗakin , ba tare da ya taɓa ƙofar ba yace ,
" ki fito ki tafi kar a gaji da jiran ki .
Daga ciki ta ce " to ka gama shiryawa ko ? Dan Allah kayi haƙuri ɗazun ban san kana shiryawa bane ,
Ɗan mitsitsin murmushi ya kuma yi yana cije leɓensa na ƙasa a taƙaice yace " eh na shirya ki fito .
Kan ta a ƙasa ta fito , a ɗan sace ta ƙyallo sa ,ta gan shi yadda yake a ɗazu da sauri sake juyawa sai dai kafin tayi wani yunƙuri ya naɗo ta ta cikin jiƙaƙƙen Hijabin ta ya haɗa ta da jikin sa ,
A ruɗe Yakaka ta fara ƙoƙarin ƙwacewa , bakin ta ya gaza furta ko kalma guda , matsera kawai take nema ,
" Meye kike haka , kamar wacce bata saba ganin Maza a tuɓe ba ? Kar ki min kinibibin ku na mata .
Doctor Hamza yace haka laɓɓansa ɗauke da murmushin da yafi kama da na mugunta , cikin zuciyar sa yana sake haƙaƙewa da abunda yayi niyya , ya juyo da ita da ƙarfi ya ɗago fuskar ta da idanun ta ke runtse , hasken da ya haske fuskar shi ya bashi damar ganin hawayen da suka jiƙa mata fuskar ta ,
Shagala yayi da kallon kowanne ɗigo na tudu da ƙwarmin da yake fuskar ta , kallo yake mata irin wanda bai taɓa yi mata irin sa ba , a idanun sa kome na fuskar ta tsararre ne da ya dace ƙwarai da muhallin da Ubangiji ya ajiye mata shi .
Zuciyar sa take buÉ—uwa tare da tashin tsikar jikin sa, bai san lokacin da ya haÉ—e tazarar da bata wuce tudun yatsa guda da yake tsakanin fuskokin su ba , ya haÉ—e fuskokin su waje guda , tare da ratsa hannuwan sa ya kewaye ta da su sosai ,
Da wani irin yanayin da ya zarce yadda yake da nufin yi , ya shiga yin abubuwan da zuciyar sa ta raÉ—a masa da ya yi a matsayin gwada Yakaka ya ga ko kalaman Suleiman gaske ne Yakakar kamilallar mace ce , tsautsayi tare da kaddarar rayuwa ce suka faÉ—a mata ?
Sai ga shi ya gaza tantance Yakaka yake son gwadawa ko kuwa martabar sa ta ɗa Namiji yake aunawa ? Domin kuwa a tsakanin lokacin jin sa yake kamar wannan ne lokaci na farko da gangar jikin sa ya fara raɓar na wata ɗiya Mace .
Yakaka da ake yiwa gwaji ita ta yunƙura ba tare da tayi amfani da ƙarfin kirki ba , ta zare jikin ta daga na shi , bata tsaya ba kamar yadda bata yadda ta bari idanun su sun haɗu ba ta taka da gudun gaske ta fice daga ɗakin da sashin nasa ma baki ɗaya ,
Bata tsaya daga gudun da take yi ba sai da ta tabbatar ta bada tazara mai É—an yawa daga sashin sa .
Zama tayi akan wani É—an tudu tana mayar da numfashi harabar wajen babu mutane alama dake nuna an riga an tafi Dinner an bar ta .
Kalaman Doctor Hamza ta tuno ," me yake nufin da cewa ta saba ganin maza a tuɓe ? Kenan nufin sa ita wata ƙasurgumar karuwa ce da ta saba cuɗanya da Maza , shi yasa ya mata abunda ya yi mata yanzu .
Hawayen ɓakin ciki ya zubo mata , tayaya zata yi rayuwa da mijin da yake zargin ta irin wannan mummunan zargin ?
Da jaan ƙafa ta nufi cikin gida , kai tsaye ta zarce ɗakin su inda ta tarar da Falmata ita ɗaya ƙwal tana kwance lamo akan gado
Bata ce mata ƙala ba kamar yadda ita ma Falmatan bata nuna alamun ta san da shigowar ta ba , ta cire jiƙaƙƙun kayan jikin ta sauya da wasu , a hankali ta zo bakin gadon ta zauna , ta ɗan dubi Falmata da jikinta yake bata ba bacci take ba ƙoƙarin haɗiye damuwar ta take lokacin da tace , " Falmata baki tafi wajen Dinner bane ?
Ba tare da ta motsa ba muryar ta can ciki tace " Ban tafi ba Yakaka Amnee tace na zauna nima tunda ke ma Yaya Dakta ya hana ki tafiya , kuma ma bana jin daÉ—in jikina bayana ciwo yake min .
Shiru su dukkanin su biyun suka sake yi , zuciyar kowaccen su na sake ƙuntata da damuwar dake cin ta a rai , can ta tsinkayi muryar Falmata tace , "Yakaka yau kwanan mu ishirin da ɗaya da dawowa daga Niger ko ?
Ɗan waigowa Yakakar tayi ta dube ta , ba tare da ta bata amsa ba tausayin ta ta ji ya kama ta , babu shakka tasan damuwar Falmata ba zata wuce akan Youssouf ba da shima yake gwada nashi walaƙanci a zaton ta ta hanyar yin shaƙulatin ɓangaro da ƙanwar ta .
Washegari duk baƙi na nesa suka fara watsewa ciki har da Malama maryam da duk wasu dangi na nesa suka yi tafiyar su bayan Amnee ta cika su da kayan biki fal .
Zuwa yammaci gidan ya rage sai su isu 'ya'ya da dangin Amnee , lokacin ne kuma Baa ya aika aka ƙira masa Doctor Hamza , bayan sun gaisa nasiha ya shiga yi masa mai ratsa jiki tare da tarin tunasarwa akan nawin da ya ƙaru akan sa , da kuma wuyar da yin Adalci yake da shi wanda kuma dole ne ya tsayar da shi a tsakanin matansa muddin yana son dacewa da samun Rahamar Ubangiji .
Bayan ya gama masa nasiha da hannu ya masa nuni da saitin akwatuna biyu da adadin su yake kai ɗaya kawai launi da sumfurin su ne ya shabanba , kowanne guda takwas , ya ɗora da cewa " Wannan lefen Matan ka ne ɗayar ka kaiwa Safiya da hannun ka , ɗayan kuma na Amina ne , kamar yadda muka yi da kai nan da ƙasa da watanni biyu nake so ka samarwa da matar ka wajen zama a kusa da kai , idan ma kuma wajen zaman ya samu a yau
ko gobe ne ka dawo ka É—auke ta ku tafi abun ku Allah ya bada zaman lafiya .
Godiya Doctor Hamza ya dunga yi ƙaunar Mahaifinsa na daɗa ratsa shi tare da ƙarin ganin ƙima da darajar sa , har ya miƙe zai tafi Baa ya sake dakatar da shi wata ɓakar leda da take nannɗe ya miƙa masa "wannan kuma wasu kuɗaɗe ne da aka bani na baka a matsayin gudumawa , ka ƙara wajen kula da gida ,
Da sauri Doctor Hamza ya noƙe hannun sa ," Baa ka bar su ayi amfani da su anan , ni ina da kuɗin da zasu isa nayi kome da su Nagode Baa nagode .
Da murmushi a fuskar sa yace" karɓi mana ai ni na baka .
Ƙarfe biyun rana Doctor Hamza yayi Sallama da iyayen sa zai koma Abuja a yau ɗin saboda gobe yana da tarin aiyuka a office da bashi da damar ɗaukar musu uzirin jinkirta yin su .
Dangin Amnee ma ya musu Sallama bayan ya bada kuÉ—aÉ—e masu yawa da yace ayi musu sayayyar duk abunda suke so kafin tafiyar su , sannan ya tsawaita godiyar sa a gare shi .
Da Khaalty Rahima ma sallamar su ta musamman ce da suka keɓe suna yi ta inda ita ma ta ɗora masa 'yar nasihar ta a ƙarshe ta ba shi shawara kan ya lallashi Safiya sosai kar ya bari ƙarin auren da yayi ya ɓata zamantakewar su .
Ƙannen sa mata ma duk Sallamar yayi da su har da Rahima amarya da ba'a riga an miƙa ta gidan mijin ta ba saboda iyayen sa ba 'yan nan bane 'yan ƙasar katsina ne , kuma a halin yanzu duk suma shirye-shiryen komawar su suke can ƙasar America inda suke rayuwar su a can , nan da ƙasa da sati biyu zasu tafi tare duk har da Rahima .
Lokacin da ya gama Sallama da kowa da ya dace , ciki har da Falmata, sai ya shiga ɗan jefa ido waje-waje ya gagara tashi ya tafi , sai daɗa jaan hirar su yake shi da ƙannen sa .
Hajja wacce ita ma tun a waje da ita ya fara cin karo tana tattara harabar gidan suka gaisa har ma ya mata sallamar tafiyar sa ta jero masa addu'o'in da yake jin daÉ—in irin su ,
Ita ce ta shiga tana ganin sa tace ," Babban likita har yanzu baka tafi ba ? Kai kuwa na ga baka saba tafiyar dare ba garin Abuja ai ba kusa ba , dan ma dai ku manya ne .
" yanzu zan tafi Hajja , yace yana ƙoƙarin miƙewa , Hajja ta shige ɗakin ta tana cewa " Allah ya tsare hanya Babban likita .
Tana shiga É—akin tayi turus ganin Yakaka kwance akan katifar ta tana buga game da wayar Rahima ,
Salatin da Hajja ta É—auka sai da ta dire shi da tafa hannuwa sannan ta É—ora da cewa " ni hauwa'u me zan ji me zan gani ? 'yar nan kan ki É—aya ?
Yakaka ta É—ago kai tana kallon Hajja ,
" me nayi Hajja ko dan na hau 'yar katifar ki ? to bari na tashi , ta ce tana miƙewa ta sauƙa daga katifar ,fatan ta shine Hajja tayi shiru kar a jiyo muryar ta a san tana nan .
Hajja ta ɗora da cewa " tambayar ki nake kan ki ɗaya ? Yanzu ace Mijinki na can shirin ɗaukar doguwar hanya ke kina nan kina latse-latsen wofi ? Bawan Allah shi yasa mana ya gagara tafiya ashe ke ce baki masa abunda ya dace ba wanda zai ƙara masa kuzari da nishaɗin tafiya , tashi nace sakaryar mata , tashi ki fice min a ɗaki , ki fita ga mijinki can yana jiran ki kuyi sallama .
" ki fito ki tafi kar a gaji da jiran ki .
Daga ciki ta ce " to ka gama shiryawa ko ? Dan Allah kayi haƙuri ɗazun ban san kana shiryawa bane ,
Ɗan mitsitsin murmushi ya kuma yi yana cije leɓensa na ƙasa a taƙaice yace " eh na shirya ki fito .
Kan ta a ƙasa ta fito , a ɗan sace ta ƙyallo sa ,ta gan shi yadda yake a ɗazu da sauri sake juyawa sai dai kafin tayi wani yunƙuri ya naɗo ta ta cikin jiƙaƙƙen Hijabin ta ya haɗa ta da jikin sa ,
A ruɗe Yakaka ta fara ƙoƙarin ƙwacewa , bakin ta ya gaza furta ko kalma guda , matsera kawai take nema ,
" Meye kike haka , kamar wacce bata saba ganin Maza a tuɓe ba ? Kar ki min kinibibin ku na mata .
Doctor Hamza yace haka laɓɓansa ɗauke da murmushin da yafi kama da na mugunta , cikin zuciyar sa yana sake haƙaƙewa da abunda yayi niyya , ya juyo da ita da ƙarfi ya ɗago fuskar ta da idanun ta ke runtse , hasken da ya haske fuskar shi ya bashi damar ganin hawayen da suka jiƙa mata fuskar ta ,
Shagala yayi da kallon kowanne ɗigo na tudu da ƙwarmin da yake fuskar ta , kallo yake mata irin wanda bai taɓa yi mata irin sa ba , a idanun sa kome na fuskar ta tsararre ne da ya dace ƙwarai da muhallin da Ubangiji ya ajiye mata shi .
Zuciyar sa take buÉ—uwa tare da tashin tsikar jikin sa, bai san lokacin da ya haÉ—e tazarar da bata wuce tudun yatsa guda da yake tsakanin fuskokin su ba , ya haÉ—e fuskokin su waje guda , tare da ratsa hannuwan sa ya kewaye ta da su sosai ,
Da wani irin yanayin da ya zarce yadda yake da nufin yi , ya shiga yin abubuwan da zuciyar sa ta raÉ—a masa da ya yi a matsayin gwada Yakaka ya ga ko kalaman Suleiman gaske ne Yakakar kamilallar mace ce , tsautsayi tare da kaddarar rayuwa ce suka faÉ—a mata ?
Sai ga shi ya gaza tantance Yakaka yake son gwadawa ko kuwa martabar sa ta ɗa Namiji yake aunawa ? Domin kuwa a tsakanin lokacin jin sa yake kamar wannan ne lokaci na farko da gangar jikin sa ya fara raɓar na wata ɗiya Mace .
Yakaka da ake yiwa gwaji ita ta yunƙura ba tare da tayi amfani da ƙarfin kirki ba , ta zare jikin ta daga na shi , bata tsaya ba kamar yadda bata yadda ta bari idanun su sun haɗu ba ta taka da gudun gaske ta fice daga ɗakin da sashin nasa ma baki ɗaya ,
Bata tsaya daga gudun da take yi ba sai da ta tabbatar ta bada tazara mai É—an yawa daga sashin sa .
Zama tayi akan wani É—an tudu tana mayar da numfashi harabar wajen babu mutane alama dake nuna an riga an tafi Dinner an bar ta .
Kalaman Doctor Hamza ta tuno ," me yake nufin da cewa ta saba ganin maza a tuɓe ? Kenan nufin sa ita wata ƙasurgumar karuwa ce da ta saba cuɗanya da Maza , shi yasa ya mata abunda ya yi mata yanzu .
Hawayen ɓakin ciki ya zubo mata , tayaya zata yi rayuwa da mijin da yake zargin ta irin wannan mummunan zargin ?
Da jaan ƙafa ta nufi cikin gida , kai tsaye ta zarce ɗakin su inda ta tarar da Falmata ita ɗaya ƙwal tana kwance lamo akan gado
Bata ce mata ƙala ba kamar yadda ita ma Falmatan bata nuna alamun ta san da shigowar ta ba , ta cire jiƙaƙƙun kayan jikin ta sauya da wasu , a hankali ta zo bakin gadon ta zauna , ta ɗan dubi Falmata da jikinta yake bata ba bacci take ba ƙoƙarin haɗiye damuwar ta take lokacin da tace , " Falmata baki tafi wajen Dinner bane ?
Ba tare da ta motsa ba muryar ta can ciki tace " Ban tafi ba Yakaka Amnee tace na zauna nima tunda ke ma Yaya Dakta ya hana ki tafiya , kuma ma bana jin daÉ—in jikina bayana ciwo yake min .
Shiru su dukkanin su biyun suka sake yi , zuciyar kowaccen su na sake ƙuntata da damuwar dake cin ta a rai , can ta tsinkayi muryar Falmata tace , "Yakaka yau kwanan mu ishirin da ɗaya da dawowa daga Niger ko ?
Ɗan waigowa Yakakar tayi ta dube ta , ba tare da ta bata amsa ba tausayin ta ta ji ya kama ta , babu shakka tasan damuwar Falmata ba zata wuce akan Youssouf ba da shima yake gwada nashi walaƙanci a zaton ta ta hanyar yin shaƙulatin ɓangaro da ƙanwar ta .
Washegari duk baƙi na nesa suka fara watsewa ciki har da Malama maryam da duk wasu dangi na nesa suka yi tafiyar su bayan Amnee ta cika su da kayan biki fal .
Zuwa yammaci gidan ya rage sai su isu 'ya'ya da dangin Amnee , lokacin ne kuma Baa ya aika aka ƙira masa Doctor Hamza , bayan sun gaisa nasiha ya shiga yi masa mai ratsa jiki tare da tarin tunasarwa akan nawin da ya ƙaru akan sa , da kuma wuyar da yin Adalci yake da shi wanda kuma dole ne ya tsayar da shi a tsakanin matansa muddin yana son dacewa da samun Rahamar Ubangiji .
Bayan ya gama masa nasiha da hannu ya masa nuni da saitin akwatuna biyu da adadin su yake kai ɗaya kawai launi da sumfurin su ne ya shabanba , kowanne guda takwas , ya ɗora da cewa " Wannan lefen Matan ka ne ɗayar ka kaiwa Safiya da hannun ka , ɗayan kuma na Amina ne , kamar yadda muka yi da kai nan da ƙasa da watanni biyu nake so ka samarwa da matar ka wajen zama a kusa da kai , idan ma kuma wajen zaman ya samu a yau
ko gobe ne ka dawo ka É—auke ta ku tafi abun ku Allah ya bada zaman lafiya .
Godiya Doctor Hamza ya dunga yi ƙaunar Mahaifinsa na daɗa ratsa shi tare da ƙarin ganin ƙima da darajar sa , har ya miƙe zai tafi Baa ya sake dakatar da shi wata ɓakar leda da take nannɗe ya miƙa masa "wannan kuma wasu kuɗaɗe ne da aka bani na baka a matsayin gudumawa , ka ƙara wajen kula da gida ,
Da sauri Doctor Hamza ya noƙe hannun sa ," Baa ka bar su ayi amfani da su anan , ni ina da kuɗin da zasu isa nayi kome da su Nagode Baa nagode .
Da murmushi a fuskar sa yace" karɓi mana ai ni na baka .
Ƙarfe biyun rana Doctor Hamza yayi Sallama da iyayen sa zai koma Abuja a yau ɗin saboda gobe yana da tarin aiyuka a office da bashi da damar ɗaukar musu uzirin jinkirta yin su .
Dangin Amnee ma ya musu Sallama bayan ya bada kuÉ—aÉ—e masu yawa da yace ayi musu sayayyar duk abunda suke so kafin tafiyar su , sannan ya tsawaita godiyar sa a gare shi .
Da Khaalty Rahima ma sallamar su ta musamman ce da suka keɓe suna yi ta inda ita ma ta ɗora masa 'yar nasihar ta a ƙarshe ta ba shi shawara kan ya lallashi Safiya sosai kar ya bari ƙarin auren da yayi ya ɓata zamantakewar su .
Ƙannen sa mata ma duk Sallamar yayi da su har da Rahima amarya da ba'a riga an miƙa ta gidan mijin ta ba saboda iyayen sa ba 'yan nan bane 'yan ƙasar katsina ne , kuma a halin yanzu duk suma shirye-shiryen komawar su suke can ƙasar America inda suke rayuwar su a can , nan da ƙasa da sati biyu zasu tafi tare duk har da Rahima .
Lokacin da ya gama Sallama da kowa da ya dace , ciki har da Falmata, sai ya shiga ɗan jefa ido waje-waje ya gagara tashi ya tafi , sai daɗa jaan hirar su yake shi da ƙannen sa .
Hajja wacce ita ma tun a waje da ita ya fara cin karo tana tattara harabar gidan suka gaisa har ma ya mata sallamar tafiyar sa ta jero masa addu'o'in da yake jin daÉ—in irin su ,
Ita ce ta shiga tana ganin sa tace ," Babban likita har yanzu baka tafi ba ? Kai kuwa na ga baka saba tafiyar dare ba garin Abuja ai ba kusa ba , dan ma dai ku manya ne .
" yanzu zan tafi Hajja , yace yana ƙoƙarin miƙewa , Hajja ta shige ɗakin ta tana cewa " Allah ya tsare hanya Babban likita .
Tana shiga É—akin tayi turus ganin Yakaka kwance akan katifar ta tana buga game da wayar Rahima ,
Salatin da Hajja ta É—auka sai da ta dire shi da tafa hannuwa sannan ta É—ora da cewa " ni hauwa'u me zan ji me zan gani ? 'yar nan kan ki É—aya ?
Yakaka ta É—ago kai tana kallon Hajja ,
" me nayi Hajja ko dan na hau 'yar katifar ki ? to bari na tashi , ta ce tana miƙewa ta sauƙa daga katifar ,fatan ta shine Hajja tayi shiru kar a jiyo muryar ta a san tana nan .
Hajja ta ɗora da cewa " tambayar ki nake kan ki ɗaya ? Yanzu ace Mijinki na can shirin ɗaukar doguwar hanya ke kina nan kina latse-latsen wofi ? Bawan Allah shi yasa mana ya gagara tafiya ashe ke ce baki masa abunda ya dace ba wanda zai ƙara masa kuzari da nishaɗin tafiya , tashi nace sakaryar mata , tashi ki fice min a ɗaki , ki fita ga mijinki can yana jiran ki kuyi sallama .