Sashe 142
Mafari Hargitsin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ya sauƙe ta yana riƙe da hannun ta suka ƙarasa cikin falon , ya samu mazauni kan ɗaya daga cikin kujerun wajen yana gaisawa da hajja wacce ta miƙe zaune daga kishingiɗar da tayi ,
Kamar yadda ta saba , yanayin ta babu walwala idan har yana waje ta gaida shi , tana riƙo hannun mama wacce take ƙoƙarin ajiye mata hular baban ta a kai ,
Bata iya hana ta ba sai da ta É—aura mata hular akan hular da take rufe akan ta wacce take mahaÉ—in doguwar rigar jikin ta ruwan madara me É—an nawi saboda tashi da aka yi da É—an sanyi garin sakamakon ruwan sama da aka kwana yi daren jiya .
Shafa fuskar ta mama tayi , kamar yadda yake al'adar su ita da mamar ta .
Maama kin yi chau dayawa ,
Papa ka ga maama na tayi chau , donne-nous des photos ,
ta ƙarasa zancen tana hayewa kan kujerar da falmata take ta zagaya ta bayan ta gami da sarƙafa hannuwan ta biyu ta wuyan falmatan ta cusa fuskar ta gefen wuyan ta .,
Biyamuradi wanda ya fara yiwa hajja bayani game da shirye-shiryen da yake na tafiyar su US , ya juyo da duban sa kan su idanun sa suka sauƙa kan fuskar falmata wacce haƙoranta ke buɗe tana murmushin da yake bayyana farin cikin ta da ganin walwalar mama ya assasa mata ,
Kamar maganaɗisu ya riƙe shi , ya kasa janye idanun sa daga kan ƴar fuskar ta da komen ta yake ɗan madaidaici idan aka cire manyan idanun ta ,
Ba tare da ya iya É—auke ido daga kallon ta ba ya zaro wayar sa daga aljihu , ya juyo baki É—ayan sa ya saita cemara ya haska musu hotuna wajen kala shidda ,
Da gudu mama ta sake sauƙowa ta dawo wajen baban ta , tana cewa zata ga hoto ?
Ta É—are cinyar sa ,
Batare da ya sake mata wayar ba ya nuna mata hotunan , da sauri ta sanya hannu tana sake tura huton gaba , fuskar wata Æ´ar baby me kyau kamar ta ya cika fuskar wayar , Æ´ar yarinya ce da bata wuce shekaru biyu ba tana tsaye a hoton ,
A hankali mama ta É—ago kan ta tana duban fuskar sa
Papa bebe waye ?
Zare wayar yayi daga hannun ta ba tare da ya bata amsa ba, daidai lokacin da hajja ta ke cewa ,
Wannan yarinyar da surutu kike kamar aku , duk kin bi kin tsare shi da surutu kin hana shi ya yi magana , bayan kuma yayi shirin tafiya aiki , ni zo nan ki zauna na miki tafiyar tsutsa a ƙafar ki .
Sauƙa tayi daga jikin sa , maimakon ta tafi wajen hajja , sai ta nufi mamar ta , tana zuwa ta zauna a gefen ta gami da kwantar da kai a jikin ta tayi shiru ,
Boyayyar ajiyar zuciya Biyamuradi yayi , cikin ran sa yana hamdala da hajja ta katse masa tambayoyin mama , domin Alƙawari ya ɗaukarwa kan sa ba zai taɓa yiwa ƴaƴan sa ƙarya ba , akan duk wata tambaya da suka masa , sai dai ko ya sakaya amsar idan kaifin hankalin su bai kai su fahimce ta ba , amma a yanzu bai shirya amsa ba ga tambayar da mama tayi ma sa .
Cigaba da yiwa hajja bayani yayi , inda yake sanar da ita , yana son ranar litinin ya zo su je ayiwa falmata da mama passport , zai fara nema musu visa
Idan Allah ya yadda daga sun samu visa shi da su zasu tafi US , da ba zai wuce tsawon nan da wata É—aya da Æ´an kwanaki ba nan gaba ,
Ba shi da masaniya akan tsawon lokacin da zasu iya yi a chan ,saboda harka ce ta neman lafiya , bai san yadda lamura zasu kasance ba , amma dai visa ta tsawon watanni shidda zai samar musu .
Ya ɗora da neman hajja ta masa bayanin duk wasu abubuwan da zata iya buƙata bayan kayan abinci da sauran abubuwan buƙata na rayuwar yau da kullum wanda zai iya kai ta watanni shidda ko fiye da haka ,
Da farko addu'o'in samun nasara akan abunda zasu nema tare da addu'ar nemawa mama samun waraka tayi ta jerowa , tana jin yadda tausayin su duk ukun ke kama ta ,
Babban soja , ni ba sai an min tanadin kome ba , saboda ka ga nima wajen shekaru biyu ake nema rabona da Æ´an uwa da dangi , dan haka idan har tafiyar ta tashi , bayan kun tafi a washegari nima zan É—au hanya zuwa nigeria nima naje na sada zuminci na ga Æ´an uwa da dangi , shekaru sun fara jaa , mutuwar nan ta yanzu kar ta gifta tsakani ba'a nemi gafarar Æ´an uwa ba , idan ya so bayan dawowar ku ko kuwa ma kafin ku dawo sai a sanar min nayi dawowa ta , ai ka ga nima na ribaci lokaci ko kuwa ?
Babu shakka hakane hajja , to babu kome idan har tafiya ta kama lokaci yayi sai ki tafi zouwa gida kafin dawowar mu , Allah ya saka da Alheri , ki min duk wasu bayanai na abubuwan da kike buƙata da zaki yiwa mutanen gida tsaraba don Allah .!
Toh madallah Babban soja , amma dayake nima a wajen nawa akwai Æ´an kuÉ—aÉ—e irin waÉ—anda kake min kyautar su ai ba ma sai na maka lissafin kayan tsaraba ba , idan tafiya ta zo ni da kaina zani nayo Æ´ar tsaraba ta ,
A ah hajja , don Allah kar ki ce hakka , irin Alherin da kika mouna a rayuwa ba zamou iya biyan ki ba sai dai Allah shi saka da Alheri , ƙwarai ƙwarai ina miki godiya , ki min lissafi abun da kike buƙata duk zan sa a kawo kome ranar da zaki tafi sai direban da ya kai ki wancen karon ya sake kai ki nagode !
Ni ce da godiya Babban soja ni ce da godiya , Allah dai ya ƙara buɗi , ya ba wa mama lafiya ,
Ameen ameen hajja ya amsa yana miƙewa ,
Sashin da suke ya mayar da duban sa , mama har tayi bacci fuskar nan a chakuÉ—e alamun fushi take ,
Bai yi mamaki ba saboda sanin ta da yayi da saurin bacci ,
A hankali ya taka zuwa gaban falmata wacce tayi shiru , tana É—an shafar kan mama da yake bisa cinyar ta ,
Fatima ni zan tafi bakin aiki zouwa le lundi zan dawo mu tai à muku passeport , ki kula da mama kar tayi wassa dayawa idan ta ji sauƙi sosai sai ta cigaba da zouwa école .
Toh Allah ya kiyaye hanya ,!
Ta amsa masa ,
Ɗan jim yayi a tsaye yana ƙure mata kallo da buɗaɗɗun idanun sa , hular ta shi ta karɓi yar zagayayyar fuskar ta me ɗan haske kaɗan , ji yake kamar ya bar mata hular a kan ta yayi ta kallon ta a haka ,
Jin yayi shiru kuma ta san da tsayuwar sa a wajen ya sa ta É—an dago kan ta , tana sake haÉ—e fuska ,
Gyaran murya yayi ganin yadda tayi kicin-kicin kamar zata fashe masa da kuka .
Fatima donne moi mon chapeau! ( miƙe min hula ta )
Ya furta hakan yana sake rage amon muryar sa ,
Falmata wacce tsayuwar sa akan ta da idanun sa da take ji suna mata yawo a jiki tamkar suna mintsinin ta ya sa ta diririce ta gaza fahimtar me yake cewa , ba wai dan bata jin yaren da yake yi ba ,
Mama bacci take .
ta ce da shi tana fatan ya bar kan ta
A hankali ya sunkuyo har tana iya jiyo hucin humfashin sa a fuskar ta ya kai hannun sa guda ya zare hular sa dake kan ta , ya mayar kan sa .
Na tafi
Yace da ita yana juyawa ya bar wajen .
Wani irin yanayi ta ji a jikin ta uwa wacce aka zubawa ruwan sanyi , har ga Allah ta mance da hular sa da take kafe a kan ta ,
Runtse idanun ta tayi da ƙarfi tana jin yadda zuciyar ta ke bugu .
Hajja wacce duk abunda ya faru akan idanun ta tana iya hango su daga inda take .
auho ! aikin banza ihu bayan hari , da kike wani runtse ido kina wani kawar da kai ya ƙadangariyar gobara , ai wallahi ni dai na daina saki a hanya kan sha'anin auren ki , tsakani na da ke ido ,!
Ace wai tsawon shekaru fiye da biyar kin kasa zama cikakkiyar matar gida , ke kenan ɗaurewa miji fuska kina muzurai , zauna nan yarinya za'a yi bake lokacin da Babban soja ya gaji da halin ki ya sillo auren sa babu ni a masu yi miki dannar ƙirji , ko muƙamuƙi ba zan danna miki ba .
Cikin rashin kulawa da zantukan hajja wanda falmata ta riga ta saba da jin makamantan su , tace
Hajja ta me kika ce ?
Abunda wancan yace , shi nace
Ta amsa mata tana shirin miƙewa daga inda take tana cigaba da mita ,
Ƙatuwar mace kamar ki ace wai har yau tana da miji amma bata san amfanin sa ba sai rainon ƴa ,?
Ai ni ina kamar ki nayi aure na na biyu ma ,
Ki ka ce me hajja ta ban ji da kyau ba ??
Na ce gidan ku !
Ta amsa mata tana ƙarasa barin wajen
Murmushi falmata tayi domin ta san ta ƙular da hajja ,
Cikin ran ta tana juya maganganun hajja ,
Ban da abun hajja shi mutumin da kullum.take kumfar baki akan a kula da shi ɗin , shi ya taɓa nuna wata alama ne na kasancewar ta matar sa ? Tsawon shekarun auren su a tun bata san me takamaimai kalmar auratayya ke nufi ba ,
Kamar yadda ta saba , yanayin ta babu walwala idan har yana waje ta gaida shi , tana riƙo hannun mama wacce take ƙoƙarin ajiye mata hular baban ta a kai ,
Bata iya hana ta ba sai da ta É—aura mata hular akan hular da take rufe akan ta wacce take mahaÉ—in doguwar rigar jikin ta ruwan madara me É—an nawi saboda tashi da aka yi da É—an sanyi garin sakamakon ruwan sama da aka kwana yi daren jiya .
Shafa fuskar ta mama tayi , kamar yadda yake al'adar su ita da mamar ta .
Maama kin yi chau dayawa ,
Papa ka ga maama na tayi chau , donne-nous des photos ,
ta ƙarasa zancen tana hayewa kan kujerar da falmata take ta zagaya ta bayan ta gami da sarƙafa hannuwan ta biyu ta wuyan falmatan ta cusa fuskar ta gefen wuyan ta .,
Biyamuradi wanda ya fara yiwa hajja bayani game da shirye-shiryen da yake na tafiyar su US , ya juyo da duban sa kan su idanun sa suka sauƙa kan fuskar falmata wacce haƙoranta ke buɗe tana murmushin da yake bayyana farin cikin ta da ganin walwalar mama ya assasa mata ,
Kamar maganaɗisu ya riƙe shi , ya kasa janye idanun sa daga kan ƴar fuskar ta da komen ta yake ɗan madaidaici idan aka cire manyan idanun ta ,
Ba tare da ya iya É—auke ido daga kallon ta ba ya zaro wayar sa daga aljihu , ya juyo baki É—ayan sa ya saita cemara ya haska musu hotuna wajen kala shidda ,
Da gudu mama ta sake sauƙowa ta dawo wajen baban ta , tana cewa zata ga hoto ?
Ta É—are cinyar sa ,
Batare da ya sake mata wayar ba ya nuna mata hotunan , da sauri ta sanya hannu tana sake tura huton gaba , fuskar wata Æ´ar baby me kyau kamar ta ya cika fuskar wayar , Æ´ar yarinya ce da bata wuce shekaru biyu ba tana tsaye a hoton ,
A hankali mama ta É—ago kan ta tana duban fuskar sa
Papa bebe waye ?
Zare wayar yayi daga hannun ta ba tare da ya bata amsa ba, daidai lokacin da hajja ta ke cewa ,
Wannan yarinyar da surutu kike kamar aku , duk kin bi kin tsare shi da surutu kin hana shi ya yi magana , bayan kuma yayi shirin tafiya aiki , ni zo nan ki zauna na miki tafiyar tsutsa a ƙafar ki .
Sauƙa tayi daga jikin sa , maimakon ta tafi wajen hajja , sai ta nufi mamar ta , tana zuwa ta zauna a gefen ta gami da kwantar da kai a jikin ta tayi shiru ,
Boyayyar ajiyar zuciya Biyamuradi yayi , cikin ran sa yana hamdala da hajja ta katse masa tambayoyin mama , domin Alƙawari ya ɗaukarwa kan sa ba zai taɓa yiwa ƴaƴan sa ƙarya ba , akan duk wata tambaya da suka masa , sai dai ko ya sakaya amsar idan kaifin hankalin su bai kai su fahimce ta ba , amma a yanzu bai shirya amsa ba ga tambayar da mama tayi ma sa .
Cigaba da yiwa hajja bayani yayi , inda yake sanar da ita , yana son ranar litinin ya zo su je ayiwa falmata da mama passport , zai fara nema musu visa
Idan Allah ya yadda daga sun samu visa shi da su zasu tafi US , da ba zai wuce tsawon nan da wata É—aya da Æ´an kwanaki ba nan gaba ,
Ba shi da masaniya akan tsawon lokacin da zasu iya yi a chan ,saboda harka ce ta neman lafiya , bai san yadda lamura zasu kasance ba , amma dai visa ta tsawon watanni shidda zai samar musu .
Ya ɗora da neman hajja ta masa bayanin duk wasu abubuwan da zata iya buƙata bayan kayan abinci da sauran abubuwan buƙata na rayuwar yau da kullum wanda zai iya kai ta watanni shidda ko fiye da haka ,
Da farko addu'o'in samun nasara akan abunda zasu nema tare da addu'ar nemawa mama samun waraka tayi ta jerowa , tana jin yadda tausayin su duk ukun ke kama ta ,
Babban soja , ni ba sai an min tanadin kome ba , saboda ka ga nima wajen shekaru biyu ake nema rabona da Æ´an uwa da dangi , dan haka idan har tafiyar ta tashi , bayan kun tafi a washegari nima zan É—au hanya zuwa nigeria nima naje na sada zuminci na ga Æ´an uwa da dangi , shekaru sun fara jaa , mutuwar nan ta yanzu kar ta gifta tsakani ba'a nemi gafarar Æ´an uwa ba , idan ya so bayan dawowar ku ko kuwa ma kafin ku dawo sai a sanar min nayi dawowa ta , ai ka ga nima na ribaci lokaci ko kuwa ?
Babu shakka hakane hajja , to babu kome idan har tafiya ta kama lokaci yayi sai ki tafi zouwa gida kafin dawowar mu , Allah ya saka da Alheri , ki min duk wasu bayanai na abubuwan da kike buƙata da zaki yiwa mutanen gida tsaraba don Allah .!
Toh madallah Babban soja , amma dayake nima a wajen nawa akwai Æ´an kuÉ—aÉ—e irin waÉ—anda kake min kyautar su ai ba ma sai na maka lissafin kayan tsaraba ba , idan tafiya ta zo ni da kaina zani nayo Æ´ar tsaraba ta ,
A ah hajja , don Allah kar ki ce hakka , irin Alherin da kika mouna a rayuwa ba zamou iya biyan ki ba sai dai Allah shi saka da Alheri , ƙwarai ƙwarai ina miki godiya , ki min lissafi abun da kike buƙata duk zan sa a kawo kome ranar da zaki tafi sai direban da ya kai ki wancen karon ya sake kai ki nagode !
Ni ce da godiya Babban soja ni ce da godiya , Allah dai ya ƙara buɗi , ya ba wa mama lafiya ,
Ameen ameen hajja ya amsa yana miƙewa ,
Sashin da suke ya mayar da duban sa , mama har tayi bacci fuskar nan a chakuÉ—e alamun fushi take ,
Bai yi mamaki ba saboda sanin ta da yayi da saurin bacci ,
A hankali ya taka zuwa gaban falmata wacce tayi shiru , tana É—an shafar kan mama da yake bisa cinyar ta ,
Fatima ni zan tafi bakin aiki zouwa le lundi zan dawo mu tai à muku passeport , ki kula da mama kar tayi wassa dayawa idan ta ji sauƙi sosai sai ta cigaba da zouwa école .
Toh Allah ya kiyaye hanya ,!
Ta amsa masa ,
Ɗan jim yayi a tsaye yana ƙure mata kallo da buɗaɗɗun idanun sa , hular ta shi ta karɓi yar zagayayyar fuskar ta me ɗan haske kaɗan , ji yake kamar ya bar mata hular a kan ta yayi ta kallon ta a haka ,
Jin yayi shiru kuma ta san da tsayuwar sa a wajen ya sa ta É—an dago kan ta , tana sake haÉ—e fuska ,
Gyaran murya yayi ganin yadda tayi kicin-kicin kamar zata fashe masa da kuka .
Fatima donne moi mon chapeau! ( miƙe min hula ta )
Ya furta hakan yana sake rage amon muryar sa ,
Falmata wacce tsayuwar sa akan ta da idanun sa da take ji suna mata yawo a jiki tamkar suna mintsinin ta ya sa ta diririce ta gaza fahimtar me yake cewa , ba wai dan bata jin yaren da yake yi ba ,
Mama bacci take .
ta ce da shi tana fatan ya bar kan ta
A hankali ya sunkuyo har tana iya jiyo hucin humfashin sa a fuskar ta ya kai hannun sa guda ya zare hular sa dake kan ta , ya mayar kan sa .
Na tafi
Yace da ita yana juyawa ya bar wajen .
Wani irin yanayi ta ji a jikin ta uwa wacce aka zubawa ruwan sanyi , har ga Allah ta mance da hular sa da take kafe a kan ta ,
Runtse idanun ta tayi da ƙarfi tana jin yadda zuciyar ta ke bugu .
Hajja wacce duk abunda ya faru akan idanun ta tana iya hango su daga inda take .
auho ! aikin banza ihu bayan hari , da kike wani runtse ido kina wani kawar da kai ya ƙadangariyar gobara , ai wallahi ni dai na daina saki a hanya kan sha'anin auren ki , tsakani na da ke ido ,!
Ace wai tsawon shekaru fiye da biyar kin kasa zama cikakkiyar matar gida , ke kenan ɗaurewa miji fuska kina muzurai , zauna nan yarinya za'a yi bake lokacin da Babban soja ya gaji da halin ki ya sillo auren sa babu ni a masu yi miki dannar ƙirji , ko muƙamuƙi ba zan danna miki ba .
Cikin rashin kulawa da zantukan hajja wanda falmata ta riga ta saba da jin makamantan su , tace
Hajja ta me kika ce ?
Abunda wancan yace , shi nace
Ta amsa mata tana shirin miƙewa daga inda take tana cigaba da mita ,
Ƙatuwar mace kamar ki ace wai har yau tana da miji amma bata san amfanin sa ba sai rainon ƴa ,?
Ai ni ina kamar ki nayi aure na na biyu ma ,
Ki ka ce me hajja ta ban ji da kyau ba ??
Na ce gidan ku !
Ta amsa mata tana ƙarasa barin wajen
Murmushi falmata tayi domin ta san ta ƙular da hajja ,
Cikin ran ta tana juya maganganun hajja ,
Ban da abun hajja shi mutumin da kullum.take kumfar baki akan a kula da shi ɗin , shi ya taɓa nuna wata alama ne na kasancewar ta matar sa ? Tsawon shekarun auren su a tun bata san me takamaimai kalmar auratayya ke nufi ba ,